Showing 114001 words to 117000 words out of 159314 words

Chapter 39 - Wata Kishiya Complete writing by Sa'adatu Bint Abdullahi .txt

wallahi, doctor yarinyarnan ta tsaneni tin a kan cin dana mata na farko na fahimci tabi ta tsaneni ko ganinama batasan yi , dole taki jinina...wallahi se an biyani cikina daya zube..." Doctor mus'ab yayi shiru yana kallan Abdoljalal shi kallan mahaukacima yake masa sbda magnganun nasa bana masu hankali bane, yaza ayi ace ka zubar da cikinka da knka kuma wai ka hau sirfafa matsifa sbda rashin hankali da rashin lissafi irin nasu na maza. "Gaskiya kaci kai..." Cewar dr. Abdoljalal ya kara hasala yace " dole kace haka tinda ba cikinka bane... yarinyar nan ta renamin hnkli gabaki daya, kilama mgninsu na yan kauye tasha ta zubarmim da ciki, wallahi wallahi taci arziki daya na SO, da har karar mutum ina iya kaiwa, koma waye ya bata maganin zubda cikin wlhi in kaishi kara ya biyani cikina, wulakncin bnza da hofi kawai..." Dr ya amshe da "Ko kuma kai a kaika kara ba, kaci yar mutane ka mata ciki baka Auretaba, kuma kana mgnr bnza, kaji mgnr bura uba kai,.." Abdoljalal ya taso masa kai kace shi ya zubar masa da cikin jikin Almuqri'ah din. "Kai kake mgnr bnza da hofi, aikin bnza aikin hofi kawai, koda nacita ba Aure ai inasan cikin nawa dana mata ko? tinda da ubansa..." Doctor ya tashi a kn kujerar da yake haushin Abdoljalal dukya rufeshi hkn yasahi tashi tsaye yace. "bakada hnkli,,,wai kayi abu kuma ka daurawa yarinya lefi, kasamu yar mutane kanata haike mata da bura,, yanzu kuma wai ka daura mata lefi, yanzu haka itama batasan ciki bane a jikinta kmr yadda kaima baka sani ba..." Dr ya tasoma Abdoljalal shima kmr ze rufeshi da duka. Abdoljalal yayi tsuki kawai shi a dole Almuqri'ah ce ta zubar masa da ciki, ya tashi ya fice a office din yanajin dr nacewa "Se Allah ya sakawa yar mutane, kanata zurmuqa mata abinda yafi karfinta kuma kana mata bura uba, se fadin bnza da hofi..." Shima duk ranshi ya bashi, dmn hk Abdoljalal yake shi murd'ad'en mutum ne sam beda dadin kai. Abdoljalal be sake bi ta kn dr ba Ya nufa dakin da aka kwantarda ita daman Ahamad ya bari a dakin, ya kalli Ahamad din rai a baci yace"Kai bani car key..." Ya Karashe mgnr yana kallan inda take kwance jininsa da ake sa mata yana shiga hannunta a hnkli. Ahamad jiki na rawa ya mika mata car key din ya amsa ya fice a asibitin, se bura ubar fadin rai yakeyi, zuciyarsa kmr zata fashe dan takaici, ga jirima na neman kwasarshi, sbda jinin da aka diba a jikinsa, dr yace ya tsaya ya huta amma yaki. Abdoljalal direct ya nufa gidansa yayi wanka, ya chnza rigarsa data baci da jini, da knshi ya wanke motar data bata da jinin ma'aikata nata kallan abin mamaki. ya dawo asibitin da duk abubuwan dazasu bukata seda ya tsaya yase musu, kana ya dawo se faman fushi yakeyi har lokacin shi a dole an zubar masa da ciki abinda ya jima yana nema, yadawo ya zauna gefen bed din yacema ahamad kai jeka kawai..." Ahamad ya mike a guje ya bar dakin, ganin oga nata muzuran dabe taba ganin yanayinuba se yau. Abdoljalal kam haushin uban kowa yakeji, tunaninsa na kan cikinsa daya zube, se tunani yakeyi a ransa, waiko namiji ne ko macece. Zuciyarsa tafi bashi macece danshi yafisan diya mace Macen ma kmr Almuqri'ah, sam baya tunanin mezeje ya dawo. da yayi tunanin se ranshi ya kuma sosuwa, hatta da haushin yarinyar seda ya kara lullubeshi shi gani yakeyi ba wani sex dinsa daya zubar da cikin kawaide yarinya ta zubar masa da ciki,, wani bakin ciki ya kuma rufesa har dare besa ko ruwa a bakinsa ba, sede ya danyi baccin awanni ya tashi. Bata farka ba se wuraren sha dayan dare, taga daurin karin jini a hannunta hnklinta ya dan tashi, sbda ba a taba mata karin jinin ba, amma se ta tuna da jinin data zubar. Abdoljalal ya mata sannu,ta kalli fuskarshi nan take taga wani irin yanayi da bata saba gani ba a tattare dashi, duk yabi