Showing 72001 words to 75000 words out of 98220 words

washegari da sassafe ya tashi, bayan an kawo masa abun kari a gidan wannan mutumin karyawa yayi ya gode yace ze wuce
Rakasa wannan bawan Allah yayi suka yi sallama yana qara masa godiya sosai
Gaba ษ—aya sai kuma ya rasa ta ina zai fara neman wannan bishiyan
Tambaya zeyi ne ko yaya? a haka dai ya samu wani bawan Allah yayi tambaya jejiin garinnan babba
kowa ce masa yake kawai ya shiga jejin dan ba nan kusa bane
Ya shiga jeji-jeji sosai sunfi a qirga dan kwanansa ษ—ai-ษ—ai har 5 amma bai samu itacen nan ba.




Mahreen gaba ษ—aya ita da ya Abdoul sun zama layla da majnoon qarfi da yaji
Yayinda Maha da soja abun nasu de sai du'aee kullum kaman wuta da auduga haka suke
Yau Abba zai dawo bayan kwana biyar da aka qara masu a aikin nasu
Me aiki ta gyara gidan tsaff sa qamshi kawai ke tashi, kitchen kuma tare da su Mahreen da Maha aka yi komi
Bayan sun gama sun kammala komi kowa ya wuce dan ya shirya
Sunyi wanka duka Maha tawa little ma wanka duk sun shirya kowa yayi kyau
Umma tayi ado cikin dogon rigan swissless blue black tasha sarqanta da kunnenta na gold karkuso kuga kyawun Umma kaman wata Amarya, sai ka ranste bata haifi soja da Ameera ba
Futowa falo tayi ta zauna sai qamshi take
Maha ce ta fito ษ—akinsu tana isowa palorn tace "Rassss Ummata kyau haka ai sai kisanya Abba kasa haquri ya huta"
Umma amma kinsan me saura abu 1 makeup kizo muje namiki Allah zaki ganki Amarya sak kawai
Murmusawa tayi ta mata danqwalo, Yau kuma nice abokiyar wasan taki doter?
Umma bafa haka nake nufi ba
Suna cikin hiransu basu ko ki dirin motorn Abba ba sai sallaman sa tare da Soja da little
Ayoyo Abbana da gudu Maha ta rungumesa
Doter an girma ba'asan an girma ba zaki karya Abban naki ai
Dariya tasa Abba inna karyaka dole a aikani aikin soja na karya soja
Shafa kanta yayi Allah maki albarka uwata.
Umma kuma zuba masu ido tayi kawai sai murmushi take
Abbane da suka haษ—a ido ya kashe mata ido guda 1 kauda kai Umma tayi tana dariya qasa-qasa
Haurawa sama Abba yayi ya nufi ษ—auki ganin haka sai Umma ta tashi tabi bayan sa
"Su Umma miji" inji Maha tana dariya
Buge mata baki Mahreen tayi wai ke iyayenki ma abokanan wasanki ne ba wanda kika bari
Abba na isa ษ—akin yana juyawa kallon qofa sai sallaman Umma, Buษ—e hanu yayi da sauri Umma ta faษ—a jikinsa suka rungume juna
Hajiyata kinyi kyau na sayi wankan nan tabbas irin wannan haษ—ewa haka ina ma zan iya kallon kowa
Murmushi tayi shikkenan yallayboi wanka ta biya kuษ—in sabulu
Umma taya Abba tayi yayi wanka
Ya shirya suka fito suka yi qasa dan yaci abinci
Abba ne yace "nifa a qasa zan zauna"
Abincin suka kawo qasan da komi duk zaama suka yi Umma tayi saving mijinta
Sunacin abinci suna fira


