Showing 12001 words to 15000 words out of 95282 words
Chapter 5 - AFIYYA BOOK COMPLETE DOCUMENT By A'ishatu.txt
zuka ba shikam Malam he's always the lead. Bayan an gama maghrib kowa ya Kama gaban shi. Fatima ce da girki tun karfe hudu ta kammalla haka take badai kaga tayi Daren girki ba. Ruwa ta tafasa ta shiga wanka, tana watsa ruwan taji wani kaikayi a duk inda ruwan ya sauka, ta dubi jikinta gurin yayi jawur tamkar ta kone, a gigice ta dubi ruwan tasa hannunta Amma shima hannun tana fito dashi se kaikayi yayi jawur, zani ta daura ta fito a guje tana kwalawa Hajja Huwaila Kira, kafin Hajja ta fito tuni Hasiya ta fito ta same ta tsakar gida tana faman sose sosen jiki, Hasiya tace
" Fatima ya akai?"
Ta kasa magana se nuna Mata take da hannu, tana Susa, lokacin Hajja ta fito itada Amarya suka samu Fatima tana Neman cire zanin jikin ta, ga yaran duk sun zagaye ta wasu a ciki na kuka, hannunta Hajja ta kama Suka shiga daki, Suka fara duba jikinta, duk inda ta Sosa yayi burdi yayi Kuma kwaf kwaf kamar konuwa. Hajja ta Yi shiru Dan ita ta rasa abinda zata ce tunda take Bata taba ganin abin ba, ta dauka hijabi tace da Hasiya
" Ke ki zauna da Yara, ni Kuma da Amarya zamuje general, ki aika a fada ma Malam"
Da hakan Suka Taya Fatima ta shirya,suka samu Keke napep Suka tafi general, kowa idan aka bude gurin gani suke allergy be hakan yasa focus din maaikatan asibitin, sede ana administering drugs din kamar bama shiga suke ba, in fact tunda jikin ba bukatar su yake ba kokarin reacting musu take. Anan Malam yazo ya same su, hankalin shi ya tashi ganin maaikatan sun ce sede su turasu AKTH suga dermatologist kawai, Malam ya karba takardar, ga Fatima ciwon se Kara Hawa take, se ihu take tana Kiran sunan Allah tana su taimaka Mata kaikayi zai kasheta.
A wannan Daren da Junaidu ya dawo ya samu gidan tamkar gidan makokin, yaran na tsakar gida sunyi jugum, Wanda sukai kuka zuwa lokacin sun hakura, Bai bi ta Kan kowa ba ya shige dakin abin shi ya zauna Yana ayyana ya kamata ace zuwa yanzun aikin shi yaci Akan Fatima, tunda kuwa Jarma yace Masa tamkar yankan wuka haka aikin malamin yake, Yana cikin zaune Sega zainab ta leko, tunda sukai abin kudinnan yarinyar ke shishigge Masa tana son ganin ta wanke laifin ta. Yana zaune ta shigo ya dago ya kalleta yace
" Meye?!"
Ta zauna tace
" Mama ce Bata da lafiya!"
Ya gyara Zama yace
" Me ya sameta?"
Ta zauna tana kuka ta fada mishi komai, maimaikon taga ya canja yanayin fuskar shi zuwa tausayi, se taga Yana murmushi, yace
" Abin yazo kenan! Kije zata ji sauki"
Zainab jiki a sanyaye ta fito ta dawo tsakar gida tayi shiru tana tunanin halin da uwar ta ke ciki, Bata Jima ba suka dawo da Fatima dan a wañnan Daren bazasu iya tafiya Kano ba sede zuwa gobe. Ihun da take yasa Junaidu fitowa kofar daki ya zauna, Bai ce musu kala ba Amma se smirking yake Yana kallon yadda Fatima ta Zama Yar bori, sight din kawai dariya yake bashi, ya zauna yaki tafiya Yana hango duk abinda takeyi, gasu Hajja Huwaila nata karbar jike jiken ayatul shifaa daga gurin Malam, Suka zaunar da ita suka Bata Tasha, Yana shiga cikin ta ta fara amai bakikirin, Hajja ta Kira Malam yana zuwa yace wannan sihiri ne Kuma an karya shi, Hajja ta rike kirji yayinda Hasiya da Amarya suka furta
"Sihiri malam!"
