Showing 108001 words to 111000 words out of 231786 words
Chapter 37 - KARFEN KAFA Book 1 COMPLETE (By Rufaida Umar).txt
da ya soma tsirfowa saman goshinsa. Miƙewa ya yi kamar wanda aka mintsila ya dauki jakarsa. A ruɗe Hisham ya miƙe tsaye ya riƙe mishi kafaɗa ya fisge har hannunsa na bugun wani ƙarfen motsa jiki, koda da zafi, bai ji ba. Yatsa ya shiga nunawa Hisham. Ya soma magana da muryar da ta ɗauki hankulan jama'ar wurin.
"Kar ka ƙara! Wannan ne gargaɗi na ƙarshe da zan maka! Bana so! Har abada banda kowa a duniyata sai Hajiya Zeenatu! She meant everything to me! Ita kadai ce dangina. Ka rike wannan ka ji?"
Ya ƙarashe a sanyaye, abin mamaki hawaye ya shiga fitarwa, a hankali ya juya ya soma taku ya bar Hisham tsaye a wurin baki a bude. Ga mamakin Hisham da mutanen wurin, faduwa ya yi. A guje suka yi kansa, Hisham ya tallafoshi, idanunsa a rufe sai numfashi yake fitarwa sama-sama
"Hussein, me ya yi zafi haka? Ka yi hakuri don Allah."
"Maida ni gida." Abinda ya iya fada kenan cike da wata iriyar kasala. Jama'ar na ta yi mishi sannu, wani ya riƙe jakar yayinda Hisham ya saƙalo hannun Hussein a wuyansa suka nufi motar Hussein din. Sai da ya zaunar da shi kafin ya koma da sauri shima ya dauko tarkacensa ya zuwa a aljihu suka bar wurin. Yau ne zuwansa gidan Hussein karo na farko, dakyar yake mishi kwatance wannan karon muryarsa ta bude ba kamar ɗazun ba kamar yanda idanunsa suka bude sosai. A gaggauce Maigadin ya bude ƙyaure ganin motar maigidan, Hisham ya tura hancin motar ya faka.
Hajiya Zeenatu na zaune a falo tana amsa waya ta ji sallamar da ba muryar mijinta ba. Turus ya yi kamar yanda itama ta yi tsaye tana dubansu.
Ganin yanayin Hussein ya sa ta ƙarasawa da sauri.
"Habeebee meke samunka? Kai kuma waye?"
Hussein ya zauna ya amsa.
"Hisham ne."
Ta dubi yanayin Hussein din sannan ta dubi Hisham wanda ke gaidata. Ta amsa fuska na yabo ba fallasa ganin irin duban mamakin da ke saman fuskarsa. Ya riga ya gane matsayinta wurin Amininsa don tun shigowarsu idonsa ya kai ga makekan enlargement din da ke dauke da fuskokinsu. Daga irin rikon da ta yiwa Hussein kadai ya ci ace duk mai hankali ya gane alaƙarsu.
'Taɓ!' Abinda ya ce kenan a ƙasan ransa. A ƙarshe ya daure ya ɓoye mamakinsa ya saki fuska. Zai ba ta bayanin abinda ya faru ne ya ji Hussein ya tareshi cikin rawar murya.
"Amm..dama kaina ne ke ciwo da jiri, ganin ba zan iya tuƙi ba yasa nace ya kawoni. Kiyi hakuri idan ganinsa ya ɓatamaki rai."
Sai lokacin ta wayance gami da sakin fuska
"Haba kai kuwa, mene abin ɓacin rai don abokinka ya kawoka? Wani zubin kamar yaron goye idan ka fadi wani zancen. Sannu, zauna mana bari na kawomaka ruwa."
Hisham ya girgiza kai yana dariyar yaƙe.
"A'a ba komai tafiya zan yi, nima yawa Amaryar na jirana."
Suka yi dariya, ya yi mata sallama sannan ya fice cike da tsantsar mamakin wacce ya gani matsayin matar abokinsa.
"Akwai wata a ƙasa." Abinda ya ce kenan bayan fitarsa daga gidan. Jikinsa ya ba shi akwai wata a ƙasa.
Har ya koma wurin Gym ya dauki motarsa ya yi gida, bai bar tunanin lamarin Hussein da matarsa ba. Da ma duk abinda ya faru tsakaninsu.
***
"Wai mene ne?"
A'isha ke tambayar Hisham cike da damuwa ganin yanda yake mata Safa da marwa a tsakar falon, idan kuma an ɗan jima ya ce "Taɓ!"
Ya dubeta sai ya kama hannunta suka zauna.