Kwarewa Maha tayi, da sauri kankowa ya motsa Soja ya miqa mata ruwa dan yafi kusa da kofin ruwan
Amsa tayi tasha kamun taji normal sannu kowa kece mata
Bayan sun kammala cin abincin
Abba ya kalli Soja wai son yaushe ne zaku Cairo en ne ko turkey kace?
Sosa kai yayi Abba nifa ba lalllai naje ba gaskiya
Ko meyasa son?
Abba kawai banson nisa da gida ne gaskiya
Shikenan fyne Allah temaka.
Tashuwa Abba yayi to kuyi hira lafiya ba naje na kwanta na huta gudnyt koh yaran kirki
Bayansa Umma tabi ta tayasa rage kayan jikinsa
Kwantawa Abba yayi, Umma zaunawa tayi a gefen gadon
Kallonta yayi lafiya tawan ba kwanciya zamu yi ba ko dai akwai wani abun ne?
Bakomi yallaษ“oi
Uhmn yauwa nace ka amshi numbern ne?
A'a ban amsa ba kin san sai a hankali sungulloli sun man yawa
To Allah ya temaka my yallaษ“oi
Yanxu ki qira mijin Ameeran ya turo bacci nakeji
Tom yallaษ“oi ษ—aukan wayan tayi ta fice a ษ—akin duka
Qiran Daddyn little tayi suka gaisa shima ta balbalesa kamun suka shirya tace ya turo mata layin yaronta, Haquri ya bata a take ya tura mata layin.
Ganin layin ba qaramin farin ciki tayi ba shiga kan layin tayi tai...............


Muje zuwa fan's โœ๏ธ


ฦณAR SARKI CE daga dausayin Alqalamin uwar batoorl
Justice Hareeyh๐Ÿ•Š๏ธ



๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹ ุงู…ู‰ ุจุชูˆู„ุฉ๐Ÿ’‹


๐˜ฟ๐™ค๐™ข๐™ž๐™ฃ ๐™ฉ๐™–๐™ก๐™ก๐™–๐™ฉ๐™– ๐™๐™–๐™Ÿ๐™–๐™ง๐™ ๐™ช, ๐™ ๐™ช ๐™ฉ๐™ช๐™ฃ๐™ฉ๐™ช๐™—๐™š๐™ฃ๐™ž ๐™– ๐™ฌ๐™–๐™ฃ๐™ฃ๐™–๐™ฃ ๐™ก๐™–๐™ฎuka:-
08146292652
๐˜พ๐™๐™–๐™ฉ ๐™ค๐™ฃ๐™ก๐™ฎ.
09161720046
๐™”๐™ค๐™ช ๐™˜๐™–๐™ฃ ๐™˜๐™–๐™ก๐™ก ๐™™๐™ž๐™จ ๐™ค๐™ฃ๐™š, ๐™ญ๐™–๐™ข๐™ช ๐™ข๐™–๐™ ๐™ช ๐™ฉ๐™–๐™ก๐™ก๐™–๐™ฃ๐™ ๐™ช ๐™– ๐™ง๐™–๐™๐™ช๐™จ๐™– ๐™ข๐™–๐™ž ๐™จ๐™–๐™ช๐™ฆ๐™ž, wai hausawa sukace sai an gwada akan san na qwarai. Ni Hareeyh ina maraba da ku masoya, har da alakoron talla inayi๐Ÿ˜!!!


# ๐˜พ๐™ค๐™ข๐™ข๐™š๐™ฃ๐™ฉ
# ๐™‡๐™ž๐™ ๐™š &
# ๐™จ๐™๐™–๐™ง๐™š




๐Ÿ’ฆ๐Ÿ’ฆ๐Ÿ’ฆ๐Ÿ’ฆ๐Ÿ’ฆ๐Ÿ’ฆ๐Ÿ’ฆ


๐™”๐˜ผ๐™ ๐™Ž๐˜ผ๐™๐™†๐™„ ๐˜พ๐™€๐™€


๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐˜ผ๐™ฃ๐™™ ๐™’๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ฉ๐™š๐™ฃ

๐˜ฝ๐™ฎ


๐™ƒ๐™–๐™ง๐™ž๐™ง๐™– ๐™จ๐™–๐™ก๐™ž๐™๐™ช ๐™ž๐™จ๐™–


(๐™๐™ฌ๐™–๐™ง batoorl)

