Showing 60001 words to 63000 words out of 98220 words

tayi gaba dan zuwa sashen mahaifiyar ta.



Umman Amjad da Abban sa kewan yaronsu suke sosai ba ษ—an kaษ—an ba Umma har da ษ—an ramewanta
Suna zaune akayi sallama, jin anfara shigowa gidan sai Abba yace a qariso.
Ahmad abokin Amjad ne ya shigo sannu da zuwa Umma ta masa ya durqusa har qasa ya gaida Abba da Umma duk suka amsa da fara'a, Umma Amjad yana nan ne?
Abba yace "Amjad dai? Baku haษ—u bane kan ya tafi ko bakasan zai yi tafiya ba?
Abba ban sani ba gaskiya jeji ya shiga ne ko Doha?
Murmushi Umma tayi yarona Ahmad wani jeji qasan gaba ษ—aya ya bari fa baka da labari kenan ya tafi wani qasa acan wai Nigeria aka ce mata nake ga.
Buษ—e baki kawai Ahmad yayi amma dai ba muyi hiran zai yi tafiya ba har na barin qasa ko da yake ma bamu cika haษ—uwa ba, yanzu dai Umma a taimaka mun da layin sa da kuke waya.
"Amadu Ni da Umman taku duka wayan jagwal ne sai a hankali kawai" Abba ya faษ—a yana murmushi,. Tom Abba amma mai yaje yi?
Umma tace "wannan yaron nawa sai a hankali wani irin abota kuke haka ni mairo wai bai faษ—a maka abinda ya faru bane?"
Umma bai faษ—amun wani abu ba gaskiya kinsan sa da rashin son magana bare dogon hira, taษ“a baki Umma tayi to Allah ya shiryamun shi, Nan ta kwashe labarin duk abinda ya faru ta faษ—a masa.
Kama taษ“a Ahmad yayi ya gyara zama "wato dai ranan abun da ya kaisa gidan sarki kenan shine bai faษ—amun ba shine har da kishi kar na rakasa" abinda ya gama faษ—a a zuciyan sa kenan kamun yace "to Umma Allah sanya alkhaeryh Allah basa Sa'a ya dawo dashi lafiya, dama zan koma ne inshร  Allahu zan dawo nima in lokacin bikin yayi"
Ameen ya Rabbi yarona kaima Allah kaika lafiya Allah nuna mana lokacin da rai da lafiya
Miqewa yayi yace "Abba Umma sai wani lokacin" ya faษ—a yana yin hanyan fita, da addu'an Allah kiyaye hanya Umma da Abba suka bishi har ya fice.
Umma ta juyo ta kalli Abba murmushi tayi tace "wannan yaro naka Allah ya shirya sa wai dan ma abokin sa ne".










Sai bayan magrib Ameerah suka koma asibitin
Sun same sa a kan darduma, jikin sa da sauqi
likitan ne ya shigo yace "Insha Allah gobe zai sallamesu in yaso su qarisa jinyan qafan a gida ko nan da sati 1 zuwa 2 ne kamun ya warke sosai dan qafan ne kawai yanzu damuwa amma b abinda yake damun sa"
Godiya Daddyn Little yai wa abokin nasa yace "Allah kai mu goben frnd".
Da Ameen likitan ya amsa kamun ya fice a ษ—akin
Gaisawa suka yi duka da mara lafiyan suka masa ya jiki ya amsa da sauqi.
Har aka yi sallan isha'i suna can, sai da lokacin ya ษ—an tafi ganin dare nayi suka masa sallama
Suka kamo hanyan gida.