ya hade rai ciki kunci, ko kallanta yakiyi, itama ta dauke knta a knshi, tana mejin mararta sakayau yau hatta da ciwon ma tadenaji, , da uban nauyin da mararta takeji ynzu bataji. sede kawai tana dan ganin jiri kadan kadan, dr mus'ab yazo ya dubata tabishi da ido sosai, tana mejin kmr ta tambayeshi wani abu sede ba damar hakan. Dubata yayi sosai ya mata allurori, yayinda jinin dake shiga jikinta ko rabi beyi na, ya mata sannu ta amsa da "Yawwah, nagode Allah yasa Aljannarh ce makomarka..." Ta fadi da bebanci, Abdoljalal da dr duk suka kalleta, duk sun fahimci me take nufi dukda da bebanci tayi mgnr. Dr mus'ab shi yasan dalilin yin Adduarh tata,. Ya mata Allurori ya kula yarinyar nada dauriya, domin data farka bata nuna raganvci ba dukda bakar whlr datasha. Dr ya kara mata sannu ko kallan Jalalu beyi ba sbda haushi yake basa yanzu seya dinga abu kmr wani karamin yaro, kai kace wanda be mallaki hankalin knsa bane shi, gabaki daya halinsa ya chnza so yakeyi ya koma mara lissafin karfi da yaji, ko jaririn yaro yakeso ya koma dr besani ba.


"Zakici abinci?'' Ya tambayeta yana wani kara hade rai kmr ze mutu.. Kwata-kwata Almuqri'ah daman batajin yunwa sam, dan haka ta kalleshi kawai ba tare data bashi amsa ba ta dauke knta, ta juya knta dayan gefen. "Nace zakici wani abin? Ya kuma tambayarta gatsal, murya cikeda zallar bala'i, shi a dole and zubar masa da ciki. Almuqri'ah tasake masa bnza, ya kara tambaya a karo na uku "Ke bada ke nake mgna na..." Ya fadi cikin fushi. Almuqri'ah ta juyo ta kalleshi duk yabi ya rikirkice da bala'i. "Banjin yunwa..." Ta bashi amsa a taikaice da bebanci. Ya kara hade rai, zuciya fal haushi. Washe gari ya kasa hkri, da sassafe tana tashi a bacci shi ko baccin dmn beyi ba, ya hau matsifa.."dan wulaknci ashe kinsan kinada ciki har kika zubarmin da abuna, ni bnsani ba, kawai dan wulakanci, ai ni dakin barmin abuna, se in biyaki kudin renon cikina ki adanamin abina in kika haihu ki bani, kayana,ai bnsan kiyayyar da kikemin ya kai haka ba,, ashe haka kika tsaneni kmr ki kasheni, wannan ma ai zaki iya kasheni tinda kin kashemin jinina..." Almuqri'ah tayi shiru tana nazarin klmnsa ita sam bata fahimceshi ba, har ya gama haushnsa sam bata gane me yake nufi ba, zuwa can kuma tace "Wani cikin?'' Da babanci.a hasale Abdoljalal yace "bansani ba, cikina mna da kika zubar, cikina na jikinki da kika zubarmin da kayana dan tsabar wulaknci dacin mutumci...." Har yanzu de Almuqri'ah bata fahimceshi ba, tayi shiru kawai,ta zubawa sarautar Allah ido. Dr mus'ab ya shigo ya sameshi yanata sababi, bebi ta knshi ba ya duba Almuqri'ah , yaga jinin dake jikinta yayi rabi, ya zauna ya mata bayanin ciki ne da ita amma ya bare. Seda dr ya mata bayanin ta fahimci dalilin matsifar Abdoljalal, watoma sharri ze mata ya zubar da cikinsa da knsa, yace itace dan itade tasan batasha komi ba, tinda ya sadu da ita ya sauka dasafennan bata kara gane kntaba. Dr ya fice a dakin byn ya gama dubata, ya bata magunguna ya cire mata jinin yace ma Abdoljalal ya bata abinci shine kawai mgnr data hadashi da Abdoljalal, wanda keta faman kumbure kumber. Brush ya taimaka mata tayi, itama haushinda takeji dande bata da yadda zatayi ne dole sede dan tayi take iya tafiya, sbda jirin datake dan gani..., ya bata abinci taci kadan sbda bakinta ba ddh, se kumbura yakeyi shikam yana niyar fashewa. Kwanansu goma a asibitin dr ya sallamesu, duk kwanakin dasukayi a asibitin yana bata kulawa sosai, ammfa be bar kumbure kumbure ba, dan daya kalleta se haushi ya rufesa shi a dole ita ta barar masa da ciki. Sam Almuqri'ah taki bi ta knsa sbda dr yace mata ta kyaleshi da kanshi ze gane kuransa tinda ba a kan gaskiya yaketa bambamin tsiyar ba...duk rashin cikin da yyne yaketa wannan haukan, abinka daba sabam ba.... (sadda Abdoljalal benan ne a asibitin yaje gida ya dawo, dr ya samu dmr gaya mata wannan mgnr).












