Showing 96001 words to 98220 words out of 98220 words

liman sallama Abdoul yaja motor, malam liman yana ษ—aga masu hannu har Motorn nasu ya ษ“ace a layin nasu gaba ษ—aya.
Juyawa malam liman yayi ya shige gida cike da kewan baqon nasa na kwana ษ—aya wanda kuma yana tunanin qara haษ—uwan su wataqil sai kuma a qiyama.
gaisawa Abdoul da Amjad suka yi wanda tun da Amjad ya shiga Motorn yake jin gabansa ya tsananta faษ—uwa, Abdoul kallon sa yayi sai yace "bros ina muka nufa?" Amjad yace "airport zaka kaini" Abdoul ya kuma kallon da ya kalli hanya yace "haba dai airport ba zaka je gida ka gaida Amarya ba? Am Amaryan ina nufin kakata gaskiya ya kamata kaje ka gaida ta inba dai kayi booking Flight na safe ba".
Amjad yace "nop banyi booking Flight ba yanzu dai in munje zanyi sai na jira, Amarya kuma inka koma kace wani jikanta na gaida ta sai wani lokacin zanzo". Murmushi Abdoul yayi ai tunda ba kayi booking jirgi ba gaskiya daganan sai gida ba wani airport da zamu ai in bankaika gida ba yau ba mai kwata na a hannun masifaffiyar stohuwar nan, kwashe yacce suka yi da Amarya yayi ya faษ—a wa Amjad yana dariya. Amjad sai da ya Murmusa jin rigiman stohuwar sai dai kuma har yanzun faษ—uwan gaban sa na yawaita, da Abdoul ya dage ba yacce zai yi qarshe yarda yayi ba dan yaso ba amma bai qudiri aniyan kwana ba yana zuwa ya gaida mutanen gidan su Abdoul ษ—in zai kawo sa airport ya samu ya shirya komi na tafiyan sa yau ษ—in nan.
Abdoul ne jin yayi shiru yace "bros ya kayi shiru? Maganan tafiya yau fa kabar sa dan anan kam ba lallai ka samu Flight direct to Qatar ba sai dai ko in zaka hau na Abuja daga can to sai ka samu na Qatar kaga kuma duka long process ne gashi yanzu rana ya fara ka bari kawai anjuma kayi booking anan sannan mijin Ameera ya maka na Qatar ษ—in in yaso d sassafe ka tafi ko in ansamu na dare sai kabi na Abuja da yamma da dare kuma ka hau na Qatar ษ—in" Amjad ba yacce ya iya haka ya aminta suka nufi GRA.
Amarya sashen baba qarami ta shiga tana bambami, kai jama'a Allah raba ษ—an mutum da wahala yo in ba wahala da tangaษ—i ba ace wai jikanka ya mai da kai birin wasa ai wannan ba ko kaffara uwar sa ke kista masa hmm! Shi uban kuma da yake maloho tangaษ—aษ—ษ—e baya iya stawatar wa an mallakesa ni Mairo na shiga uku an raba ni da yara na. Baba qarami da ke zaune a palourn mama hafsatu yana aiki a system nasa kasancewar yau yayan sa na hanya shiyasa bai fita aiki ba, muryan mahaifiyarsu da ya jiyo ne ya sanya shi rufe system ษ—in ya miqe ya nufa hanyan babban palourn da yasan bazai wuce tana can ba.
Tarar da ita yayi tsaye tana share hawayen da babu shi da gefen hijab nata, baba qarami na isowa har qasa ya durqusa yace "Gwaggo ina kwana antashi lafiya?" Wani kallo Amarya ta masa sai kuma ta fece hanci tace "yanzu ba dan ubanka mijina bane kuma ya rasu bawan na kwance cikin rahamar Ubangiji yo da sai nace dan jakar ubanka, amadu ban kwana ba kuma in mutuwa nake na rashin lafiya ba to ba ruwanka,kullum faษ—i nake ka riqe azkar da salatin Annabi za ka fi qarfin duk wanni stubbace-stubbace amma dan tsabar lalacewa da tangaษ—ewa yaron nan ba kayi, amadu baka neman albarka" baba qarami dake stungune a qasa ba abinda yake cewa sai "Gwaggo ayi haquri a yafeni".
Mama hafsatu da ke qarasowa palourn ne tace "Alhaji ai ba haquri zaka bada ba tambayan me kayi zaka yi" Amarya kallonta tayi sai tayi qwafa za tayi magana sai baba qarami ya riga ta "ke Hafsa banson rashin hankali".
