Showing 75001 words to 78000 words out of 95282 words

Chapter 26 - AFIYYA BOOK COMPLETE DOCUMENT By A'ishatu.txt

Ayshatuu   

16 Jul 2024

6661

bace, Allah wadaran wannan matar, tana zuwa gate suka hadu da Nads da Harith. Nads ta tsaya suka gaisa sannan ta fada Mata Shehu na London, Nusaiba ta dinga rokon ta seda ta samu contact din shi na can kafin ta tafi tana jin abinda Ummiey ya Mata ba komai bane indai har ta samu contact din da zata sameshi ta ci Masa mutunci.






Afiyya is not free pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258
[15/02, 23:10] +234 703 364 5886: 54








Tunda na sakko akan gado nake jin zuciyata Babu dadi, na dai daure nayi wanka Amma Ina Zama akan gado Dan fara shiri se na fara kuka, a hankali sautin kukan ke fita, inama inada dama na ayyana a raina da bazan Bari ya tafi ba, wannan satin biyun da yayi a tare damu ba karamin farin ciki ya saka ni a ciki ba, ya saka na tuna lokuta da dama na rayuwata ta baya, yasa ya Kara samun babban matsayi cikin zuciyata. Na share hawayena Ina murza Mai a jikina har lokacin ban daina kukan ba, how I wish he will stay with me and be my one, to Babu yadda zanyi Dole zai tafi Dan kuwa komai is not formalize. Na Kara goge fuskata Ina jin kamar na Hana shi tafiyar, na saka Kaya na wuce toilet na wanke fuskata sannan na fito parlor Amma dukda Haka Dana hango fuskata a jikin mirror se Naga idanuna sun danyi ja alamar kuka, na samu Nanny da Mom suna zaune, Nima na zauna Mom tace min da Bata lura da yanayi na ba


" Yau Shirin ya dade, muje Kar yayi missing flight dinsa"


Ba tareda na amsa ba na Mike tsaye da wayata a hannu na nufi kofa, se lokacin ta fahimci kuka nake yasa ta mike ta biyo bayana,


" Menene abin kukan Kuma? Naga zaku dinga waya"


Na gyada Mata Kai, tace


" Jeki dakko shade ki saka sannan ki wanke fuskar ki, idan yaga kina kuka he'll be disturbed"


Haka na koma nayi yadda tace sannan na fito shima lokacin ya shigo, clad in black trouser da Kuma turtled neck top me long sleeve ta ciki black ya daura suit a sama saboda har lokacin yanayin sanyin Bai Gama saki ba. Yayi kyau sosae na kalle shi Dan tunda na fito hankalin shi na kaina, ya karba key din motar hannun Mom muka fita bayan sunyi sallama da Nanny, na bi Bayan shi ni ya fara budewa seat din gefen shi na zauna ya rufe min sannan ya zagaya ya shiga ya zauna ya tada engine. Mom ta tuna Masa akan zamuje office din Dad suyi sallama Dan shi ba zai samu damar yin rakiyar ba. Tunda muka tafi motar shiru Babu me yin magana har mukai parking gaban katon building din, Yana kokarin fita Mom ta dakatar dashi da fadin


" Zauna kawai Bari na same shi mu fito"


Yayi murmushi Dan ya fahimci she's giving us some space muyi magana, tana fita ya dube ni all worried yace


" Damsel! Me yake damunki?"


Na girgiza kaina bayan na Dan bashi brief kallo he looks worried and disturbed. Na juyar da kaina jin hawayen na Kara taruwa a idanuna, ya saka hannun shi ya janyo fuskata tareda zare shades din Dana saka, ai tuni se hawaye ya balle min, na daura fuskata akan Bayan hannun shi Ina kuka a hankali, ya Dan saki siririn tsaki yace


" Look Damsel ki daina kuka, Nima kaina I wish Zan iya Yun kukan saboda na nuna Miki zanyi kewar ki idan na tafi, but at least idan na tafi na barki kina kuka hankalina bazai kwanta ba Zan ta tuna yadda muka rabu"


Na saki ajiyar zuciya Ina jin dukkan kalaman shi, na dago da jajayen idanuna da Kuma fuskata da tayi kacakaca da hawaye nace


" I'm going to miss you terribly"


Ya danyi murmushi me ciwo yace


" It's same here, I promise you I'll be coming often zamu dinga magana kullum kinji? Know that Ina sonki, a gurina you're irreplaceable kinji?"