"Ba komai Princess, kar ki damu. Amm..please kiramin Antinmu a waya ki ban."
Cikin rashin fahimta ta ce.
"Wacce a ciki?"
"Ramlat."
Nan da nan tunanin A'isha ya tafi wani bigiren, murmushi ta yi don gani take fatanta ne zai tabbata tsakanin abokin mijinnata da Yayarta. Ta mike ta nufi ɗakinta ta dauko wayar kai tsaye ta dannawa Ramlat kira.
Bayan ta ɗaga sun gaisa ta sanarmata saƙon Hisham sannan ta miƙa masa.
"Ranki ya dade Antinmu."
Daga daya bangaren Ramlat ta ɗan yi murmushi mai sauti.
"Angon ƙanwata fatan kuna lafiya?"
"Lafiyarmu kalau, don Allah alfarma nake nema a wurinki."
"Toh wace iri?"
"Ina son idan kin samu lokaci ki zo gidana ko kuma na sameki wurin aiki wata ƴar magana zamu yi mai muhimmanci."
Shiru ya ɗan biyo baya, ba wanda ya ce uffan tsakaninsu. Ga Hisham, dama ya bata ta nutsu ta bashi amsa, ga Ramlat kuwa jinin jikinta ta sha da kuma fargabar dalilin Hisham na nemanta. Can dai ta nisa.
"Shikenan, gobe In sha Allah daga wurin aiki zan biyo."
"Yauwa Antinmu, Nagode sosai. A gaidamin ƴaƴana."
Daga nan ya miƙa wa A'isha kan wayar ya shige daki cike da damuwar abokinsa.
"Auta, lafiya dai ko? Ba wani laifin kika yi ba?"
Dariya A'isha ta yi jin tambayar da Ramlat ta watsomata ta cikin wayar.
"Wallahi lafiya sumul, bansan menene ba amma ina fatan alheri ne."
Ajiyar zuciya mai karfi Ramlat ta sauke.
"Shikenan Auta, sai Allah Ya kaimu goben."
Daga nan suka ajiye wayar.
***
Ramlat ta kasa sukuni tun bayan wayar, har ta kasa hakuri sai da ta faɗawa Hajiya. Shiru Hajiya ta yi na ƴan daƙiƙa kafin ta ce.
"Toh ko wani laifin Auta ta yi ne yake ɓoyewa?"
Girgiza kai Ramlat ta yi.
"Na tambayeta ta tabbatarmin lafiya kalau. Ko mene dai idan naje goben in sha Allah zan ji."
"Ya za ki yi da kiran da Dakta ke miki?"
Gabanta ya fadi, ɗazun da yamma a hanyarta ta dawowa daga wurin aiki ne ta amsa wayar Baba Dakta akan yana nemanta a gidansa. Tun sadda ta ji hakan ta rasa sukuni, tasan tatsuniyar gizo bai wuce na ƙoƙi.
"Kin yi shiru." Hajiya ta furta tana kallon yanda ta ke dama fura cikin nono ba tare da ta san me take ba don inda ludayin ya ke kallo daban da abinda ta ke.
Maganar Hajiyar ya maidota cikin nutsuwarta. Sauke ajiyar zuciya ta yi.
"Nasan ba wani jimawa zan yi a gidan A'isha ba, da zarar mun kammala zan wuce gidan Baba Dakta kafin na shigo."
Girgiza kai Hajiya ta yi tana murmushi.
"Ramlatu kenan, ba haka za'a yi ba. Ina gidannan ina gidan Baba Dakta? Ki tashi dai ki je yanzu kinga goben kin huta. Miƙomin furar na dame abata."
Ta kalli Hajiya a raunane, babu damar ta ce a'a, ta mike jiki a sanyaye ta miƙamata.
"Mami zan bi ki!"
Ummi ta furta tana ɗago kai daga zanen da take na makaranta. Daƙuwa Hajiya ta mata.
"Gidanku, wato ma ba karatun kike ba kunnenki yana nan ko? To babu inda za ki je, idan kuma kika bi ta babu ke ba shan fura."
Ai da sauri ta ce ta fasa. Murmushi kawai Ramlat ta yi ta nufi daki, hijabinta kawai ta zura ta dauki wayarta ta fito. A sannan ko sallar Isha'i ba'a yi ba, an dai kusa kira. Ta yi musu sallama ta fita.
***
Zuciyarta kamar ta yi tsalle ta fito sadda ta gama jin dogon jawabin da Baba Dakta ya ɗauko game da batun aure. Sai da ya gama nunamata muhimmancinsa ga rayuwar ƴa mace kafin ya bita da nasiha mai ratsa jiki, daga karshe ya tafi kai tsaye ga inda ya sa gaba.