Amarya tace "a'a karka sona amadu ba laifinta bane ai komai tace kai ka nuna masu ba dai baka neman albarka ba?"
Mama saratu ta qaraso palourn itama tace "Gwaggo Barka da shigowa ki zauna mana". Kallonta itama Amarya tayi sai kawai ta sa kuka "yanzu amadu fistaran da kuke shuka mun kai da matanka har ya kai haka? Wai ni da gidan Yaro na sai ance na zauna da uban wani ya gina masa gidan to banson shishishigi shigilitu, amadu kai dai Allah staremun kai amma mata sun mallake mun kai ai daษ—i na da Haruna kenan bawan Allah gashi dai mace ษ—aya gare sa kaman mahaifin sa amma yafi qarfin gidan sa yanzu dan stabar ba mai ganin girmana a gidan nan ace yaranku ma kun hure masu kunne sun fistare qafafunsu sun ษ—auko baqin halin ku" baba qarami jin haka to yasan tabbas wani abun Abdoul ya mata dan in hayra ce ba mai jin tsakanin su suyi faษ—an su su shirya acan ba mai ji amma in ta shigo tana faษ—a tom indai yara ne Abdoul ne ya mata abu ko kuma Autan ta Jamila.
Ajiyan zuciya baba qarami ya sauqe yace Gwaggo kiyi haquri Insha Allah zan ษ—au mataki kiyi haquri ki zauna, Amarya kujera ta samu ta zauna har da ษ—aura miqe qafa tace "tunda kana neman albarka har da haษ—a ni da Allah tom na zauna Allah maka albarka amadu na Allah yasa ka gama da duniya lafiya yanzu dai amadu kaji storon Allah kaji storon haษ—uwa da shi wai ace ba za ka yiwa yaranka faษ—a ba ka nuna masu nice uwarka nice na haifeka sai sun kyautata mun nasa maka albarka kamun suma zasu samu kasa musu albarka su gama da duniya lafiya" ayi haquri Gwaggo Insha Allahu za'a gyara.
Ai nasan zaka gyara amadu wai ni zancewa Abdu ya jira ni na ษ—auko lufaya muje aikin ladan tare amma wannan yaro da farantin goshinsa kaman na uwar sa tunda shina dai kaman hariran matar ubansu tana hure masu kunne tunda ita bata haifa ba ita ta mallake ku duka da kai da uwarsu da su ษ—in dan kar kuyi albarka, yaron nan ya ja akwalan motar sa ya tafi ya barni tsaye riqe da lufaya kaman mata mai takaba yo Allah na tuba tun ba'a auri uwarsa ba na gama takaba na ja'irin yaro zai dawo ya same ni, du Allah miqo mun ruwa na jiqa maqoshi na duk yaro ya sani surutu maqoshi na kaman zai tsage bani ruwa na yayyafa masa".
Mama hafsatu da ke kusa da fridge miqewa tayi ai Amarya da sauri tace "haramun ni Mairo ban aike ki ษ—ibamun ruwa ba Saratu ฦดar albarka tashi kiban"
Mama Saratu tashuwa tayi ta ษ—auko ruwan ta bawa baba qarami yasa a cup ya miqawa Amarya ita kuma ta amsa ta kai baki da mugun sauri ta tufar da ruwa ta ษ—aura hannu a kai tace "amma dai Saratu Allah shiryaki shi kawai zance maki kashe ni za kiyi wannan sanyin ruwan ai kurษ“a ษ—aya sai lahira, kinga Hansatu ษ—iyata ฦดar albarka bani ruwa nasha" mama Hafsatu ta miqo mata ta amsa tasha tayi hamdala.
Kallon baba qarami tayi tace "Amadu kai da matanka ni Mairo ba abinda zance muku sai Allah ya maku albarka Allah yasa kuma yaranku su kula da ku su muku biyayya Allah sa ku gama da duniya lafiya, amma ke Hansatu ki dena mun fistara in ba haka ba kwashe maki albarka zan yi ba naje na jira ja'irin yaron naku da kuka hure wa kunne yau sai ya faษ—a mun sadakin uwar sa tunda ni zai ษ—auka birin wasan sa ya tafi ya barni kaman stinkakken silifas" qarisa maganan tayi tana miqewa, baba qarami haquri ya qara bata Mama Hafsatu da Mama Saratu duka suma haqurin suka bata, tayi gaba suka bi bayanta suka nufi hanyan waje dukansu.