Sai da suka yi sallan isha'i kowa ya taษ“a hutu kamun suka tafi sashen kawun nasu wanda suke qira da baba qarami suka gaidashi da matan sa suka dawo kowa ya wuce dan ya kwanta don gajiyan bai tafi ba.
Soja ne yake ta laluษ“a wayan sa amma shiru babu wayan ba labarin waya, fitowa yayi yaje ya duba har cikin motor nan ma babu waya, abun da ya faru ษ—azu a hanya ne ya faษ—o masa a rai tabbas ba ko kokonto yarinyar nan ce ta ษ—au wayan nan.
Juyawa yayi ya koma ciki ransa a ษ“ace yayi hanyan ษ—akin da yake na su Maha, da ya Abdoul ya haษ—u yana zaune a palourn Kakus yana danna waya
Ganin Soja sai ya Abdoul ya tsayar dashi yace "our able army sai ina haka? Ya Abdoul ษ—akin su Mahreen zan karษ“o wayana
Ya Abdoul yace okay plss a turomun Mahreen ษ—in tazo ina dinning area
Tom ya Abdoul.
Sallama yayi a qofan dakin nasu, Mahreen ce ta amsa ya Habeeby ka shigo
Shiga yayi ya bata saqon qiran da ya Abdoul ke mata, himar ta jawo ta saka ta wuce dan amsa kiran da ake mata.
Bayan fitan ta in da Mahreen ke kwance tayi ษ—aษ—ษ—aya ya nufa, yana zuwa wajan ba jinkiri kawai ya jawo ta qasa ji kake timmmmm!
Kaman a mafarki ta ji an buga ta da qasa ihu ta saka 'Wayyo Mutum ko Aljan na shigesu za'a karya"

Cewa yayi "qanin ubanki ne zaki tashi ne ko sai nayi ball dake? wai ke ina wasa dake ne kam da har zaki ษ—auki wayana? Kin tashi kin ban wayana ne ko sai na harbe ki idiot kawai
Jin muryan sa kuma tasan halin sa tashuwa tayi a hankali tana hawaye dan tabbas ta bugu
ฦŠauko wayan tayi ta basa tana Allah ya isa kuma sai Allah ya saka mun.
Sarai yaji me tace amma sai ya basar heษ—e ransa yayi yace "ke me kika ce?
Tura baki tayi ni ba abinda nace
Qwafa yayi ya duba wayan yaga chajin shi bai ko sauqa ba alaman bata yi komi dashi ba kawai neman magana ne, tsaki yaja "Ni na rasa mai yasa bansa security a wayan nan ba" da ya gama seta mata zama yai hanyan waje dan ya koma ษ—akin sa.
Bayahn fitowan Mahreen wajan zama ya abdoul ya nuna mata ya mata umurni da ta zauna dan samun su tattauna
Bayani yake ta koro mata daki-daki na yacce yai kewansu sun jima basu zo Bauchi ba
Sai da ya tabbatar ta sake dashi suna hiran kamun ya numfasa a yanayi na muhimmin magana ya dube ta yace "qanwata ki aramun duka hankalinki anan zamu yi magana mai muhimmanci kinji"
kallon sa tayi da murmushi tace "yayana in da qarin hankalin ma duka na ara maka ina sauraranka"
Nan ya kwashe duk abinda ke xuciyan sa abinda yake ji game da ita tun da ya ganta ya faษ—a mata(hausawa suka ce abari ya huce shi ke kawo rabon wani).
Qanwa ta ina sonki so kuma na gaske son Aure wanda in son samu ne ayi bikin nan cikin wata 1 kai yamun nisa ma irin dai week hakan nan
Tun da ya Abdoul ya fara jawabi tayi qasa da kanta ta ษ“oye fuska a hijab da ya kai aya ya buqaci da ta ษ—ago ta basa amsa taqi ganin ya masta ko takan wayan ta dake hannun sa bata bi ba tayi hanyan ษ—aki har da ษ—an gudun ta
Dede tana shigowa ษ—akin shi kuma Soja zai fice a ษ—akin kenan suka kusa yin karo
Ransa a ษ“ace amma ganin Mahreen tsayawa yayi ya dara yace "yarinya ta kamu kenan taga handsome yayana*
Wucewa tayi tana rufe fuska bata ce komi ba.

Duk abunda ke faruwa kuwa Hajiya kakus ta fito ษ—aukan abun gurza goronta data bari a palourn sai ta tarar da draman da ake yi
Ganin duka jikokin nata na son junansu abun ba qaramin daษ—i ya mata ba( a tunanin ta Soja ma hira yaje) haka taje ta kwanta da farinciki.
Ya Abdoul ganin ta gudu sai abun ya burge sa ya kuma qara masa qaunan ta "tabbas inason mace mai kunya" abun da ya faษ—a ya miqe yana murmushi
Soja yace "yayana Allah kaimu musha biki"
Ya Abdoul da farinciki Yace "Ameeรฑ our able army"
Dariya soja ya kuma yi ya wuce wajan baccinsa, shima ya Abdoul fice wa yayi ya nufi nasa wajan baccin a sashin su, wanda yake dama da soja ne amma yace a sashen kakus zai kwana.
Ya Abdoul ko da ya koma ษ—akin sa haka ya kwanta yana ta juye-juye shi dai har ga Allah yake son qanwar tasa kuma bai qi a ษ—aura masu aure ko yanzu ba.
(haba malam abdu daga uhmn sai ehem ko a hand kake ne?
Kunga inko a hand yake ya hwaษ—an nice ourmman batoolerh mai wuqa da nama sai nasa a aura masa ita yanzu)
ko ba haka ba FAN'S ?