"Lokaci ya yi da ya dace ke da kanki ki yiwa kanki faɗa ki fiddo mijin aure Ramlatu, na kyaleki don a ganina kina da ƴancin da za ki zaɓawa kanki abokin rayuwa wannan karon ba tare da waninmu ya tilasta maki ba. Ki tsaida hankalinki ki yi tunani mai kyau. Akwai da dama waɗanda suka zo wurina neman aurenki kamar yanda shima kawunki Bashir ya sameni da batun maneman aurenki sun sameshi. Toh koda a baya bamu ba su damar neman yardarki ba, wannan karon ba zamu hanasu ba Ramlatu. Babban burinmu shi ne mu ga kema kin yi aure. Aiki ba ya hana aure idan har mijinki ya amince, idan kuwa bai amince ba sai ki zamanki a daki ki nemi wata sana'ar kamar yanda ƴar uwarki ta yi."
Yana nufin Amrah. Wato ma dai ana zuwa har can Yakasai neman aurenta? Wannan abu ya dauremata kai, kodayake yana daga dalilinta na dauke ƙafa a gidan Hajja, a gidan ma akwai ɗan Kawunta da ke sonta sai dai mahaifiyarsa ta ce sam ba da ita ba. Wannan shine rikici ma na karshe da akai har zuwa gidan ya fice a ranta. Basu da masaniyar babu Kamalu a ƙoƙon ranta, ba ma shi kadai ba, kowane namiji ma ba ya gabanta. Aliyu ta so, kuma har gobe akwai kaunarsa a zuciyarta. Rana bai taɓa fitowa ya faɗi ba tare da ta yi mishi addu'a ba.
"Kinji ko?"
Maganar Baba Dakta ya katsemata tunani. Gyada kai ta yi tana share kwallar da ta cikamata idanu. Cikin sallamawa ta amsa.
"Eh Baba Dakta, da yardar Allah zan yi yanda ku ke so."
Murmushi ya yi gami da gyara zaman gilashinsa.
"Allah Ya yi maki albarka. Ya zaɓamaki abokin rayuwa wanda za ku rayu har abada cikin aminci, so da yarda."
Kunya ta sanya ta kasa amsawa sai murmushi.
"Sai abu na gaba, meyasa bakya tura yarannan su gaisa da dangin mahaifinsu?"
Ta ƙara russunar da kai.
"Kwanaki ma fa sun je family meeting dinsu."
"Aa, wannan ba hujja ba ce, ai inada labarin shima ba da son ranki ba wannan yarinyar ta wurin Justice ce ta zo ta tafi da su kina cika da batsewa kamar alkubus ko?"
Dariya ta yi shima ya tayata don dama ya fadi ne don ta maido walwalarta. Mamaki take yi na inda ya samu labarinnan amma ta fi zaton a bakin Amrah ne.
"Ba'a haka Ramlatu, yanda kike da iko a kansu, su ma suna da iko. Wannan karon idan aka yi hutu idan ma ba ki sanya an kai su ba, da kaina zan kwashesu na kai. Dolensu ne fa, idan kika hanasu zumunci da su, wataran da ƙafarsu zasu taka su je, lokacin ne kuma za ki sha kunya."
Har sannan murmushi take, kaunar Baba Dakta na ƙara ratsamata zuciya da gangar jiki, tana jinsa kamar Abbanta. Irin kulawa da kaunar da yake nunamusu, ko Abba yana raye abinda zai yi kenan. Daidai gwargwado yana kokari wurin kula da gidansu, abinci duk wata sai Nana Dakta ya ajiyemusu, samun mutum kuma amini irinsa abu ne mai matukar wahala a wannan ƙarnin.
Ba ita ta bar gidan ba sai da suka ci abinci ta yi sallah.
Hajiya ta ji dadin dalilin kiran Baba Dakta, ta kara da fadin.
"Ai gwara dai ya tunasar da ke, idan kuwa kin fi kaunar mu zauna muna haɗa ƙugu a gidannan sai ki yi kiga idan zai ɓullar da ke. Gwara ni na tsufa na ci ƙuruciyata yanda ya kamata."
Dariya ma maganar ta ba Ramlat, furarta da aka bar mata ta sanya a fridge, ta tashi yaran da suka sheme a ƙasa suna bacci ta kai kowannensu makwancinsa. Affan kuwa sai da ta tabbatar ta kai shi ya yi fitsari kafin ta kwantar da shi saman gadonta bayan ta kakkaɓe. Ta yi mishi addu'a sannan ta faɗa wanka.