Amjad bayan zuciyansa dake stinke wa yanzu kuma da yaga sun shiga anguwan sai yana jin wani irin zafin wuta na bugun sa kaman yana tunkaran wajan da aka hura gunguman wuta haka yake ji, ga faษ—uwan gaba ga kuma wannan zafin da yake ji yana tunkara.
Abdoul ne ya juya ganin yanayin sa sai yace "brother lafiya kuwa?" Lafiya lau amma Please in bamu kusa iso gidan ba mu juya.
Kallonsa Abdoul ya kuma yi mu juya kuma? Ga gidan nan fa banda waษ—an can gate ษ—in da kake gani wancan na gaban shine gidan. Amjad suna qara tunkaran gidan tururin wutan da yake ji na qara daษ—uwa suna iso qofan gidan kuma kaman an kama masa maqoshi sannan ji yake kaman tsakaninshi da wutan da zafin sa ke damun sa bai wuce taku ษ—aya ba.
Qofan fitan baba qarami ya buษ—e ma Amarya ta fito shima ya fito mama Saratu ne ta fito itama Mama Hafsatu kuwa da ke staye a bakin qofan haka kawai sai taki kaman ana juya mata gidan jiri lokaci ษ—aya ya kamata ha wani kukan jarirai da take ji ya cika mata kunne, dafa qofan sashen nasu tayi ta jefo qafan ta waje. Amarya da ke zuba surutu har yanzu kaman zata ari baki sun iso tsakiyan haraban gidan kenan mai gadi ya wangale gate sakamakon horn na motorn Abdoul da yaji.
Suna shiga cikin gidan tun bai qarisa parking ba Amjad da ya sanya hannunsa a wuyan sa sanadin jin shaqan da aka masa yayi yawa kuma kaman an jefa sa acikin wutan wani wawan qara ya saka wanda ya kusa da Abdoul sakin staring motorn, yana sakin qaran hannun sa a wuyan sa sai ya faษ—o jikin Abdoul a matacce ba numfashi Ba shiri Abdoul yayi parking.
Wannan qaran ya razana duk wani halitta dake cikin gidan, Amarya da Mama Saratu san da suka kusa sakin fistari a staye duk suka rikice, baba qarami nufan Motorn yayi sai kuma suka kuma jin wani qaran a bayan su da kuma sautin faษ—uwan mutun, waye za kuma su gani? Mama Hafsatu ce yashe a qasa. Amarya zama tayi dirsham a qasa gaba ษ—aya ta rikice Mama Saratu kuwa ba'a magana, baba qarami qara juyawa yayi sai ya kuma jin....
Jirgin su Abba yayi landing a tafawa ษ“alewa airport dake garin Bauchi, Abba waya ya ษ—aga yayi qira shiru ba'a ษ—auka ba, ganin haka sai ya tare taxi ya juya dan mawa su Ummey magana suzo su shiga sai kawai yaga Umma ta yanke jiki ta faษ—i.....
TIRQASHI TASHIN HANKALIN DA BA'A SAKA MASA RANA KENAN!
CAKWAKIYA, SARQAQIYA GAMI DA ฦŠAUREWAR KAI.
WAI ME KUKE TUNANI?
ME KE FARUWA?
DUK ME YA JAWO WANNAN TASHIN HANKALIN?
ME YAKE FARUWA DA AMJAD?
MENENE YA SAMU MAMA HAFSATU LOKACI ฦŠAYA?
ME KUMA KE FARUWA DA UMMA?
DUK MENENE HAฦŠIN WANNAN TASHIN HANKALI DA YA SAME SU LOKACI ฦŠAYA?
INA LABARIN UMMAN AMJAD?
INA LABARIN GIMBIYA DA MAGANAN AUREN SU DA AMJAD?
ANYA WANNAN NE DALILIN FAฦŠUWAN GABAN DA KE DAMUN AMJAD?
IN BA WANNAN BA ME ZAI FARU GABA KENAN DALILIN FAฦŠUWAN GABAN SA?
ANYA MA KUWA AMJAD NA DA RAI?
TAMBAYOYI BARKATAI DAI
SANNAN ANAN NA KAWO QARSHEN FREE PAGE'S DOMIN SAMUN AMSOSHIN WANNAN TAMBAYOYI DA SUKE RANMU DA KUMA KUNCEWAR WAฦŠANNAN RIKITATTUN AL'AMARIN KUYI HANZARI KU BIYA NAIRA โ‚ฆ300 KACAL DAN ACI GABA DA LABARI DA KU.
NORMAL PAYMENT GA WAฦŠANDA KE GROUP ALREADY โ‚ฆ300
GA WAฦŠANDA BASA GROUP โ‚ฆ400
GA MASU BUQATAN COMPLETE PAGE'S โ‚ฆ500
V.I.P COMPLETE DOCUMENT โ‚ฆ500 ONLY
TA WANNAN ACCOUNT
๐Ÿ‘‡
2220553988
HARIRA SALIHU ISAH
UBA BANK ๐Ÿฆ
KO KATIN WAYA TA WANNAN LAYIN
09161720046 MTN
07015870735 AIRTEL
SANNAN ZAKU TURO SHEDAR BIYA TA WANNAN LAYI A WHATSAPP 09161720046


