Showing 84001 words to 87000 words out of 98220 words

you ฦดammaya zanzo Inshร  Allah kuma in nazo all those peck's da komi duka sai anmun har da hug lemme tell you ba dau komi kice sai nazo ba ke mai wayo ko? Tom ina hanya kede ki fara shirin tarbana.
Sanin rigiman sa murmushi kawai tayi tace "as you wish ya rouheei Angon Indon sa Allah kawo mun kai lafiya"
Waya suka cigaba da yi cike da soyayya da nishaษ—i gami da begen junan su (Romeo da Juliet)
Maha na isawo cikin palourn waje ta samu ta zauna tace "Ummeyh nikam ina my son?" Ooh! rigimammen ษ—an za kice, ai tun ษ—azu yana can ku na wajan habeeby"
Shiru tayi bata qara cewa komi ba ta sa hannu a bowl da Ummeyh ke shan fruit ta ษ—au yankan abarba ta kai baki.
Can suna zaune shiru kowa hankalin sa na kan TV qira ya shigo wayan Umma da itama dai-dai tana fitowa daga ษ—akin ta kenan, zuwa tayi ta ษ—auki qiran ganin Ameera ke qiranta.
Gaisawa suka yi, da Ameera tace Umma "'kinsan me? A'a ya akayi ko haihuwan ne yazo.
La Umma haihuwa dai tun yanzu, Umma tace "Tom naa sani ko shi ษ—in ne zaki haifi ษ—an baiwa"
Murmushi Ameera tayi tace "Umma ba wannan ba albishir kekam"
"Goro" inji Umma
Tom Farin goro ko ja Ummata?
Umma a hasale da ษ—an faษ—a-faษ—a tace "Ameerah yaushe muka fara wasa dake?ki fita idona".
Umma sorry tom Ummanmu, yanzun nan muka gama waya da yaronki shine albishirin dama.
Murmushi kwance a fuskan Umma kaman an mata bushara da kuษ—i, tace "dan Allah dai? ya yake? dariya Ameerah ta saka amma dai yanzu kam naci goro, Umma Allah son da kike masa ya fara yawa zamu fara kishi muma"
Umma tace "basak kuyi kishin ba dan gidanku wa ma yasan kuna yi? Kuma na fasa bada goron nikam ma kashe waya Bmbara na qirasa"
Tom Ummah daman ma zan tura masa layin ya Abdoul ko address ษ—in gidan duk wanda ya samu
Yauwa ฦดar kirki Allah maki albarka, ki tura masa nima zan qirasa yanzu kuma za muyi waya da Abdul ษ—in nima,yauwa Ummeyhn ku ma tazo yaushe zakuzo gaidata? Dan ku kayi latti cinye staraban zamu yi.
yaushe Ummeyh tazo wayyo! daษ—i dan Allah Umma ki bata wayan naji muryanta, ai zuwa ya zama mun dole.
Umma tace "Bazan bada ba uwata ba dai kina da layinta ba qira ta nikam yarona zan qira" Sallama suka yi Ameerah na dariya Umma ta kashe qiran.
Ummeyh ce ta kalleta tace "Umman yara wato baza ki haษ—a ni da ษ—iyata ba?
Bafa haka bane Gwaggon yara, wannan bawan Allah da na baki labari mijinta ya buge shine fa suka bari ya tafi Bauchi shi ษ—aya kuma ba ษ—an Nigeria ba, "Ina ji dai ya warke ai umman yara?" Ummeyh ta tambaya
Bai wani warke wa ba fa baqin hali ke damun su Gwaggon yara, Ameera kam da mijin ga sai a hankali, kinji-kinji yacce muka yi ranan, kwashe yacce suka yi ranan da Ameerah tayi ta faษ—awa Ummeyh"
Subhanallah yanxu dai ya ake ciki tom?
Wai layinsa ya shiga shine nake son qiransa, Ai kuwa ya kamata yaje nasan Gwaggo kam zata yi masa masauqi ita da son yaran nan.
Nikam ma Ummeyhn yara da ya yarda ya zauna kamun muje.
Ummeyh tace "Gaskiya kam dan ya kamata muma mu gaidashi da jikin, in yaso sai mu shiga Bauchin da wuri ba?
Eh tom yanzu dai sau yayanki ya dawo muji ta bakinsa.