Ya fada Yana sakar min tattausan murmushi tareda bani karamin yatsan shi Dan yaga Ina kallon shi irin Are you sure dinnan, ya gyada min Kan shi, na bashi yatsan nawa muka kulla yace


" Deal sealed!"


Nayi saurin sakin hannun saboda nasan abinda nayi ko nace mukai Babu kyau, na saki murmushi na maida hankalina Kan shi nace


" To kaima kayi kukan Naga da gaske zakai missing Dina".


Ya fara min dariya da tafa hannun shi yace


" Idan maza sukai kuka ai Babu kanta, know that I'm gonna miss you"


Na gyada kaina Ina Dan Kara jin Babu dadi. Mom ta karaso tare da Dad sukai sallama sosae Yana ta Masa godiyar zuwan da yayi. Daga Haka mukai sallama muka wuce airport shi Kuma ya koma ciki, mom Bata fito ba tayi Masa sallamar daga ciki sannan tayi.min alamar na bishi, tare muka dauki luggage din har zamuyi gaba tace mu tsaya tayi Mana hoto sannan Kuma muka wuce, seda aka Gama dukkan wasu formalities da Zan iya tsayawa tare dashi kafin Kuma yazo ya tsaya gabana yace


" Zan tafi, I love you!"


Na Dan Yi kasa da kaina Ina Kara jin ba Dadi nace


" I love you too"


Ya saki wani murmushi me taushi gaske so Charming nake fada muku yace


" You finally said the L word!"


Na rufe fuskata Ina dariya se Kuma wauan shi ta fara ringing, ya Dan Jima Yana kallon wayar kafin ya Kara kunnen sjhi Yana min alamar nayi excusing dinsa


" Nusaiba?! Ina Kika samu contact Dina"


Bansan ta ba Amma a family banji ance munada Nusaiba ba, hakan yasa a wayance na tattara dukkan hankalina Kan sauraron abinda yake fada, yeah sure I'm eavesdropping Amma ba zaka ce ba


" Har ka Isa ma? Why will you be happy bayan nayi dumping dinka"


" Dumping?!"


Na maimaita a hankali Ina Kara faking looks Dina, yace


" Nusaiba look, Dan mun taba relationship Bai Baki right ki.."


" Ohhh! Har zancen right kake? Kalla abinda ka samo ka rasa me zaka so se wani Kashi da Rai, kaci min mutunci da zaka so ni sannan ka kalla wannan abar kace kana so. Thank God I dumped you"


Abinnan ya min ciwo, ya kalleni Dan zargin ko naji Amma se yaga wayata nake dannawa yace


" Don't drag her into this mess! Kuma na barki ne kije da pride din ki shiaysa ni ban fara dumping din ki ba, tun Muna tare na ganta..."


" So you cheated on me? Da wannan guntun wanin, ai nayi tunanin zaka nemo wadda ta fini ne Dan naji haushi"


Yayi dariya wadda tasa na kalle shi yace


" Ni ba competition nake dake ba, sannan ki snai ita din tafi min ke say dubi, if I'll start over I wouldn't have dated you and ki sani I regretted dating you!"


Yana Gama fada ya kashe wayar shi, nasan duk inda take se taji kamar ta mutu Dan takaicin abinda ya fada, ya kalleni lokacin aka fara announcement akan zasu fara Hawa jirgi Dole mukai sallama seda ya kulle sannan na juya na fito daga departure hall din. A hanya Mom tace min


" Afiyya darling yake cewa Wai ko karshen shekara ayi muku aure, se nace ya Bari ki Gama makaranta"


Billah unconsciously nace


" Mom shekaran wajen uku fa, he'll be drained of waiting"


Aikuwa ta fara dariya tana tsokana ta Wai dama so take taga reaction Dina, naji kunya sosae yadda Baku tunani.