Ina mai qara baku haquri waษ—anda tun farkon littafi suka biya sannan ina da babban garaษ“asa gareku a next book namu da kuma baku zaษ“i akan labarin da kuke so mu fara.
ฦณan uwa abokan arziqi masu daraja gaisuwa gare ku Ako da yaushe kuma ako ina kuke a faษ—in duniyan nan daga taku har kullum mai nishaษ—antar daku HARIRA SALIHU ISAH (UWAR BATOORL)
MARUBUCIYAR ๐Ÿฅ€ ๐Œ๐€๐…๐€๐‘๐Š๐ˆ ๐๐€๐‡ ๐Ÿฅ€


YANZU KUMA ๐Ÿ‘‘ ๐˜๐€๐‘ ๐’๐€๐‘๐Š๐ˆ ๐‚๐„ ๐Ÿ‘‘
Sannan da labarai daษ—aษ—a da na tanadar domin ku da nishaษ—in ku.


Kar ku manta sunan labarin da muke ciki ๐Ÿ‘‘ฦณAR SARKI CE ๐Ÿ‘‘ DAGA DAUSAYIN ALQALAMIN UWAR BATOORL ๐Ÿ”ฅ




๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹ ุงู…ู‰ ุจุชูˆู„ุฉ๐Ÿ’‹




๐˜ฟ๐™ค๐™ข๐™ž๐™ฃ ๐™ฉ๐™–๐™ก๐™ก๐™–๐™ฉ๐™– ๐™๐™–๐™Ÿ๐™–๐™ง๐™ ๐™ช, ๐™ ๐™ช ๐™ฉ๐™ช๐™ฃ๐™ฉ๐™ช๐™—๐™š๐™ฃ๐™ž ๐™– ๐™ฌ๐™–๐™ฃ๐™ฃ๐™–๐™ฃ ๐™ก๐™–๐™ฎuka:-
09161720046
๐˜พ๐™๐™–๐™ฉ ๐™ค๐™ฃ๐™ก๐™ฎ.
07015870735
๐™”๐™ค๐™ช ๐™˜๐™–๐™ฃ ๐™˜๐™–๐™ก๐™ก ๐™™๐™ž๐™จ ๐™ค๐™ฃ๐™š, ๐™ญ๐™–๐™ข๐™ช ๐™ข๐™–๐™ ๐™ช ๐™ฉ๐™–๐™ก๐™ก๐™–๐™ฃ๐™ ๐™ช ๐™– ๐™ง๐™–๐™๐™ช๐™จ๐™– ๐™ข๐™–๐™ž ๐™จ๐™–๐™ช๐™ฆ๐™ž, wai hausawa sukace sai an gwada akan san na qwarai. Ni Hareeyh ina maraba da ku masoya, har da alakoron talla inayi๐Ÿ˜

NOTED : karku nemeni a wannan layi 08146292652 domin yanzu baya aiki both whatsapp and call.


# ๐˜พ๐™ค๐™ข๐™ข๐™š๐™ฃ๐™ฉ
# ๐™‡๐™ž๐™ ๐™š &
# ๐™จ๐™๐™–๐™ง๐™š
ALHAMDULILLAHI ALA KULLI HALIN
Anan na kawo qarshen BOOK 1 Wand yake a FREE BOOK
Masu buqatan ci-gaba BOOK 2 ๐Ÿ‘‘'YAR SARKI CE๐Ÿ‘‘
Sai subi process da nayi magana ko su mun magana via WhatsApp number na
09161720046


Masu comments wasu bana samun yin reply afuwan abubuwan sai a hankali
Fatan alkairi a gare ku daga uwar batoorl taku


Sai mun haษ—u da ku a book 2 fan's

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login