Mahreen tattabaru angama soyewa, sallama suka yi tai masa addu'an da yake matuqar qara masa qaunarta
"Allah kulamun dakai rouheei
Allah tsaremun kai rouheei
Allah Buษ—a maka hanyoyin samun ka rouheei
Ya rabbi ...................."
Ameen y Rabbi Yar aljannah ta, Mar'atussaliha ta, ki kula sosai ko.
Insha Allah yayana
Murmushi yayi daga ษ—ayan ษ“angaren bai ce komi ba, Ita ta kashe wayan tana mai jin annashuwa da nishaษ—iii.
Tashuwa tayi tai hanyan palour itama
Bayan ta kashe wayan bai wuce da minti biyu zuwa uku ba text ya shigo wayan ta, buษ—ewa tayi da mamaki ta zaro ido ganin tulin kuษ—in da ya Abdoul ya tura mata wai na gyaran kai, addu'oee ta kuma masa kamun ta miqe cikin farin ciki ta nufi palour.
Da sallama ta shiga palourn gefen Ummeyh ta zauna, sannu da hutawa Ummeyh am,
Wani hutawa ฦดar nan ko bacci banba, ai gobe kar ma ku yarda na kama qafanku a hanyan ษ—aki na dan baccin gajiyan nan duka sai nayi sa na samu naje wajan stohuwata Nima.
Umma shiga lambobin ta tayi, layinsa ta nemo tayi dialing farincikk ya cika ta jin ya shiga sai dai har ya gama ringing ba'a ษ—auka ba qara qira tayi again haka..




Amjad Jin shiru bata turo masa saqo ba kuma bata qira ba sai ya ajiye wayan a gefe ya ษ—an kishingiษ—a akan yana yajira qiranta, a haka har bacci ษ“arawo ya sace shi.