" So me kake so nayi yanzun? I gave you chance kayi Wasa dashi"


Hasher ya Kara Bata fuska, why is she not understanding


" Ammi ya kamata ki gane halin da nake ciki, how on Earth Zan Bari ta aura wani?"


Anty Bintu ta Kara kallon shi tace




" Hasher ka bar Afiyya tunda ta furta maka shi take so you please leave her, don't confuse her more"


" Ammi Ina sonta!"


" Shi ne dalilin da zaisa ka barta din, kasan abinda na yadda a soyayya, if you love someone is not necessarily making that person yours, you let him go as far as that person is happy it's ok! I know it's hard do it Hasher"


Ya Jima shiru yana tunanin duk tsawon watannin da sukai me yasa Bai fada Mata Yana sonta ba se yanzun? Kai bazai Bari ba he definitely need to do something Kuma. Ganin yayi shiru Anty Bintu tace


" Kai da Babana duk daya kuke, I'm so glad shi ne yake sonta ba bare ba, yarinyar nan has gone through alot Wanda ni a shekaruna ban dandani rabi ba, Hasher please ka kyaleta tayi farin ciki, don't stress her more'


" Ammi kenan Baki Sona da ita?"


Anty Bintu ta girgiza Kia tace


" Ka fahimce ni Hasher, baka San Afiyya ba I introduce you to her and vice versa, naso kuyi aure Amma nasan Shehu ya kasance tare da ita tun kafin ta sanka ni bansan Yana sonta ba shiyasa nake baka hakuri! I'm sorry son"


Ya gyada Kai bawai Dan ya hakura ba se Dan ya kwantar Mata da hankali!








Afiyya is not free pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258.
[15/02, 23:10] +234 703 364 5886: 55








Tamkar hasken Rana Haka gidan yake bakace wannan lokacin yayi Kama da Bayan sallar ishai ba, kowanne kwai ya haske gidan ya bada asalin kyau. Babu kowa a tsakar gidan se wata Mata da shekarunta zasu tasar ma ashirin da hudu zuwa biyar, tana sanye da maxi bubu Amma dukda Haka seda cikin jikin ta ya bayyana, tana tsaye da waya a kunnen ta alamar waya take, Jin sallamar Malam da Kuma Junaidu yasa tayi saurin juyowa, ta saki wayar ta Fadi Akan dabdanyar interlocks din da suka malale tsakar gidan. Ta nufi gurin fuskarta dauke da madaukakin annuri ta riko hannun Junaidu tace


" Yaya Junaidu! Kaine? Kaine ka dawo gida?"


A hankali Junaidu yace


" Zainab kece Kika girma Haka?"


Se ta juya cikin gidan tana fadin


" Hajja! Baba!! Ummaah!! Anty!!! Ku fito Yaya Junaidu ya dawo"


Ina tunanin hatta makwabta seda Suka jiyo maganarta, ta dawo ta rungume shi tana sakin kuka, karku manta zainab ita ce sanadin mafarin komai, dalilin ta aka fara takun saka da shi da Fatima har yayi sanadin fadawa abinda yake Yi. Hajja ta fara fitowa se Ummaah wato Fatima wadda kullum tana jin kamar ita ce dalilin lalacewar shi, ita ce sular barin gida shiyasa kullum cikin adduar ta tana roka Masa ranar da zai dawo gida ta samu ta rikeshi gafara shima ya roki gafarar iyayen shi. Hajja ta karasa ta rungume shi Dan tuni zainab ta sake shi ta matsa gefe, Hajja ta fshe da kuka tana ta shafa fuskar shi tana fadin


" Allah nagode maka, Allah nagode da ka karba adduaya ka dawo min da yarona gida, Allah nagode maka"