Paid book ne 08101626484






29
Adamawa yola.
Cikin temakon mahaliccin sammai da kasai, ubangijin da ba'a dogaro dashi a tabe, sede a fuskanci jarabawa, kuma Allah baya jarabtar wanda ba mumini ba, domin gwajin karfin imanin bayinsa mumina. Hajiya salma tasamu saukin jikinta sosai, sede fa akwai ciwon da baze warke ba a zuciyarta wannan sede mahalicci inya yanke mata shi, Shine soyayyar danta da tsananin kwad'ayin san ganinsa.


A kwanakinnan mafarkinta a kan abdoljalal ya chanza, ada ganinsa takeyi a cikin wani irin duhu wasu muggan mutane na janshi, amma a halin yanzu, gabaki daya mafarkanta sun juye ganinsa takeyi a wani irin haske, wanda rabinshi haske ne rabinshi duhu ne, se tadinga ganin shi Abdoljalal din na tinkaro hasken duhun kuma yana tunkararsa, a kullum cikin sadaka take., yau kawai seta tashi da kwad'ayin san ganin d'anta ko zata samu sassaucin zuciyarta ita koda ganinsa ne tayi ko me ze mata kawai tanaso taga d'anta a yau, koda ze zageta ta uwa ta uba, daman tin tini takeson zuwa inda yake ta ganshi me martaba ke hana shike tausar mata zuciya. Bayan tayi asubahi yau ko laziminta data sabayi a kullum batayi ba, ko wanka batayi ba, tasa jallabiya baka, ta fito compound din gidan, tasa dreva dinta ya kawo mota inda take, sauri-sauri takeyi gudun kada me martaba dayaje masallaci ya dawo ya sameta, sbda yana samunta ze dakatar da ita daga zuwa taje taga danta ita kuma tana tsananin bktr hkn, jiya ma kusan kira goma ta masa wayoyinsa kashe, a kullum seta kirashi koya shiga baya dauka, gabaki daya Saude ta rabasu bawai rabuwar wasa ba, ko lambar mahaifiyarsa bayaso yagani a saman screen din wayarsa. Dreva ya kawo motarta inda take, ya bude mata gidan baya ta shiga ya mayar ya rufe yana me mamakin ina kuma Sarauniya zataje da asubarnan. Dreva din ya shiga mazaunin dreva ya juyo ya kalleta fuskarsa daukeda karin bayanin ina zasuje..."muje abuja..." Dreva ya zaro ido yace "Abuja kuma a mota hajjaju?'' Sbda ko taraba basa zuwa a mota Sede a jirgi tanada jirgi mallakinta ne dashi suke zuwa inda zasuje da dreva din tukin jirgin nata. Hajiya ummu salma tayi shiru tana naxari, bawai nazarin maganganun Dreva dinta ba, aah nazarin cikin abuja da kaduna a ina zata samu Abdoljalal dinta. "Muje kaduna kawai..." Zuciyarta ta bata hakan Kuma ta furta hkn..dreva yace "ranki ya dade Allah yaja zamaninki matar sarki uwar jalalu saraki, gimbiya yar hajiya jikar hajiya,, gimbiya ai baze yuba muje kaduna a mota ranki ya dade sede a shirya miki jirgi gimbiya matar me martaba, Allah ya kara lafiya..." Ya fadi cikin ladabi. Hajiya salma tace "No muje a motarma is okay ai kasan gidan d'ana jalalu a kaduna kou?" Se tambayar tata tabawa hassan Dreva tausayi, kaf ma'aikatan gidan sun san halin da take ciki. "Nasani ranki ya dade..." Ya bata amsa cikin ladabi hadi da tausayawa. Hajiya salma ta sauke ajiyar zuciya tana mejin san danta na kara taso mata tace "Nan zaka kaini..maza ka tada mota mu tafi..." Ba musu hassan dreva ya tada motar, domin dolensa ne yabi umarni. Dai-dai sun iso get din gidan na farko Me martaba yafito daga