***
WASHEGARI just published "BABI NA TALATIN DA UKU" of my story "Ƙarfen Ƙafa". https://my.w.tt/JH0s4CH5Wab
🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️
_*Rufaida Umar*_
Bismillahir Rahmaanir Raheem.
33)
Tunda ta ji kira daga sama wai kuma daga Chairman Aliyu Dikko ta ji kanta ya yi ringingin, ma'aikata dai sun fi dubu a ƙasan bawan Allahnan, ta ina har ya ganeta da har zai turo Oganta ya kirata? Sai kuma da ta tuna Oga ya nema kafin ita ne yasa ta gane bakin zaren.
Kai tsaye tare da Oga suka shiga wurin Chairman. Matar da ta gani zaune yasa ta shan jinin jikinta. Sanadin aikinta dai Hajiya Zeenatu za ta yi mata. Sai cika take tana batsewa, kallon da take watsamata tun shigarta ofis din ya sanya Ramlat daga kallo ɗaya ba ta ƙara duban inda take ba har suka karasa.
Chairman ya na juyi saman kujerarsa yake duban wacce aka kira da Ramlat duba irin na ƙurillah. Ya haɗiyi miyau maƙwat. Koda ya taɓa ganinta ya manta saboda dubunnan matan da ke zirga-zirga a Revenue.
"Yallaɓai gatanan."
Oga Ɗalhatu ya ƙara magana a karo na biyu ganin kamar Chairman ba ya tare da shi, Chairman ya yi gyaran murya kafin ya maido nutsuwarsa ya saita kansa.
"Yauwa Ɗalhatu, kana iya tafiya." Cike da girmamawa Oga Ɗalhatu ya amsa gami da barin wurin.
"Wannan ita ce?"
Chairman ya fadi gami da ɗauke kallonsa kamar ba ya so daga kan Ramlat zuwa na Hajiya.
"Ita ce! Karuwa la'ananninyar Allah! Ita ce ke bibiyar mijina.!"
Zuciya ya zo wa Ramlat wuya, wannan suna da Hajiya ke laƙabamata ya isheta.
"Ni ba karuwa ba ce, kuma da kike fadin wai ina bibiyar mijinki, ki tambayeshi ki ji sau nawa shi ya tako zuwa gidanmu da sunan zance."
Ba zato Hajiya ta shammaceta ta kifamata mafi, itama ba ta yi ƙasa a gwuiwa ba ta ɗaga hannu da zummar ramawa, tsawar Chairman ta dakatar da ita ta sauke hannun tana kara zura dara-daran idanunta cikin na Hajiya. Itama Hajiya Zeenatun kallonta take kafin cike da zafin rai ta dubi Chairman.
"Me na faɗamaka?! Me nace game da yarinyar nan?! Wallahi Dikko idan ba ka sallami wannan yarinyar a ma'aikatarka ba ka sani abinda ka binne a hannuna yake, da kaina zan tona asirinka a ..."
"Haba Hajiya Zeenatu, ya isa mana! Haba!"
"Ke wuce ki bar nan!" Ramlat ta haɗasu duka ta watsamusu banzan kallo kafin a fusace ta bar ofis din, ba ta jin ko ɗarr, ta shirya abinda ya fi kora daga aiki ma a yi mata idan har akan Hajiya ne. Matar da ba ta san darajar dan adam ba, ba ta kaicon a koreta daga aiki.
"Me kake nufi da hakan Dikko?!"
Hajiya Zeenatu ta furta rai a ɓace. Shima daure fuska ya yi yana saita tunaninsa.
"Na ce ki bar komai a hannuna zan dauki mataki a kanta ko?"
"Dikko na sanka kamar yunwar cikina, kar ka yi wasa da hankalina."
Wani murmushi ya yi.
"Haba Hajjaju, na fadamaki da kaina zan dauki mataki don wallahi nikam na ga abinda ba zan kyale ba."
Ta yamutse fuska.
"Me kake nufi?"
Ya gyara zama ya kora ruwa a cikin ƙaton tumbinsa sannan ya yi mata bayani daki-daki, wani murmushi ta yi kafin kuma ta kwashe da dariya yana tayata. Da yatsa ta nuna saitin kwanyarta.
"Kai dinnan na yarda akwai ƙwaƙwalwa!"
Ya shafi sanƙonsa.
"Haba Hajjaju! Ai mun ci dubu sai ceto. Ke dai ki kwantar da hankalinki."
Da wannan ta mike ta fice.