Mahreen na shiga ษ—aki ta samu Maha na sharar kwalla sai tace "menene ya sameki ko wani abun ya habeeby ya maki?
Maha kaman zata rufe addan nata da duka tace "Idon matambayi ne ya sameni, ba habeeby ba habibu mutum sai son jin gulma"
Kallonta Mahreen tayi tai murmushi ita dai tana farinciki bata da time na surutu da Maha
"Allah shiryaki" shine abinda tace tayi kwanciyan ta tana ta murmushi ita dai tana ji kaman ta jita a jikin yayan nata.
Mutumiyar kuwa Allah ya isa take jawa soja yafi cikin girgi.


Autan Umma yana komawa ษ—aki kwanciya kawai yayi ko ta kan wayan bai bi ba ransa fess ya fara maganin renin yarinyar nan.....

Masha Allah jama'a sahiyar alkhaery


Mu dai mun riga mun tashi๐Ÿ‘ฏ sai kuma inda qarfi ya qareโœ๏ธ






Muje zuwa
Masoyan ๐™”๐˜ผ๐™ ๐™Ž๐˜ผ๐™๐™†๐™„ ๐˜พ๐™€
๐˜ฟ๐˜ผ๐™‚๐˜ผ ๐™๐˜ผ๐™Ž๐™†๐˜ผ๐™ ๐˜ผ๐™‡๐™Œ๐˜ผ๐™‡๐˜ผ๐™ˆ๐™„๐™‰
๐Ÿ‘‡
๐™ƒ๐˜ผ๐™๐™„๐™๐˜ผ๐™๐™๐™’๐˜ผ ๐™๐™’๐˜ผ๐™ ๐˜ฝ๐˜ผ๐™๐™Š๐™Š๐™๐™‡




๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹ ุงู…ู‰ ุจุชูˆู„ุฉ๐Ÿ’‹




๐˜ฟ๐™ค๐™ข๐™ž๐™ฃ ๐™ฉ๐™–๐™ก๐™ก๐™–๐™ฉ๐™– ๐™๐™–๐™Ÿ๐™–๐™ง๐™ ๐™ช, ๐™ ๐™ช ๐™ฉ๐™ช๐™ฃ๐™ฉ๐™ช๐™—๐™š๐™ฃ๐™ž ๐™– ๐™ฌ๐™–๐™ฃ๐™ฃ๐™–๐™ฃ ๐™ก๐™–๐™ฎuka:-
08146292652
๐˜พ๐™๐™–๐™ฉ ๐™ค๐™ฃ๐™ก๐™ฎ.
09161720046
๐™”๐™ค๐™ช ๐™˜๐™–๐™ฃ ๐™˜๐™–๐™ก๐™ก ๐™™๐™ž๐™จ ๐™ค๐™ฃ๐™š, ๐™ญ๐™–๐™ข๐™ช ๐™ข๐™–๐™ ๐™ช ๐™ฉ๐™–๐™ก๐™ก๐™–๐™ฃ๐™ ๐™ช ๐™– ๐™ง๐™–๐™๐™ช๐™จ๐™– ๐™ข๐™–๐™ž ๐™จ๐™–๐™ช๐™ฆ๐™ž, wai hausawa sukace sai an gwada akan san na qwarai. Ni Hareeyh ina maraba da ku masoya, har da alakoron talla inayi๐Ÿ˜


# ๐˜พ๐™ค๐™ข๐™ข๐™š๐™ฃ๐™ฉ
# ๐™‡๐™ž๐™ ๐™š &
# ๐™จ๐™๐™–๐™ง๐™š
๐Ÿ’ฆ๐Ÿ’ฆ๐Ÿ’ฆ๐Ÿ’ฆ๐Ÿ’ฆ๐Ÿ’ฆ๐Ÿ’ฆ


๐™”๐˜ผ๐™ ๐™Ž๐˜ผ๐™๐™†๐™„ ๐˜พ๐™€๐™€


๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐˜ผ๐™ฃ๐™™ ๐™’๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ฉ๐™š๐™ฃ