Ya gyada Kai yace
" Tabbas sihiri ne! Allah ya Bata lafiya"
Suka saka ta kuskure bakin ta, ta saki ajiyar zuciya ta lumshe idanu bacci ya dauke ta. Malam ya gyada Kai ya juya zuwa dakin shi, daidai dakin Junaidu yaji Yana waya
" Man nake fada maka abin yaci fa, dukda dama ba wani tsawon lokaci zai dauka ba Amma nasan ta karbi wahala"
Ya Jima Yana sauraron magamganun Junaidu Amma ya kasa gane inda zancen ya dosa, shi yaron tsoro yake bashi tunda Suleiman yace ya ganshi tsakar dare Yana Kona wani Abu a kasko shikenan ya koma jin tsoron shi. Shidai yasan kullum Yana adduar Allah ya shirya yaron Amma Kuma har yanzun abubuwan Junaidu Kara gaba suke. Ranar baccin dadi Junaidu yayi, Dan burin shi ya Gama cika. Da asuba kowa ya tashi yin sallah, seda ya Bari kowa ya fita massalaci, masu Yi a gida sun tayar, ya fito Dan shi ba sallar yake ba se jefi jefi idan ya ga dama. Dakin Fatima ya wuce ya sameta tana kan sallaya tana sallah, ya zauna Kan kujera har ta idar Dan ita Bata lura da shigowar shi ba. Tana idar da sallar ya sakko ya nufo ta, da sauri ta juyo zatayi ihu yace
" Junaidu ne!"
" Me kake min a daki? Fitar min daga daki nace"
Yayi dariya yace
" Ba wani Abu nazo nayi Miki ba, daki da kike cewa na fitar Miki daga shi, ai ni Banga daki anan ba. Kinga sakamakon zagi da sharri da Kika min, ko Baki fahimci nine nasa aka Miki sihirin da kikai kaikayin jiya, idan Baki fita harka ta ba Zan saka an Miki wanda Zaki rasa rayuwar ki gaba daya, ko ki haukace, Kuma wallahi zakiyi kyau da hauka.."
Yayi dariya ita Kuma tuni jikinta ya fara rawa, tsabar yadda ta tsorata da maganar shi.
" Idan kinji shikenan kin tsira idan..."
Malam ya bude labulen dakin a zuciye ya Shigo, Fatima da Junaidu lokaci daya Suka Mike, Fatima tayi saurin matsawa gefen Malam Neman kariya, yayinda Junaidu ya tsaya sokoko Yana tunanin abinda zaiyi, Wani Mari Malam ya sauke Masa a saman kuncin sa, yayi baya kamar zai fadi, ya cakumo wuyan shi ya tsayar dashi ya Kara Masa wani, cikin tsananin bacin Rai yace
" Ni Dana zaije gurin bokan! Malamin tsubbu! A gidana"
Junaidu yayi shiru yana kallon Malam dake janshi har ya kawo shi tsakar gida, dake fadan malam yasa duk sun firfito Dan ganin meke faruwa, duk suna tsakar gidan yasa Sukai carko carko suna kallon Malam da Junaidu a hannu, ga Fatima a gefe se hawaye ke bin fuskarta!
Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria send evidence to 09063467258.[15/12, 10:38] +227 98 36 59 34: Junaidu ya runtse idanun shi Yana tuno kalaman malam daya bayan daya, yasa hannun shi ya hargitsa gashin da ya Tara a kanshi, looking like the bad guy he always is, ya sakko da katon akwati ya fara life kayan shi a ciki
" Malam kada kayi haka, kada ka yanke hukunci lokacin da ranka ya baci, yawanci idan akai haka a gaba zaayi Dana sani, Kai me fada ne, Kai me bawa Yara tarbiyya ne kada kayi haka Malam!"