Sashen baba qarami na nufa dan hayaniyan da nake ji, tun ina shiga palourn sashen nake jin ashar na tashi, da hanzari na garzaya ciki dan jin meke faruwa?
Mama hansatu ce ke cewa "haba ke kuwa saratu me na damuwa haka har da ashar? Ai ba komi dan ya aureta bakya ga uwarsu da ubansu nada kuษ—i duka ba.
Mama saratu tace "Kutumar uban can (a'uzubillahi) hansatu dan dai ba kece ba shiyasa za kice haka, ai in iyayensu na da kuษ—i, nima yarona tufarkalla Masha Allah shima yana da kudin sa atou, ke hansatu har yau bakisan rayuwa na kuma bakisan ษ—an Adam da son zuciya ba, sai kiga sun kwashemun yaro tass sun shuษ—e sa sun lashe sa sun maida shi sakarai shagiri girbau.
Dubi fa yacce uwar tasu take mana mijinta ya zamo kaman maloho ko nace gaษ“o(sakarai) komai sai abun da tace zai yi, ke baki Ga zuwansu kwanaki ba ne?
Ai wallahi abinda bazan ษ—auka ba kenan ko sama da qasa zata haษ—e wannan buro-uban ba da ni saratu ba in dai na cika haifaffiysr ฦดar sunna ko zanyi yawo stirara Abdul bazai Aure ta ba.
Hhhh! Hansatu tana dariyan da daga ka gani kasan na makirci ne tace "saratu sama da qasan bata dai haษ—en ba ai tuni kika yarje har da sa albarkazaki sa musu da addu'ar a haifa mans shiryayyun jikoki, faษ—in mama hansatu tana dariyan mugunta, Kuma da kike maganan mallakewa ba sai munso za'a mallake mana yaro ba ai ba zama zamu yi ba saratu".
"Hmmn hansatu kenan ni dae Ina dede dasu duka kawai na ษ“ula ganye ne ina kallonsu inbasu sani ba daga shi balagaggen marar kunyan har da figeggen ubansa zasu haษ—u dani tun da ba wanda ya ษ—auke ni da daraja har ana maganan auren sa ban saniba tom baze auri Mahreen ba in de sunana saratu kuma nono na yasha, ai ko ke yadikko da baki haihu ba za'a faษ—a maki kuma kema kyaji haushin rashin faษ—a maki da akayi bare ni da na ษ—au ciki wata goma na haife, in ba rashin ganin daraja ba su ya kamata na riga Gwaggo ma jin wannan zancen, ayi mu ganine in tusa zata hura wuta" Kwafa mama saratu tayi, dan kana ganinta kasan a cike take fam da masifa.
Tashuwa hansatu tayi dan maganan rashin haihuwan da mama saratu tayi ya ษ“ata mata kawai tayi shiru ne sai tace "tom saratu ba naje na ษ—aura girki nikam kamun ya auro mana surka ta hutarmu yin aiki".
shewa suka yi suka tafa hansatu ta fice a palourn mama saratu.
Mama Hansatu tana shiga ษ—akinta me zata yi in ba dariya ba, har da kama ciki can ta miqe fuska a haษ—e kaman ba ita ta gama dariya yanzu ba ta tsaya tace "saratu dani kike maganar kici gaba damun gorin haihuwa ko yanzu yaranki basu fi qarfin su mutu mu zama ษ—aya ba na barsu ne kawai dan taqaicin su ya kashe ki, wawuya jahila jaka mara tunani ance maki duk zamanmu dake inasonki da alkhaeryh ne ko dan Allah nake maki wasu abun ai wallahi sharri da kaina nake tura maki se dai ki samu ki stallaka in Allah ya soki tunda dai kin ษ—an riqe azkar, amma ba komi muje zuwa zaki sha mamaki dan tabbas sai naga bayanki duk kuzo a bayana a auro ku amma ku haihu ban haihu ba sannan yaran ku su ษ—aukaka wallahi yacce nayi sanadiyan yaron wancan shashashar matan kema ษ—ukda ษ—an ki ya girma baifi qarfin na hallakar dashi ba (wa'iyazubillah Allah ka shiryamu). Ina ji ina ganin ษ—an ki ya auri wannan kyakkyawan yarinya ga iyayenta kuษ—i na qyale caษ“, ace mun iyayen baban ta sune masu sarautan Adamawa sannan na bari ษ—an ki ya haษ—a jini da sarauta ai wallahi sai dai bayan rai na itama ฦดar taki ko mashinshini ba zata samu ba sai dai ta dawwama tana wa stohuwar kikalkin kakar su aiki kamar haka mtssswww.
Lamarin ki saratu Ba malami ba boka zugi ya isa kisa a fasa auren ke da kanki ko na ss ki stinewa yaron ki kece da asarar ba ni ba hansatu tun da ke janitalau ce baki da hankali baki da tunani, sannan ina dab da saki aikata shirka akan auren nan
Jamila(Ummey) ke kuwa haka zaki qarashi rayuwanki sai dai gani daga nesa bake ba ฦดan uwanku bare uwarku ke da Nigeria ko mutuwa uwarku tayi Bazan bari kizo ba duk soyayyan da yayunkk ke maki sai nasa ya koma mugun tsana kin rasa mai ke maki daษ—i a duniya, tunda a lamarin yaranki dole akwai Aure Tom sai dai suga ana Auren daษ—i duk dagewan kakannin su a kansu(su Arษ—o) sai nasa sunyi auren qasqanci Auren wahala.
Sai kuma ta kwashe da dariyan da sanda bangon ษ—akin ya amsa kaman zai stage Hhhhhhhhhhhhh!! Sai ni hansatu, hansai tamai gari naci aradu Nasha yasin na ci dubu sai ceto



Shine bai tashi baccin da yake yi ba sai da ake qiran Sallan magrib, da salati da addu'a ษ—auke a bakinsa ya farka yana miqa, jin qiran Sallan sai ya tashi ya zauna yana kai har magrib yayi caษ“ astagfirullah Allah na tuba.
Tashuwa yayi bebi ko takan wayan sa ba ya ษ—au buta ya shige bayi......