๐˜ฝ๐™ฎ


๐™ƒ๐™–๐™ง๐™ž๐™ง๐™– ๐™จ๐™–๐™ก๐™ž๐™๐™ช ๐™ž๐™จ๐™–


(๐™๐™ฌ๐™–๐™ง batoorl)

ุงู„ู„ู‡ู… ุตู„ู‰ ูˆ ุณู„ู… ุนู„ู‰ ุณูŠุฏ ู†ุง ุฑุณูˆู„ู„ู‡ saw๐Ÿ–ค๐Ÿค


_______________________________________________________________


๐Ÿ…ฟ๏ธ 45&46



๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹ ุงู…ู‰ ุจุชูˆู„ุฉ๐Ÿ’‹













Kasancewan yau Sunday ba aiki da sassafe Ameerah ya haษ—a kayan karyawa suka shirya suka nufi asibiti.
Isan su asibitin direct wajan abokin nasa ya nufa ita kuma Ameera tayi ษ—akin da mara lafiyan nasu yake
Da sallama ta shiga ษ—akin ya amsa mata
Wajan gadon taje ta zauna kamun ta gaida shi
Yaya na fatan ka tashi lafiya ya qarfin jiki?
Lafiya Alhmdlh jiki da sauqi sosai
Masha Allah haka muke so yayana Allah qara afuwa
Ya amsa da Ameen daga haka bai qara cewa komi ba Ganin haka itama bata ce uffan ba
Suna zaune shiru Daddyn Little yayi sallama ya shigo
Amsawa suka yi a tare ita da mara lafiyan
Gaisawa suka yi da Daddyn Little ya masa ya jiki? Yace "da sauqi sosai"
Ameerah ce tace "husby har ka karษ“o mana Sallaman?
A'a wiffey ban same shi ba kinsan yau Sunday ba lallai yazo da wuri ba ga kuma munyi sammako
Tace "Tom shikkenan sai kazo nasa maku abun karyawa"
Sauqa tayi ta shumfiษ—a masu babban darduma ta jawo kondon kayan karin ta zuba masu peppe chicken da chip's sai soyayyen kwai ta haษ—a masu tea kowa da cup na sa.
Yayana ka sauqo ku karya ko
Ba musu ya sauqo a gadon suka zauna tare shi da Daddyn Little kowa ya ษ—au spoon
Chips en yaci kaษ—an sai kuma peppe chicken, a jiye cokali yayi ya ษ—au cup na tea yana kurษ“a
Daddyn Little ne yaci abinci sosai da ya gama ya ษ—au tea shima
Suna gamawa ta masto ta tattara wajan sannan ta koma ta zauna
Bayan wasu lokuta Daddyn Little barin danna wayansa yayi ya maida aljihu, miqewa yayi yace "ba na koma wajan likitan nan ko ya zo" Ameera ta amsa adawo lafiya to
Office na likitan ya nufa cikin sa'a kuwa dai-dai isan sa qofan office ษ—in lokacin likitan ke isowa shima, da murmushi suka kalli juna Daddyn Little yace "kai man wanne irin likita ne kai haka ka tsaya soyayya kabar mu a asibiti tun qiran asuban farko".
Dariya ya saka wato dai freind sammako kuka yi gaskiya sannu da qoqari Nikam inacan manne da matata sai yanzu aka barni na fito
"ฦŠan iska Zaka ji dashi ai Nikam buษ—e mana qofa mu shige" Daddyn Little ya faษ—a yana dariya
Tare suka shiga office ษ—in da sallama, likita ya zauna a wajan zaman sa shi kuma ya nema wajan zama ya zauna
Gaisawa suka yi suka ษ—an taษ“a hira kamun Daddyn Little yace "kaga frnd sallame ni nasan zaka je duba Patience's naka so kar na ษ“ata maka lokaci a sallamemu mukam.
sallama ya rubuta masu sannan da sauran magungunan da ake buqata na game da qafan nasa
bayani ya masa yacce za'a sha da na shafawa duka sannan ya kamata ya kai sati a gida kamun ace ya fara fita sai dai yana da kyau ya dinga mosta qafan yana ษ—an takawa dan zai fi saurin warke wa ko bai cika sati cif ba
Daddyn little yace "bakomi doctor Insha Allah za'a kiyaye fitansa yanzun fatan mu dai Allah sa ya warke da wurin
Musabaha suka yi ya kuma yiwa abokin nasa godiya yai masa sallama ya fice a office ษ—in
Wucewa pharmacy dake cikin asibitin yayi dan ya sayo maganin da aka rubuta a hanya ya haษ—u da Abba ya shigo qara duba marar lafiya kamun ya wuce don jiya bai samu komawa ba.
Tare suka je pharmacyn aka basu maganin duka da suka je wajan cashier Abbane ya biyan kuษ—in duka yace Daddyn Little ya bari
Suna gama biya suka koma ciki wajan su Ameerah
Gaishe da Abba yayi suna tafiyan sannan ya masa godiya Allah qara arziqi Abba l
Ameera ganin Abba sai taji daษ—i sunkuyawa tayi ta gaida Abban nata ya amsa da fara'a yace "sannunku da qoqari mamana"
Gaisawa suka yi da mara lafiyan
Ya masa ya jiki? amsawa yayi da sauqi Alhaji