ุงู„ู„ู‡ู… ุตู„ู‰ ูˆ ุณู„ู… ุนู„ู‰ ุณูŠุฏ ู†ุง ุฑุณูˆู„ู„ู‡ saw๐Ÿ–ค๐Ÿค


_______________________________________________________________


๐˜ฟ๐™ช๐™  ๐™ฌ๐™–๐™ฃ๐™™๐™– ๐™ฉ๐™–/๐™ฎ๐™– ๐™จ๐™–๐™ช๐™ฎ๐™–๐™ข๐™ช๐™ฃ ๐™ก๐™–๐™—๐™–๐™ง๐™ž ๐™—๐™–๐™ฃ๐™ฎ๐™–๐™›๐™š ๐™—๐™–
๐˜ฟ๐™ช๐™  ๐™ ๐™ช๐™จ๐™ ๐™ช๐™ง๐™š๐™ฃ ๐™™๐™– ๐™ข๐™ช๐™ ๐™–๐™ž A๐™ก๐™ก๐™–๐™ ๐™ ๐™– ๐™ฎ๐™–๐™›๐™š๐™ข๐™ช A๐™ก๐™ก๐™–๐™ ๐™ ๐™– ๐™—๐™–๐™ข๐™ช ๐™ž๐™ ๐™ค๐™ฃ ๐™–๐™ข๐™›๐™–๐™ฃ๐™ช๐™ฌ๐™– ๐™™๐™– ๐™ฌ๐™–๐™ฃ๐™ฃ๐™–๐™ฃ ๐™ก๐™–๐™—๐™–๐™ง๐™ž
๐™’๐™–๐™Ÿ๐™–๐™ฃ ๐™ ๐™ช๐™จ๐™ ๐™ช๐™ง๐™š A๐™ก๐™ก๐™–๐™ ๐™ ๐™– ๐™ฎ๐™–๐™›๐™š ๐™ข๐™–๐™ฃ๐™– ๐™—๐™ž๐™Ÿ๐™–๐™๐™ž R๐™–๐™จ๐™ช๐™ก๐™ช๐™ก๐™ก๐™–๐™๐™ž SAW โค๏ธ