Ya rike hannayenta Yana jin wani irin abu a cikin zuciyar shi, ran shi da Kuma jikin shi, wani yanyai ne marar misaltuwa, wani irin rauni yake ji tamkae bashi dinnan bane Wanda no matter abinda ya faru zuciyar shi Bata motsawa, Amma kawai se yaji Abu Yana bin kuncin shi, ya saki hannun Hajja ya taba se kawai yaga hawaye ne, shikam bazai tuna last time da hawaye ya fita a idanunshi ba, me yasa yayi Haka? Ya dinga Jin Babu dadi,zuwa wani lokaci Yara duka sun fito kadan ya gane a ciki Amma sauran duka Bai tuna su ba ko ya tafi aka haife su ko Kuma suna Yara ya barsu, Amma cikin su kowa yasan shi saboda Babu ranar da zata zo ta Fadi baayi maganar shi ba, wasu da suka San gidan shi har zuwa suke wajen Afiyya wadda Basu San Bata nan ba. Parlon Hajja aka zazzauna aka kawo Masa abinci Wanda tun safe Bai Kara cin komai ba, komai ya canja hatta iyayen nashi sun Kara manyanta sun tsufa. A Daren jamilu da Anty Jidda Suka zo sauran ne ma suka Bari seda safe. Bai San dalili ba wanann Daren se yaji bacci yake cikeda nutsuwa Wanda wani lokacin se yayi ta munanan mafarki ko Kuma abinda yake son cikawa zuciyar shi Wanda gashi duk yadda ya kamata ace ya cika burin abin yaki yiwuwa.


Washegari Malam da Junaidu da sauran yaran maza Suka tafi massallaci, tamkar mafarki dukkan su Haka suke ji to Amma Kuma waye yace Allah ba maji kukan bayinsa bane ba, ka roka ka daura yakinin cewa zai amsa maka tabbas zakaga biyan bukata, for 15years suna addua Basu gaji ba Basu yanke tsamannni zaa amsa musu ba se gashi Rana daya, minti daya Junaidu ya dawo gida, Junaidu yayi sallah wannan ai abin ayi murna ne.


Da safe gidan ya cika se saukewa ake ana daurawa dukda kannen nashi na dardar dashi sanadin ko can ba sakar musu fuska yake ba, shi dinma wani iri yake ji musamman ganin yadda suke tsananin farin ciki da annaashuwa se Kiran abokan arziki suke suna fada musu ai Yaya Junaidu ya dawo. Se dare sanann ya samu Suka kebe shi da Hajja da Malam, Babu wani tone tone da akai the only abinda Malam ya tambaye shi shi ne Ina Amina? Junaidu yayi kasa da Kan shi ya fara fadawa Malam duk abinda ya faru har zuwa yadda akai suka rabu.


" Dama niyyar ku daga Kai har kawun ta bamai kyau bace, shiyasa ba zaku ga daidai ba har se Kun nema yafiyar ta. Dan Haka gobe ka shirya muje sannan namiji baya cika seda aure. Ya kamata kayi aure"


Shi gaba daya Junaidu ya manta da cewar Yana da Erectile dysfunction, hakan yasa yayi sunkui da Kai yace


" Malam zaka iya ma kawunnan ta magana su yadda na maida ita"


Hajja tace


" Aminar?"


Ya gyada Kai yace


" Ita din haske ce a rayuwa ta, na cutar da ita na zalunce ta har abinci nake hanata Amma kullum taga Nayi wani Abu marar kyau to se ta yimin magana Koda Zan kashe ta ne. Dalilin ta na dawo hayyacina, na dawo Kan tafarkin musulinci. Na Kuma tabbatar zuciyata son ta take a lokacin da ya kamata ace na tausaya Mata na Kuma kula da ita, Malam Dan Allah kayi kokarin ganin ka dawo min da ita, ita din HASKEN RAYUWA TA CE"


Malam ya jinjina Kai tabbas Afiyya ta taka muhimmiyar rawa wajen gyara Junaidu dukda magana ce kawai tayi Amma wani lokacin bamu sanin how powerful words are, shiyasa duk lokacin da zakai magana weigh the words, baka San idan sun fita me zasu janyo ba, they can break soul, deform a heart, kasan me zaka fada shi ne kawai!