***
Da wani irin fushi take tuƙi, yanda Hisham ya matsu ta je su yi magana haka itama ta matsu ta je ta ba shi saƙo ya faɗawa Hussein akan matarsa. Har ta isa ƙofar gidan A'isha ba ta ji wani sassauci a zuciyarta ba. Maigadin zai budemata ƙyaure ta dakatar da shi, ko'ina ta rufe ta faɗa gidan.
Falon babu kowa shiru, sallama ta yi ba amsa don haka ta yi zamanta tana jijjiga ƙafa, tunawa da ta yi ba ta yi sallar La'asar ba ne yasa ta miƙewa ta faɗa ƙaramin ɗakin saukar baƙi na A'isha.
***
A'isha ta fito daga daki ta yi turus ganin jaka da mayafi, can kuma ta fahimci ko na wace, da wani ɗoki ta faɗa ɗakin da ta san za ta iya ganinta ciki, ai kuwa ta ji motsin ruwa a banɗaki, ba jimawa Ramlat ta fito. A'isha ta tsaya wani sakaka tana kallonta.
"Ke kuma ina kika shiga na zo ina ta sallama shiru?"
Maimakon ta ba ta amsa, sai ta jefamata tambayar da ke cinta.
"Lafiya kuwa? Kinga yanda idanunki suka kumbure suka yi ja?"
Guntun tsaki ta ja, tana jan skirt din atamfarta don ya sauka sosai.
"Bani hijabi."
Abinda ta ce kenan ba ta ko damu da ba ta amsa ba, A'isha ta juya ta fita can kuma ta dawo dauke da Hijab. Warware hijabin ta yi ta shiga kokarin zurawa.
"Ki kira mijinki idan ba ya gida ki ce na zo, sauri nake ba zama zan yi ba A'isha."
Daga haka ta shiga kokarin tayar da sallah hawaye na ciccikowa daga idanunta.
A'isha dai ta lura akwai matsala don haka ta fita ta ja mata ƙofar. Wayarta ta fitar ta kira Hisham kamar yanda ta nema ta sanar da shi zuwan Ramlat din. Ya yi mamaki don a zatonsa sai zuwa yamma.
"Ki ce ta ɗan ƙara hakuri, nan da awa In Sha Allah zan iso."
Daga haka A'isha ta katse wayar. Kicin ta faɗa ta haɗomata abinci a faranti da lemu da ruwa. Komai ta haɗa ta kai mata ɗakin, a sannan ta idar da sallah ta zauna kawai ta yi shiru. Ƙarasawa ta yi ta ajiyemata a gefenta kafin ta ce.
"Mun yi waya ya ce nan da awa zai iso in Sha Allah."
Gyada kai kawai Ramlat ta yi.
"Wai don Allah meke faruwa haka ne? Duk kin tayarmin da hankali na rasa nutsuwa."
Sai a sannan ta ɗan yi murmushin yaƙe.
"Ba komai."
Haushi ya sa A'isha miƙewa ta fice. Sai duk kuma ta ji ba ta kyauta ba, ai laifin wani ba ya shafar wani. Don haka ta janyo plate din ta tsakuri abincin gami da korawa da lemu. A falon ta tarar da A'isha ta ƙura wa talabijin idanu tashar Zee World. Babu tabbacin ma hankalinta na wurin. Zama ta yi.
"Ke Auta sarkin fushi, ba wani abu bane ba fa. A wurin aiki ne aka ɓatan rai."
Ganin haka itama A'isha ta sauko.
"Kai amma kin faɗarmin da gaba, dama nayi tunanin hakan. Allah Yasa dai ba wannan Halimar ba ce."
Murmushi Ramlat ta yi. Ta tuna irin walwalar da Halima ke yi na ganinta cikin wannan yanayi, wanda dai ba ya sonka zai wuya ya so ka.
Share batun suka yi suka koma hirar abinda ya shafi bikin Munir. A hankali kuma zuciyarta ta ɗan yi sanyi.
Karfe biyar da wasu mintocin, Hisham ya shigo gidan. Gaisawa kawai suka yi yana jan ta da zolaya sannan ya faɗa ciki don kimtsawa, A'isha ta mara mishi baya.
Ba jimawa ya fito da alama wanka ya yi, ya sauya daga manyan kaya zuwa jallabiya.
"Antinmu ina wuni."
Ta ɗan harareshi.
"Na gaji da wannan doguwar gaisuwar, na ƙagu ka faɗamin dalilin wannan neman don nima inada magana."
Ya yi dariya.
"Allah Ya ba ki hakuri toh."
Daga nan ya bata labarin komai har