Muje zuwa fan's โœ๏ธ
ฦณAR SARKI CE daga dausayin Alqalamin uwar batoorl
Justice Hareeyh๐Ÿ•Š๏ธ



๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹ ุงู…ู‰ ุจุชูˆู„ุฉ๐Ÿ’‹


๐˜ฟ๐™ค๐™ข๐™ž๐™ฃ ๐™ฉ๐™–๐™ก๐™ก๐™–๐™ฉ๐™– ๐™๐™–๐™Ÿ๐™–๐™ง๐™ ๐™ช, ๐™ ๐™ช ๐™ฉ๐™ช๐™ฃ๐™ฉ๐™ช๐™—๐™š๐™ฃ๐™ž ๐™– ๐™ฌ๐™–๐™ฃ๐™ฃ๐™–๐™ฃ ๐™ก๐™–๐™ฎuka:-
08146292652
๐˜พ๐™๐™–๐™ฉ ๐™ค๐™ฃ๐™ก๐™ฎ.
09161720046
๐™”๐™ค๐™ช ๐™˜๐™–๐™ฃ ๐™˜๐™–๐™ก๐™ก ๐™™๐™ž๐™จ ๐™ค๐™ฃ๐™š, ๐™ญ๐™–๐™ข๐™ช ๐™ข๐™–๐™ ๐™ช ๐™ฉ๐™–๐™ก๐™ก๐™–๐™ฃ๐™ ๐™ช ๐™– ๐™ง๐™–๐™๐™ช๐™จ๐™– ๐™ข๐™–๐™ž ๐™จ๐™–๐™ช๐™ฆ๐™ž, wai hausawa sukace sai an gwada akan san na qwarai. Ni Hareeyh ina maraba da ku masoya, har da alakoron talla inayi๐Ÿ˜!!!


# ๐˜พ๐™ค๐™ข๐™ข๐™š๐™ฃ๐™ฉ
# ๐™‡๐™ž๐™ ๐™š &
# ๐™จ๐™๐™–๐™ง๐™š


๐Ÿ’ฆ๐Ÿ’ฆ๐Ÿ’ฆ๐Ÿ’ฆ๐Ÿ’ฆ๐Ÿ’ฆ๐Ÿ’ฆ


๐™”๐˜ผ๐™ ๐™Ž๐˜ผ๐™๐™†๐™„ ๐˜พ๐™€๐™€


๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐˜ผ๐™ฃ๐™™ ๐™’๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ฉ๐™š๐™ฃ

๐˜ฝ๐™ฎ


๐™ƒ๐™–๐™ง๐™ž๐™ง๐™– ๐™จ๐™–๐™ก๐™ž๐™๐™ช ๐™ž๐™จ๐™–


(๐™๐™ฌ๐™–๐™ง batoorl)

ุงู„ู„ู‡ู… ุตู„ู‰ ูˆ ุณู„ู… ุนู„ู‰ ุณูŠุฏ ู†ุง ุฑุณูˆู„ู„ู‡ saw๐Ÿ–ค๐Ÿค


_______________________________________________________________




๐Ÿ…ฟ๏ธ 61&62



๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹ ุงู…ู‰ ุจุชูˆู„ุฉ๐Ÿ’‹







๐“๐€๐‹๐‹๐€!! ๐“๐€๐‹๐‹๐€!! ๐“๐€๐‹๐‹๐€!!


๐Ž๐”๐Œ ๐€๐‹'๐€๐Œ๐„๐„๐ ๐ƒ๐€๐“๐€ ๐’๐„๐‘๐•๐ˆ๐‚๐„
๐ฒ๐จ๐ฎ๐ซ ๐ฌ๐š๐ญ๐ข๐ฌ๐Ÿ๐š๐œ๐ญ๐ข๐จ๐ง ๐ข๐ฌ ๐จ๐ฎ๐ซ ๐œ๐จ๐ง๐œ๐ž๐ซ๐ง.