Yinin ranar Junaidu yayi shi cikin zulumi dan kuwa Malam ya nuna Masa bazai iya ba, shi kunyar yarinyar ma yake ji da Bai ma santa ba, how he wish abinda ya faru Bai faru ba da yayi farin ciki, ya nunawa Junaidu wannan yakin nashi ne ba Wanda zai Masa wannan fadan ba shi zaiyi wannan fadan. Yayi shiru a dakin shi Yana ayyana ko ya Afiyya zatayi shi Bai masan Bata kasar ba yasan dai zaa same ta a ringim. Yana zaune se rehearsing yadda zai Mata magana yake


" AFIYYA kiyi hakuri ki yafe min! Ki bani wata dama mu Kara Zama inuwa daya"


Se ya girgiza Kai yace line din is too plain and odd. Ya Kara yin shiru kafin Kuma ya Mike Yana zagaya dakin yace Yana zuwa zai zube akan gwiwar shi


" Aminatou nasan ke din haske ce, Dan Allah ki dawo rayuwata Dan na gyara kurakurai na da nayi a baya"


Se ya girgiza Kai yace wannan Kuma yayi extreme da yawa , can se ya fita zuwa wani katon shago yayi sayayya iri iri wadda yake da tabbacin zata burge ta sannan ya dawo gida.




Washegari da wurwuri Hajja Baba da Malam, jamilu da Anty jidda, Ambaby da Kuma shi kan shi me gayya me aiki Junaidu. Yasha manyan Kaya ya kafa hula Kama kallon shi kaga lafiyayyen namiji managarci Amma abin baa fuska yake ba. Ambaby na sane tasan Afiyya Bata nan Amma dai so take taga iya gudun ruwan kowa. Misalin Sha daya na safe suka Isa cikin garin Ringim, tiryan tiryan komai ke dawo Masa tundaga ranar da suka fara zuwa gurin ta yaki Mata magana zuwa auren su inda akai controversy akan sakin ta, ya nuna musu kankanci ta hanyar daukar ta cilak ya saka a mota ya tafi da ita, se yaji zufa ta karyo Masa ta Ina zai fara kuma,? Ta Yaya zai fuskanci Yan uwanta iyayen ta da ya batawa Rai a wañnan rana. Se yaji kamar yace su juya ya fasa but it's today or never! Se Kuma yayi tunanin ai inda ake Hawa to ta nan ake sauka Dan haka se ya kwatanta musu gidan Kawu Sa'idu. Suna Isa kofar gidan Yana fitowa daga ciki Allah basshi zakuyi tunanin shi din mahaukaci me saboda yadda ya fito a firgice tamkar Wanda Zaki ya biyo shi. Ya tsaya se waige waige yake kafin Kuma ya daga kafafun shi Dan tafiya motocin su Junaidu suka tsaya, Dole ya tsaya Dan duk tunanin shi Kawu Tijjani ne da yace masa zai zo Ringim din ranar, suna hada idanu da Junaidu yayi azamar komawa ciki se Malam ya dakatar dashi da fadin


" Malam barka da safe!"


Kawu ya tsaya Yana Dan haki yace


" Barka dai! Me ya kawo ka kofar gidana ko kazo ka karasa ni ne da Raina?"


Malam ya danyi gyaran muryar yace


" Allah ya huci zuciyar ka ni din mahaifin shi ne, nazo muyi magana ne"


Kawu ya dallawa Junaidu harara sannan Kuma ya Shiga ciki se gashi ya fito da tabarma, matan yace su shiga ciki, tunda Ambaby ta Shiga da Jidda suke Willa idon ganin Afiyya Amma shiru har Siyama ta baza musu tabarma wadda auren nata yake lilo shi Bai mutu ba shi Kuma baa zauna ba. Suka zauna suna zazzare idanu, ta debo musu a katon Kofi ta aje sannan ta koma daki ta zauna, Ummaan su ta fito Wanda da batayi niyyar hakan ba, Suka gaisa tace


" Daga Ina hakan ban gane ki ba"


Hajja da fara'ar ta tace


" Iyayen tsohon mijin Amina ne"


Ummaah ta kalle su tace


" Wacce Aminar kenan?

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login