masallacin dake cikin gidan ganin za a fita da motar Hajiya salma kuma yasan ba a fita da motar dole sede in hajiya salmar ce zata fita a cikinta,. Hk kawai ya tsinci knsa da karasowa bakin get din ya hana masu gadi bude get din gidan, hajiya salma ta kalli glass din motar taga me martaba ne, taji sam bataji ddh ba. Tayi kasa da glass din , ya zubo mata ido, itama idan ta zuba masa, kallan mamakin ina zataje da Asubahinnan me martaba yabita dashi."pls ka bari inje inga d'ana koda na yaune pls..." Hajiya salma ta fadi hadi da marairaicewa. Me martana yayi jim, daman yasan wannan dalilin ne kadai ze fiddata daga gida a wannan lokacin."tafiya kuma ba sallahma gimbiyata, sakko dan Allah..." Ya fadi cikin kwantar da murya. Ta bude baki zatayi mgna yace "Bakiyimin musu ki sakko kawai..." Ba tare data masa musu ba ta bude murfin motar ta fito zuciyarta sam ba dadih, me martaba ya tasata gaba zuwa falonta, tana Shiga falon nata ta nufa inda photon Abdoljalal yake, ta dauko hoton dake jikin bango ta rungume a jikinta, nan da nan seta fashe da kuka me martaba na tsaye jikin bangon falon yana kallanta, shi kadai yasan irin damuwar da yake ciki amma yasan ta fishi damuwa a kan d'ansu. "Ki dinga sawa kanki dangana dan Allah Ummusalma..." Me martaba ya fadi da sanyin murya, hadi da nufar inda take tsaye tana rikeda photon Abdoljalal tana kallo tana kuka. Ya amshe photon Abdoljalal dake hannunta, ya ajiyeshi hannun kujera, ya jawota jikinsa tana shashekar kuka, yashiga mata natsihohi,...da kyar yasamu ta samu nutsuwa a nan bacci yayi awan gaba da ita mara dadih, me martaba ya dauketa ya kaita bedroom dinsa, ya lullubeta kana ya dawo falon da knsa ya tattare kaf pictures din Abdoljalal dake bangaren nata duka sbda ya fuskanci in tana ganin photonsa hankalinta kara tashi yakeyi, ya zauna a falansa kawai ya dauki wayarsa yayi dealing number din Alhaji Isma'il shine wazirinsa kuma babban amininsa, hausawa sunce abokin kuka shi ake gayawa mutuwa. ., bugu daya Alhaji isma'il ya dauki wayar, me martaba yace "Inasan ganin ka yanzu isma'il..." Yana fadae hkn ya katse wayar hadi da shiga tunannika, damuwar Hajiya salma tana kada masa hankali babban abin damuwar tasa kuma gashi bata da cikakkiyar lafiya, duk lamarinsa ya maidashi kaddara, yanada kudade amma sam beda farin ciki. Ba jimawa isma'il ya iso falon nasa me martaba ya masa iso, ya karaso Ya miko gaisuwa game martaba ya amsa ya masa izinin zama a kn kujera yana zama me martaba yayi gyaran murya hadi da fara magana. "Waziri na rasa ya zanyi da salma a kan yarannan,..." Ya kwashe komi ya fadu a yau din ya gayawa isma'il kana ya daura dacewa " wallahi damuwar ta kaini kwano ina tunanin kawai zan nemi Abdoljalal in rokeshi ya dinga zuwa yana ganinta kodan lafiyarta, banasan wani abu ya sameta kwata-kwata..." Ya karashe maganar cikin damuwa. Alhaji Isma'i ma fuskarsa dauke takeda dumbin damuwa daman tinda ya kirashi yasan tasuniyar gizo bazata wuce ta koki ba. Cikin ladabi Alhaji isma'il ya fara magana "aah me martaba, ai a halin yanzu ko an nemeshi duk hanyar bame billewa bace, sbda bayin knsa bane, adduarh