๐Š๐ฎ๐ณ๐จ ๐ค๐ฎ ๐ฌ๐š๐ฒ๐ข ๐๐š๐ญ๐š ๐ฆ๐š๐ข ๐ฌ๐š๐ฎ๐ช๐ข ๐ฆ๐š๐ข ๐ข๐ง๐ ๐š๐ง๐œ๐ข ๐๐จ๐ฆ๐ข๐ง ๐ ๐š๐›๐š๐ญ๐š๐ซ ๐๐š ๐ก๐ข๐๐ข๐ฆ๐จ๐ฆ๐ข๐ง ๐ค๐ฎ ๐š ๐จ๐ง๐ฅ๐ข๐ง๐ž ๐ค๐จ ๐ค๐ฎ๐ฐ๐š ๐ค๐š๐ฅ๐ฅ๐š๐œ๐ž-๐ค๐š๐ฅ๐ฅ๐š๐œ๐ž ๐š ๐˜๐Ž๐”๐“๐”๐๐„ ๐›๐š ๐ญ๐š๐ซ๐ž ๐๐š ๐๐š๐ญ๐š๐ง๐ค๐ข/๐๐š๐ญ๐š๐ง๐ค๐š ๐ฒ๐š๐ฒ๐ข ๐ฌ๐š๐ฎ๐ซ๐ข๐ง ๐ณ๐ฎ๐ช๐ž๐ฐ๐š ๐›๐š. ๐ˆ๐ง๐š ๐ฆ๐š'๐š๐›๐จ๐ญ๐š ๐š๐ฆ๐Ÿ๐š๐ง๐ข ๐๐š ๐ค๐š๐Ÿ๐š๐ซ ๐ฌ๐š๐๐š๐ฐ๐š ๐ญ๐š ๐“๐ˆ๐Š๐“๐Ž๐Š ๐ฆ๐š๐ฌ๐ฎ ๐ค๐ฎ๐ค๐š๐ง ๐ฌ๐š๐ฎ๐ซ๐ข๐ง ๐ช๐š๐ซ๐ž๐ฐ๐š๐ง ๐ƒ๐€๐“๐€ ๐ญ๐จ ๐Ÿ๐š ๐ฐ๐š๐ง๐ง๐š๐ง ๐›๐š ๐ค๐š๐ฆ๐š๐ง ๐ค๐จ ๐ฐ๐š๐ง๐ง๐ž ๐›๐š๐ง๐ž ๐ฌ๐š๐ข ๐š๐ง ๐ ๐ฐ๐š๐๐š ๐š๐ค๐š๐ง๐ฌ๐š๐ง ๐ง๐š ๐ช๐ฐ๐š๐ซ๐š๐ข ๐๐š๐ง ๐ข๐ง๐ ๐š๐ง๐œ๐ข ๐๐š ๐ค๐ฎ๐ฆ๐š ๐ช๐š๐ซ๐ ๐จ ๐ ๐š ๐ƒ๐€๐“๐€๐ง ๐ค๐š ๐ญ๐จ ๐ค๐ช ๐ณ๐ข๐ฒ๐š๐ซ๐œ๐ข ๐Ž๐”๐Œ ๐€๐‹'๐€๐Œ๐„๐„๐ ๐ƒ๐€๐“๐€ ๐’๐„๐‘๐•๐ˆ๐‚๐„