๐Ÿ…ฟ๏ธ 53&54



๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹ ุงู…ู‰ ุจุชูˆู„ุฉ๐Ÿ’‹












Abdoul ne zaune a ษ—aya daga kujerun dake palourn kakar tasu, kujera me zaman mutum ษ—aya 1 yana danna wayan sa. Hayrace tazo tawuce sa tana "Babban yaya sannu da zama halan yau kazo gadin kakus ne?"
Ke dai bari kawai boษ—ษ—i Kakus hukuma ce sai da rarrashi, tace "tom nide nayi kitchen yaya kamun ta fito ta balbaleni ban gama girki ba rana tayi
Dariya yayi yace "keda kakus kam sai Allah kullum faษ—a amma bata iya kwana bata ganki ba wataqil in mun aurar dake tare mijin ze aureku" Caraf sai a kunnen Amarya wacce ke fitowa yanzu daga ษ—aki tace "Yo inba sinqin shishishigi shigilitu da sa ido irin naka ba ina ruwan ka tsakanina da baiwar Allah, Allah ne ya haษ—a jininmu atou kuma qarshe ko mutuwa tare zai ษ—auke mu bare miji da daman wannan dolen sa ne in dai ba'a tangaษ—e aka haife sa ba ba mai raba mu" wucewa kitchen Hayrat tayi ba tace qala ba sanin halin kakar tata, ai kuwa dai bata stira ba dan kakus bin bayanta tayi da harara tace "kinanan a wajan kaman tangaษ—aษ—ษ—en budurwan kaza, ai da karma kije kiyi girkin yo ai ni dole ma na biki gidan miji kar kije kimana abun kunya tunda de baza kiyi abuba sai ance kiyi dan tsabar layiii" da ta gama ษ“aษ“atun zama tayi a kujera me ษ—aukan mutum 2 tana bismillahi ni jikan mutum 4, Abdoul ne ya kalleta sannu da fitowa uwargida ta bayan ke babu wata sai dai amarya ya qarisa yana dariya
Da har ta washe baki sai kuma ta stuke bakin kallonsa tayi tace "Yau ษ—an nan har yaudaran yakai haka a gabana kake faษ—an sai de amarya? Tom jeka na yafe maka ka kawo badon halinka ba ษ—an kwal uba"
Murmushi yayi shiyasa nake yinki amarya uwargida, gaisheta yayi ta amsa tana tambayansa ya aiki ya kishiyanta?
Murmushi yayi ai maganan kishiyan naki ma shi ya kawoni Hajiya Kakus tamuุŒ Yauwa dai ango ai ni nafison haka kuyi aure tun da raina inga yaranku Allah raya ku ya baku zuri'a mai albarka, nifa so nake kan na mutu naga har da tattaษ“a kunne na kaga ฦดar albarka takwarata matar auwalu har cikin na biyu gare ta kaga da yardan Allah in ta haifi mace kan na mutu zan aurar da yarinyan, Murmushi Abdoul yayi yana jin shirmen kakan tasu bai ce komi ba shi dai .
Yauwa to wacece kishiyar tawa ma tukunna insan wacece ta shirya kishi da mairama daso, Murmushi yayi yace "wata baiwar Allah ce nutsaststiya kyakkyawa ga hankali ga ilimi ga tarbiya ga asali ga ga ga........."
Me amarya zata yi in ba dariya ba Abdu lafiyan ka ko dai duk ta tangaษ—ar da kai ne ta zautar mun da ango tun yanzu ta mallakemun kai, murmushi yayi haba de ai ni dake mutu ka raba, Tom irin wannan lissafowan haka ko kunya na baka ji ba yo ma ai ka rage dan ganin idona kar nayi kishi nace a'a ko, Murmushi yayi ai kema kinsan kin fita komi amarya uwargida kuma duk a wajanki ta gado su, washe baki tayi Allah maku albarka jikokina Allah sanya alkhaeri, da Ameen ya amsa yace "Kakus ba kowa bace face...
Maganan hayra ne ya tsaida shi tace "ya Abdoul yi sauri ka faษ—a na matsu naji wacece akewa yabo ba kunyan kakus Allah yasa dai wacce nake tsammani ne"
Danqwalan ta kakus tayi to ฦดar kwal uba haษ—asu kasa rabasu bazaki shiga tsakanin mu ba kuma baza'a faษ—a ba tafi ki bamu waje gulmammiya kawai, taษ“e baki hayra tayi tace "in tayi tsami za muji" ta wuce abinta
Yace yauwa kakus AISHA ce fa MAHREEN
Guษ—a Kakus tayi tare da kabbara tace "ALHAMDULILLAHI Allah nagode maka ni mairo, amma naji daษ—in wannan batu Allah maku albarka Abdu, a Yauwa kaga ina ma wayana ne laluษ“osa tayi ta miqa wa Abdoul tace "gashi dannamin layin ita uwar tasu tunda ta balaga ta balage garin su ba abinda ake koya masu sai tangaษ—i bata neman albarkan uwarta to ni uwarta zan nemi albarkanta ฦดar jakar uba kawai"
Qiramun ita in bazata zo ba ni zan iya zuwa har qasan masu layiin inba ma tsabar tangaษ—e wa ba asawa gari sunan mutum wai fa sunan uwata sunan garin nasu tom dai bazai hanani qira ba, qasan kulu masu tangaษ—aษ—ษ—iyar hali suna koyawa yaran mutane fitsara da rena iyayensu wannan baqin halin har ina ni Mairo ษ—an nan qiramun ita da wuri
Karษ“a yayi haba kakus surka tace fa kibar zaginta nikam
Au ashe surkar ka ce? tom ban sani ba hanani faษ—an abunda nayi niyan faษ—a dan kwal ubanka jai'ri kawai ina ruwanka ni da ษ—iyata inma me nace wani ya haifarman ita ba dai nice na haifi abata, shekara nawa ban sata ido ba ba dole abun ya dameni ba tunda zuciyata ni ba irin na ฦดan kasar su bane, ita fa kaษ—ai gareni ษ—iya mace, tom don haka karka shiga tsakanina da ฦดata yar albarka
Murmushi yayi dama abunda ya sashi saka baki kenan ta dena mita gashi hartasawa ummeyhn tasu albarka
Numbern Ummeyh ya dubo ya qira, yana shiga aka kashe aka qira.
Miqawa kakus wayan yayi Kinga ma ta kashe ta qiraki gashi kuyi magana to
Yanzu dan tsabar ka renani baka ganin girma na ni uwar ubanka shine bazaka ษ—aukan mun qiran ba na ษ—auka da kaina dan jakar uwaka bazan ษ—auka ba to
ฦŠauka yayi da sauri gudun kar qiran ya yanke "Assalamu Alaiki gwaggo"
Amsawa tayi ah ah yaron gwaggo sai yau ake jinku kenan nasan yau ma albarkacin uwata aka qiran ko?
Sunkuyar da kai yayi yana sosa qeya ayi haquri Ummeyh abubuwan ne sai a hankali, Ummeyh taace "Bakomi yaron Gwaggo" gaisawa suka yi yace mata "ga kakus" ya miqawa amarya wayan
Amsa wayan Amarya tayi bayan ta karkata ษ—aurin kwalinta
Sallama Ummeyh tayi kakus tace "bazan amsaba dan gidanku wato de Jamila kin girmi neman albarkan uwaki sede ni na nemoki bazaki iya zuwa ki ganni ba bare gaisuwa kema kinbisu kun taru kun tangaษ—e kunzama tangaษ—aษ—ษ—u masu layi to yayi kyau ni Mairo bazan maki baki b Allah shiryaki y maki albarka, amma nasan wannan balaraben mijin naki baze hanaki zuwa ba dan hankali garesa ga sanin girman iyaye tunda dai yaron nan habu har yamun takwara, Ammade Allah ya shirya mun ku wallahi.
Ummeyh najin ta bata ce komi ba har ta gama magana sanin halin mahaifiyar tata "Kiyi haquri Gwaggo Insha Allahu bazan wuce kwana 2 ba zaki ganni" Ummeyh ta faษ—a cikin ladabi
Yauwa dai yar albarka ko kefa ni shiyasa nake sa maki albarka kullum ko baki nema ba dan kinfi sauran jin maganata Allah de ya maki albarka ya rabaki da tangaษ—ewa har abada
Ta amsa da Ameen suka yi dan hira sama-sama can suka yi sallama kashe wayan tayi ta aje, qwalawa hayra qira tayi "Harirtu qawar kakus kawo man ruwa nasha ฦดar albarka bakina sai zikiri yake duk sun bi sun sani surutu kaman kanari"
Hayran ta shigo da sallama ta miqo mata ruwan ta karษ“a tasha, Abdoul ne ya murmusa yace "yanzufa kika koreta gashi da kanki kin qirata" hararan sa kawai Amarya tayi bata ce masa komi ba. Abinci hayra ta shirya masu suka wuce dinnig kowa ta zuba masa, cin abincin suke bame cewa komi
Sede kakus da bakinta baya shiru kana ganin bakin kasan akwai abunda yake son cewa..