Umma ya qira bayan sun gaisa sai ya bawa Ameerah wayan
Karษ“a tayi ta gaisa da Umman, tambayanta mai jiki tayi tace "da sauqi sosai har an sallamemu"
Umma tace ta basa wayan su gaisa
miqa masa tayi "yaya na ga Umma ku gaisa"
Amsan wayan yayi ya kara a kunnen sa, lumshe ido yayi bayan Jin sallaman Umman Ameera
Bai san meyasa ba jin muryan wannan baiwar Allahn na rage masa kewan Umman sa.
Gaisawa suka yi tace masa "yanzu ya jikin naka yaro na?
ya amsa da sauqi Alhamdulillahi
Addu'oee tai masa sosai wanda yasa shi Jin daษ—i fin tunani gaba ษ—aya sai yake jin kamar Ummansa ce.
"Ameen ya Hayyu ya Qayyum Nagode sosai Umma Allah saka da alheri"
Suka yi sallama ya miqawa Ameerah wayan
Sallama itama suka yi tace" ga shinan Umma ba na miqa masa"
Daddyn Little ta miqawa wayan tayi amsa yayi suka gaisa da surkar tasa
yace "Umma bakomi Allah qara girma mungode sosai"
Ya miqawa Abba wayan bayan sunyi sallama
Abba kara wayan yayi a kunne ya fita a ษ—akin.


Ameera tattara komi da suka zo dashi asibitin tayi Daddyn Little na taya ta yana kwashewa ya kai masu motor
Bayan sun kai komai motor Taimaka wa mara lafiyan yayi yana ษ—ingisawa har suka isa in da motorn nasu yake Parke, suna isa yabuษ—e masa murfin back seat ya shiga ya zauna.
Sallama suka yi da Abba, escorts nasa suka tada motor sae filin jirgin dake garin Abuja
Gaba Ameerah ta shiga Daddyn Little ya shige mazaunin driver ya jasu sai gida
Hira suke sama-sama a motorn suna sako sa shi kuwa yayi nisa a tunaninsa baya amsawa hiran nasu ma (dama shiba ma'abocin surutu bane).
Driving yake a hankali
Juyowa yayi ya tambayesa bro akwai abunda kake buqata mu tsaya mu saya kamun mu wuce gida?
Girgiza kai kawai yayi bai ce komi ba
Ameerah ce tace "husby ka tsaya musai koda fruits ne to"
Tsayawa suka yi suka saya da yawa kaman masu sari, aka sa masu a boot en motorn suka biya suka qarisa gida
Suna isa mai gadi ya buษ—e masu qofan yana ranka ya daษ—e sannunku da dawowa amsa masa yayi
Parking space ya isa yai parking motorn
ฦŠakin da suka shirya already don shi a balconyn gidan Daddyn little ya temaka masa ya kaisa har ษ—akin
ฦŠakine madedeci mai ษ—auke da duk wani abunda mutum zai buqata a ษ—aki
Gado,walldrop,resting chair,mirrow,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login