๐Œ๐“๐ ๐€๐ˆ๐‘๐“๐„๐‹


๐Ÿ๐†๐ - 250 ๐Ÿ๐†๐ - 2๐Ÿ“๐ŸŽ
๐Ÿ๐†๐ - 5๐ŸŽ๐ŸŽ ๐Ÿ๐†๐ - 500
๐Ÿ‘๐†๐ - 75๐ŸŽ ๐Ÿ‘๐†๐ - 750


๐†๐‹๐Ž ๐Ÿ—๐Œ๐Ž๐๐ˆ๐‹๐„


๐Ÿ๐†๐ - 25๐ŸŽ ๐Ÿ๐†๐ - 25๐ŸŽ
๐Ÿ๐†๐ - 50๐ŸŽ ๐Ÿ๐†๐ - 5๐ŸŽ๐ŸŽ
๐Ÿ‘๐†๐ - 75๐ŸŽ ๐Ÿ‘๐†๐ - 75๐ŸŽ


๐Œ๐ฎ๐ง๐š ๐š๐ซ๐š๐ก๐š ๐ฆ๐ฎ๐ง๐š ๐ก๐š๐ง๐š bashi๐Ÿ˜Š ๐ฌ๐š๐ฒ๐š๐ง ๐ง๐š ๐ ๐š๐ซ๐ข ๐ฆ๐š๐ข๐๐š ๐ค๐ฎ๐๐ข ๐ ๐ข๐๐š(๐ข๐ง๐ฃ๐ข ๐ก๐š๐ฎ๐ฌ๐š๐ฐ๐š)
๐™๐š๐ค๐ฎ ๐ข๐ฒ๐š ๐ญ๐ฎ๐ง๐ญ๐ฎ๐›๐š๐ง ๐ฆ๐ฎ ๐š๐ค๐š๐ง ๐ฐ๐š๐ง๐ง๐š๐ง ๐ฅ๐š๐ฒ๐ข ๐๐š๐ง ๐›๐ข๐ฒ๐š ๐ค๐จ ๐ญ๐š๐›๐›๐š๐ญ๐š๐ซ ๐๐š ๐ฌ๐ก๐š๐ข๐๐š๐ง ๐›๐ข๐ฒ๐š
๐ŸŽ๐Ÿ•๐ŸŽ๐Ÿ๐Ÿ“๐Ÿ๐Ÿ‘๐Ÿ๐ŸŽ๐Ÿ๐Ÿ—
๐‚๐€๐‹๐‹/๐–๐‡๐€๐“๐’๐€๐๐

๐€๐œ๐œ๐จ๐ฎ๐ง๐ญ ๐ง๐ฎ๐ฆ๐›๐ž๐ซ
๐Ÿ•๐ŸŽ๐Ÿ๐Ÿ“๐Ÿ๐Ÿ‘๐Ÿ๐ŸŽ๐Ÿ๐Ÿ—
๐€๐ˆ๐’๐‡๐€ ๐€๐‹๐ˆ๐˜๐”
๐Ž๐๐€๐˜ ๐๐€๐๐Š.


๐’๐€๐ˆ ๐Š๐”๐๐™๐Ž๐Ž๐Ž......