de damuka saba ita zamu Cigaba,, insha Allahu komi me wucewa ne....ita kuma gimbiya abin fa dole se an hada da amso mata adduarh, ranka ya dade dole abin da ciwo d'annan fa daya tilo gareta, wallahi tayi ma try Sosai.." Me martaba yace "Hakane Waziri...Toh shikenan Allah ya datar damu Amma ni ina ganin kawai kaddaratace haifar Saraki, gani nakeyi kamar a haka ze mutu bashi ba d'a bashi da jika, ga damuwarsa dake cikin zuciyoyinmu musammanma mahaifiyarsa, wallahi ina tsoron ta mutu ta sanadin bakin cikinsa, ina jiye masa duniyarnan..." Alhaji isma'il ya amshe da "Ai ba lefinsa bane ranka ya dade,,,, Adduarh de kmr yadda mukeyi a fari ita zamu ci gaba dayi, insha Allahu zansa malam muhammadu ya mata rubutu a kawo mata yau,,Allah ya temakeka insha Allahu aski yazo gaban goshi, yafi zafi dole se an jure, Allah yaja kwananka sarki jikan sarki...." Me martaba ya girgiza kai kawai, gani yakeyi kamar har abadan hankalin Abdoljalal baze dawo garesu ba. Alhaji isma'il ya dinga tausar Me martaba hadi da dannar zuciyarsa a kan damuwarsa,,me martaba yana tsananin kaunar waziri Isma'il, wazirinsa ne kuma majibancin lamuransa ne, da zuciya daya yake bashi shawarwari a kan damuwar dake Addabar me nmrtaba shida iyalinsa, wato damuwar Abdoljalal, dabadan karfin tawakkali ba dashi kansa me martaba baze iya taka kafafuwansa ba, shi kadai yasan damuwar dake ransa A kan Abdoljalal a kullum baya bacci yana bisa dadduma Adduarhsa daya ce tall byn ta Allah yajikn mahaifansa, a kan Abdoljalal. Seda waxiri yayi azahar a gidan kana ya bar gidan yana shiga motarsa ya dauki waya yayi dealing wata number me M kawai a jikin number din, bugu biyu aka daga wayar. Bayan sun gaisa daga cikin wayar Alhaji isma'il yace "tsarinmu kmr ba nasara mus'ab duk nasare ..." Cikin tsananin damuwa yayi maganar. Daga cikin wayar dr mus'ab yace "Da nasara ranka ya dade, Domin kuwa har yarinyar ma tasamu ciki da Abdoljalal sede cikin ya zube,...tin ranar na nemi number dinka yallabai bata shigaba..." Wani irin farin ciki ya rufe Alhaji isma'il hadi da damuwa duka, yace "Alhamdulillahi, koda cikin ya zube naji dadih da farin cikin hakan, munasa ran samun wani insha Allahu....sede akwai matsala..." Dr mus'ab yace "matsala cikinta muke ranka ya dade,,, me ya faru yanzu?'' Alhaji isma'il yace "iyayen Abdoljalal suna cikin damuwa a kn lamarinsam a yan kwanakinnan, musammamma ita mahaifiyarsa, kasan kwanaki na gaya maka zuciyarta har kumbura tayi, wlhi ina tsoron abubuwa da dama,, kwata-kwata banasan damuwar me martaba da duk wani jininsa saboda shi mutum ne gareni, shi mutum ne da Alkhairinsa baze mantuba har abadan a gareni...nasha da muka kullah Auren da yarinyar kaf matsalolin AAfimily ze tafi, Amma har yanzu naji shiru mus'ab, Abdoljalal ko mararin gida bayayi mahaifiyarsa na mararinsa tamkar zatayi hauka, in akwai wani solution din muyisa sbda hnklinsa ya dawo ga iyayensa..." Dr mus'ab yayi shiru hadi da sauke ajiyar zuciya byn ya gama sauraren maganganun Alhaji isma'il yace "Ranka ya dade duk wanda yayi hkri yana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login