Hasiya ta fada tana jin kamar ta kurma ihu, Hajja dama tunda taji abinda ya furta ta sulale a gurin ta zauna, saboda tasan matsawar ta cigaba da tsayuwa jirin da take ji zai yadda ita ne a gurin, Kuma ba lallai ta Kara taka kafafunta ba. Malam Bai ce ma Hasiya komai ba yaja hannun Fatima ya maida ita daki sannan ya dawo tsakar gidan, Amarya ta dube shi tana kuka tace
" Malam ka sassauta zuciyar ka, ku kuke yiwa mutane waazi akan kada su Bari bacin Rai yayi ruling din su se gashi Kai da bakin ka ka tsinewa Dan da ka Haifa ka Kuma Kore shi daga gidan! Malam"
" Na fada Junaidu na fitar shi a cikin Yayana, kada ya Kara waiwayata sannan Kuma kada ya Kara zuwa gidana"
Daga haka ya juya ya wuce dakin shi, Hajja ta fara kuka Hasiya na Taya ta, amarya ce me Dan kwarin gwiwar Basu hakuri da lallashin su. Junaidu ya kammalla hada kayan shi tas, ya fara kokarin Jan akwatin Sega Hasiya da Ummiey sun shigo, Ummiey kanwar shi ce,
" Yanzun Junaidu baka bawa mahaifin ka hakuri ba, me yasa kake haka?"
Ya kakkabe kanshi yace
" Ya Dade Bai hakura ba in har ni Zan bashi hakuri. Duniya da Fadi maye ba zaico Kan shi shi kadai ba"
Ummiey ta rike hannun shi tace
" Dan Allah Junaidu karka tafi, Dan Allah kaje ka bashi hakuri, durkusawa wada ba gajiyawa bane"
Ya doke hannunta yace
" Ni Zan durkusa na bashi hakuri, ni basamude ne Kinga yazan durkusawa wada kuwa?"
Ta share hawayenta tace
" Mahaifin ka ne fa, idan ka tafi Ina zakaje"
" Ke Wai Ina ruwanki, badai ya koreni ba yaje ai watarana zai neme ni, Baba Hasiya ki kula min da Hajja nagode!"
Daga haka yaja kayan shi ya fita ko tsakar gidan Bai kalla ba balle yaje ya ma Hajja sallama, Hasiya ta biyo shi ta rike rigar shi tace
" Tafiya zakai? Ba zaka bashi hakuri ba wai!"
" Ki Bari Dan Allah Baba Hasiya, kawai Zan wuce ne"
Daga haka Bai Kara waiwaye ba ya juya ya bar gidan, duk abin Junaidu da ya fita daga gidan yaga Babu inda zau nufa, garin Babu mutane saboda safiya su Kuma ba Yan uwa ke gare su ba se kawai yaji wani kunci da takaici ya lullube shi. Ya cigaba da tafiya Yana cin buri da alwashi a cikin zuciyar shi, inda Suka Saba Zama yaje ya zauna, shi daya sannan ya fito da bankin shi ya fasa, kudi sosae ya taru a ciki Dan shi mutum ne Mai adani bawai komai ya samu yakai ciki ba. Kamar yasan irin wannan ranar zata zo masa ya dinga Tara kudi, mikewa yayi ya siyo abinci yaci sannan ya dakko wayar shi ya Kira huzaifa yace Masa ya sameshi a gurin su, sannan ya taho da sauran.
Nanny kwana biyu ta kara, ranar asabar da safe ta gama Shirin ta zata tafi, tun dare da Naga ta na saka min komai yadda ya kamata kayan data siyo min na fara kuka, ko lallashin na Bata Kara Yi ba ta kyalleni. Na kalleta idanuna sunyi jawur nace
" Nanny tafiya zakiyi? Ki tafi Dani Dan Allah Nanny, it's horrible living here"
Ta rike hannuna tace
" Ni awa Zan tafi dake Afiyya? Zan cigaba da zuwa Ina ganinki inshallah, duk abinda kike bukata kimin waya zansan yadda zanyi a kawo Miki. Karki manta you've to live saboda iyayenki su samu masu musu addua, karki manta da maraicin ki, a kullum ki tuna Allah shi ne gatanki Kuma komai ya faru dake kaddara ce. Naga hisnul Muslim dinki a jaka, na Kara Miki wani kiyi ta addua komai zai zo da sauki ko ba yau ba, akwai ranar da zakiji Dadi!"