Tashuwa yayi ko takan wayansa bebi ba ya shige bayi(toilet) yana fitowa ya ษ—aura alwala, cikin ษ—akin ya koma yaja qofan ya rufe ya nufi masallaci.
ko da yayi Sallahn magrib bai koma ba har sanda yayi Sallan isha'ee bayan sun idar da sallan ne liman ya ษ—an yi tunatar wa ga al'umma(wa'azi) yana idarwa jama'an masallacin suna raguwa har aka waste ya rage mutane qalilan.
Amjad matsawa yayi wajan liman yayi masa sallama suka yi musabaha sannan suka gaisa fuskan liman a sake ba yabo ba fallasa.
Liman yace "saurayi daga ina haka dan ban cika ganinka anan ba?"
Murmushi Amjad yayi yace "malam ni ba ษ—an qasan nan bane"
Ikon Allah ikon gaske yanzu tom kazo wajan wani naka ne kenan? A'a Allah gafarta malam banma san kowa ba hasali ma ban taษ“a zuwa ba yanzu ma dalili ne nazo neman wani magani ne kuma na shiga jeji sosai iya shiga na ban samu ba ko alaman bishiyar ban gani ba, kuma ance mun dama anan zan samu.
wani magani ne haka? Bawan Allah
Amjad yace "๐—ญ๐˜‚๐—น๐—บ๐—ฎ๐—ฟ ๐—ฑ๐—ฎ ๐—ธ๐˜‚๐—บ๐—ฎ ๐—ธ๐—ฎ๐—ป๐˜†๐—ฎ"
jinjina kai limamin yayi yace "kai aikam dole ka gama duba wa baka samu ba dan ba'a ta yankin nan ake samu ba sai ta jejin yankari ko can yankin Borno sambisa, amma yanzu dai a ina kake zaune(masauqinka)?
Yace "Allah gafarta malam nan bayan nan ne ba nisa"
Liman yace "to to shikkenan in ba matsala muje gida na in yaso daga nan sai ka wuce ko dan abubuwan na da qa'idodi nasan kasani ba ako ina ake shiga dashi ba.
Nagode Allah gafarta malam yanzu zanje gidan na haษ—a abubuwa na na sallami mai ษ—akin sai na zo.
to yaro shikkenan sai kazo, sallama suka yi da limamin ya fice a masallacin ya wuce inda yake kwana, buษ—e ษ—akin yayi ya haษ—a komi nasa ya bawa mai ษ—akin gefen sa makullin ษ—akin shi kuma ya fito yayi gidan limamin.
Da ya isa gidan limamin tsayawa yayi a bakin qofan yayi sallama.
amsawa akayi wata budurwa ce ta amsa tace "ana zuwa".
yana tsaye yaji an buษ—e qofan, ษ—agowa yayi suka haษ—a ido ita, kyakkyawar budurwa ce wacce a shekaru bata haura 20 years ba, ta buษ—e qofan tana tambaya waye ne?
Nazo wajan liman ne, sai tace "tom ace masa waye?
Kice masa ษ—an Qatar ne, qara kallonsa tayi kamun tace to ba na faษ—a masa, cikin gidan ta koma can ta qara fitowa tace wai ka iso.
shigewa cikin gidan tayi yabi bayan ta tai masa jagora har ษ—akin baqi bayan sun isa tayi masa iso ya shiga ya samu waje ya zauna ficewa tayi a ษ—akin.
can sai gata ta shigo da ruwa a hanunta ajiye masa tayi ta tsugunna ta gaidasa fuskanta da murmushi shi kuwa ba yabo ba fassala fuskan nasa haka ya amsa.
wai kasha ruwa baban yana zuwa, okay nagode.
Murmusawama tayi ba komi sannu da zuwa ta tashi ta fice a ษ—akin tana murmushi, bayan fitanta qofan yabi da kallo nustuwan yarinyar ya burgesa sosai.
Bayan mintuna da fitanta sai yaji sallaman liman, amsawa yayi yana sannu da fitowa malam yauwa yaro sannunka ko, waje liman ya samu ya zauna.
Durqusawa yayi ya gaida sa amsawa yayi yana yaro tashi abunka ka zauna, koma wa yayi ya zauna ya sunkuyar da kai, liman yace "yauwa baka faษ—amun sunanka ba saurayi" kansa aqasa yace "sunana Muhammad Amjad Allah gafarta malam"
Masha Allah to naji maganin da kake nema ai abinda yasa ba zaka samesa ba a jejinmu na nan saboda wasu bishiyoyin an sassare wasu kuma ba zasu yi amfani ba mugaye sun riga da sun ษ“ata su wannan ษ—inma abinda yasa na qiraka kar acan wani mugun ya gani ya ษ“ata kasan hausawa sunce shi mugu baida kama.
Hakane Allah gafarta malam Nagode sosai, a'a bakomi saurayi yanzun tunda kace kana samu zaka wuce ko? Eh malam tom mu kwana nan yau gobe Inshร  Allah da rai da lafiya sai ka wuce yanzun bana shiga na kawo maka maganin, to Malam Allah saka da alheri Nagode sosai.
tashuwa limamin yayi ya fice a ษ—akin yana faษ—in "kaqi shan ruwan ko? sosa qeya yayi.
bayan fitan limamin komawa yayi ya jingina da kujeran yana lumshe ido

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login