Bayan ya turo mata layin ษ—auka tayi ta qira amma sede be shiga ba ta gwada yakai sau uku 3 amma baya shiga akashe take ji, hankalinta ne ya tashi sosai dan haka kawai take jin kaman ba lafiya ba, dafe kai tayi tana ambaton sunan Allah "Ubangiji yasa ba wani abun ta sameka ba yarona" sai kuma tunanin ษ—an ta yafaษ—o mata rai nan take hawaye ya cika idonta jin kaman mostin mutum ya sanya ta saurin sharewa ta seta kanta, Mahreen ce ta shigo palourn zuwa wajanta tayi da sauri tana cewa "Ummanmu lafiya? Mai ya faru?"
Murmushi tayi bayan ta ษ—ago kai tace "lafiya lau doter kawai na qira wani layine auntynku Ameera suka turomun sai de bai shiga ba" Mahreen tace "to amma Umma tagumi ba kyau ki dena kinji Insha Allah lafiya lau layin kuma zai shifa kibari anjuma ko gobe ki gwada inyaso in bai shigaba sai ki qirasu ki faษ—a masu ko zasu qira maki layin ko Umma"
Shikkenan doter ina Auntan Ummeyh fa? Tana can ษ—aki da waya banmasan me take ba, Umma tace "to je ki qiramun ita" tashuwa Mahreen tayi tana to Ummanmu
Wucewa Mahreen tayi ษ—aki dan qiran Maha, Umma Qiran aminiyar ta ne ya shigo wayanta ta ษ—auka suna gaisawa da alama magana me muhimmanci suke yi.
Mahreen bayan ta shiga ษ—akin ta samu Maha akwance tana danna waya, fisge wayan tayi tace "wai me kikeyi ne awaya kam maha?" Turo baki Maha tayi tace "ni don Allah ki bani kar ki batar dani inda nake abu ya ษ—auko daษ—i" Kallon fuskan wayan tayi ta kalli Maha mene wannan kuma? littafi ne? Maha tace "eh novel ne wallahi Adda kuma me shegen daษ—i"
Kallonta tayi tace "ooh kekam da novel bansan waya koya maki karantawan ba ma ni Indo"
Allah kema Adda Mahreen in kin fara karanta littafinnan ba zakiso ki tsayaba ga abun tausayi ga darasi aciki ga daษ—i kuma ayya barin ma maisunana ta cikin ษ—ayan littafin abun tausayi bakiga Yacce mamanta take treating nata ba, Kallon Maha tayi tace "to yanzu dai faษ—amun sunan littafin dai ko"
Guda biyu 2 ne aka turomun masu shegen daษ—i kekam ma ba'a gama labarin ba tukun ษ—ayan dai sunansa JAHILCI KO AL'ADA ษ—ayan kuma something maita ne ko me na mance amma Adda kinji daษ—in littafin nan kuwa wallahi ya burgeni, murmushi Mahreen tayi ai kuwa zan karanta nima ba na samu zama