Na saka kaina a hannunta na dinga kuka, zuciyata ciwo take min, a shekarun da nake dasu kalilan na fuskanci abinda da yawa Basu San Yana wanzuwa ba.
" Idan naje maiduguri zanyi magana da dangin Maman ki muga ko zasu zo su dauke ki, sannan zanyi magana da Alhaji karami naji ko akwai abinda zai iya Yi"
Nayi saurin girgiza Kai Ina jin bacin Rai Yana mamaye ni nace
" Nanny Dan Allah kada kiyiwa kowa magana, ki rabu dasu Dan Allah, a yanzun bana bukatar su. Watarana Nima Zan fita daga halin da nake ciki"
Se tayi murmushi me ciwo tace
" AFIYYA kada kiyi fushi dasu, akwai abubuwan da a shekarun ki bazaki gane ba,nasan nan gaba Zaki fahimci waye ainahin kawun ki Sa'idu. Kiyi addua sosae Allah zai kawo Miki dauki"
Kasa rakata nayi, na tsaya kofar daki nayi ta kuka, Mino da Siyama na tsaye suna kallona da tausayi musamman Mino, Ummaan su dama Bata fito ba, daki sukai sallama, kawu ya leko yayi Mata godiya yace Yaya ya kaita Tasha, ya koma ciki. Har ta Kai zaure se na nufe ta da gudu na rungume ta, na rike hannun ta Ina fadin
" Nanny kin yi min alkawarin Zaki dinga zuwa akai akai ko?"
Ta gyada min Kai ta share min hawayen dake zarya a kumatuna tace
" Kiyi shiru kinji, karki Kara kuka komai zai wuce"
Ta dubi Yaya dake a hargitse, idanun shi sunyi ja tace
" Me sunan waziri amanar kanwar ka, ka kula da ita Dan Allah"
Daga haka ta fita, na Dade a zauren Ina kuka, Babu Wanda yazo ya lallashe ni seda nayi me isata sannan na dawo ciki nayi shara na hada wuta. Nayi wanka na saka Kaya, Yan kayan Dana cire naje na wanke su dukda ba iyawa nayi ba Amma wannan rayuwar da nake ciki ni ce uwata ni ce ubana, Babu me cemin nayi wanki ko akasin haka, ita dai indai nayi Mata aikin ta to idan naga dama ma kada nayi wanka. Inata sakin ajiyar zuciya naji an kwalla min Kira,na fito Amma na kasa magana ta dubeni tace
" Bakin ki ciwo yake Miki da Zan kiraki ki ki amsawa?"
Nayi Mata shiru kawai, daka min duka tayi a cinya ta tareda dangwarar min da shayi tace
" Shegiyar yarinya kawai"
Bance komai ba na juya na bar tea din a gurin, ba abinda nake son Sha kenan ba, in fact abinci a wañnan lokacin shi ne Abu na karshe a wanted list Dina, kawai space nake bukata. Na koma daki nayi jugum se jin kawu Sa'idu nayi Yana kwalla min kira, na fito a hankali shima ban amsa ba, Ina tsayawa kawia naji saukar Mari a kuncina, bana tunanin an taba Mari na, idanuna a warwaje na rike gurin na dago na fara kallon shi, kallon da nake Masa na mamaki, tsoro, tsana da Kuma warning, hakan yasa ya daka min tsawa yace
" Saukar da idon ki kasa shegiya kawai!"