( KUMA FAN'S KARKU SAKE A BAKU LABARI DOMIN KUWA DA ฦŠUMIN SA YAZO
JAHILCI KO AL'ADA?
VERY SOON ZA'A SAKE MAKU SHI
๐™Š๐™ช๐™ง๐™ข๐™ข๐™–๐™๐™ฃ ๐™—๐™–๐™ฉ๐™ค๐™ค๐™ก๐™š๐™ง๐™๐Ÿ”ฅ ๐™›๐™ค๐™ง ๐™ก๐™ž๐™›๐™š )


Tom yanzu tashi muje Umma ce tace na qiraki, tare suka fice a ษ—akin sukai palourn wajan Umma..

Kakus ce a hakimce a kujera baba qarami na zaune a qasa, gaisheta yayi ta amsa fuska a sake "Allah maku albarka yaran nan kuma Allah sa yaran ku su maku biyayya su kula daku fin yacce kuke mun nide aihuwa tamun rana Alhmdlh sai kuma ta ja gefen ษ—an kwalinta tana fece hanci ga hawaye "Allah sarki malam ina kake dai kaga yacce yaranmu suka zama da jikoki, qara fece hanci tayi Allah maka rahama Allah sa ka huta". Da Ameen baba qarami ya amsa
Share hawayen tayi tace "Yauwa dama akwai maganan da nake so muyi dakai amma ya kamata sai yayanku ya shigo In da son samune da qanwarku amma tunda nasan halinta itakam ta fistare qafanta tangaษ—aษ—ษ—iyar garinsu sun koya masu rashin neman albarkan iyaye to taje can ta qarata ku kuma tunda kuna storon ta tafi qarfinku to sai kuci gaba dayi karku daina manyan wofi, nasan ba lallai mu ganta ba dan haka dakai da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login