Have you ever felt pain radiating daga zuciya zuwa kowanne sashe na jiki kuwa? Wannan kalma ta shegiya na tsane ta, tafi Marin ciwo a gurina. Naki dauke idanuna yau taurin Kan ya motsa , sede ya motsa inda bazan ci nasara ba. Waya ya dakko ya min duka da ita, na dinga kuka Ina ihu Amma se zagina yake Wai taimko na yake na Isa nama matar sa rashin kunya. Sede yayi min lilis, Mino na gefe da Siyama na kuka. Ya kalleta yace idan na Kara Mata Abu ya Bata go ahead ta dakeni! Anan ko tashi banyi ba na dinga kuka Banda tukuki Babu abinda zuciyata keyi, se jikina da nake jin ya fashe saboda dukan da nasha da cord wire. Ba Wanda ya kulani Dan yaranta tuni ta daka musu tsawa Suka baje, shi Kuma har lokacin Yaya Bai dawo ba. Ina wannan kukan tace naje nayi wanke wanke idan na ga dama na kashe kaina damuwata ce. Haka na tashi naje inayi suka zo suka fice gaba daya sunyi kwalliya Hafsa kayana ne ma a jikinta, shima Babu jimawa ya fita ya rage ni kadai. Ina gamawa na fara maida kayan kitchen, har lokacin hawaye Bai daina sauka ba, mafita kawai nake nemawa kaina. Na shiga kitchen wukar Dana wanke ta silale ta fado seda na aje kwandon sannan na dauki wukar, I began to think ko dai na kashe kaina kawai kowa ya huta, na rike wuakr Ina lumshe idanuna, na saita ta daidai cikina se Kuma na maida ta inda aka cemin major arteries da veins na jiki na gurin wato wuyana, na saka a hankali na furta
" Astagfurillah, Abbu Mama I failed you!"
Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence through 09063467258.
[15/12, 10:38] +227 98 36 59 34: Dake yan class din sun fara lesson a month ago se ya zamana sunyi nisa a physics din, motion shi ne topic din da ya rubuta a jikin board, Amma kafin ya fara bayani Kan motion din seda ya tambayi Yan class Wanda zai iya recapping abinda aka koyar. Sauda dake kusa Dani ta daga hannu, hakan yasa malamin yayi pointing din ta ta tashi ta fara bashi amsa, ta Jima tana bayani kafin Kuma yace ta zauna bayan yasa an tafa Mata. Na kalleta Bayan ta zauna nayi Mata murmushi itama tayimin. Babu dadewa ya shiga bayani Alan motion, nayi shiru Ina assimilating abinda yake fada, haka Ina jotting points where necessary. Seda ya Gama sannan ya mikawa class rep note din yace ta rubuta Mana a board ya fita gaba daya. Na sauke ajiyar zuciya na kalla Sauda nace
" Sauda Dan Allah naga note book dinki"
Tayi murmushi ta Miko min tace
" Amina kinada kyau!"
Nayi murmushi kawai Amma ko godiyar compliment din banyi ba, na bude na fara kwafar note dinta, dake inada sauri Kuma Yan class din sun tsaya Wasa ko fara rubuta sabon note din baayi ba yasa na Gama kafin wata period din ta shiga. Nutsuwa nayi inata going through Dan na samu na iya abinda aka koyar. Ina cikin Yi se ga wani malamin ya shigo me maths, wani young guy haka, muka gaishe shi yayi abinda zaiyi ya fita, har lokacin Babu Wanda yayi noticing Dina a ajin, a ranar da aka tashi Sauda ta Ara min books dinta Dan naje na kwafa. Ana tashi na hada books Dina na saka cikin jaka na dubi Sauda na Mata sallama, se sauran dake kusa damu da bansan sunan su ba na musu sallama na fito Ina kallon yadda kowanne dalibi ke kokarin tafiya gidansu, se na tuna tawa rayuwar a NTIC. Na girgiza Kai kawai na fara tafiya a hankali, ga Rana ga zafi ga Yunwa, Amma haka na nufi gida bakina ya bushe saboda kishin ruwa. Tun daga kofar gida na hango Yaya a tsaye Yana magana a waya, cikin sauri na karasa Ina hango murmushi kwance saman fuskar shi, na karasa kafin yayi min magana ko ni nayi ya Miko min wayar shi, na karba na Kara a kunne ba tareda na duba me Kiran ba.
" Hello Afeey darling!"
Kadan ne Bata kashe min dodon kunne na ba saboda ihun da tayi, na saki dariya a hankali Ina kallon Yaya da ya lumshe idanun shi Yana kallona nace
" Rooks! I missed you"
Tace min she missed me too sannan tace
" So fada min ya makaranta? Yau ranar ki ta farko how do you find it"
Tambaya dai a gurin Rooks ba daga nan ba, na zauna kan bencin da Yaya ya janyo min na fara fada Mata komai akan makarantar, a karshe nace Mata
" Nafi son waccan ta Abuja, saboda idan na dawo gida Ina tarar da Abbu da