Showing 189001 words to 192000 words out of 231786 words

Chapter 64 - KARFEN KAFA Book 1 COMPLETE (By Rufaida Umar).txt

zumunci ko?"


Kawu Adamu da mamakin yanda Modibbo ya san da zuwansa garin Kano ya ba da amsa ta wayar.


"Wa ya fadamaka na je Kano?"


"Ɗanka Yahaya muka yi waya ya cemin ka shigo Kano tare da Hassan. Ko karya ya ke yi?"


Ganin yanaamsawa a zafafe ne yasa dole Kawu Adamu ya sauko ya shiga bada hakuri da fadin.


"Wani ɗan uzuri ne ya shigo da ni, kuma shigowar ta gaggawa ce shiyasa ban samu na karaso ba. Amma ayi hakuri don Allah."


Kawu Modibbo ya yi shiru, can kuma ya ce.


"Wane uzuri ne haka?"


Har Kawu Adamu zai ba shi bayani sai ya tuna roƙon alfarmar da Hussein ya yi mishi akan cewar ba ya son Kawun ya san da batun aurensa. Bai faɗamasa dalili ba ko ba komai dai ya sani Kawun bai kaunarsu, amma shi kuma ya ce ba komai zai mishi wannan alfarmar.


"Daurin auren wani ɗan abokina ne ya kawo ni."


Kawu Modibbo ya ji sai dai bai yarda ba, maimakon ma ya ci gaba da sauraronsa kawai sai ya yanke wayar. Shiru ya yi yana tunani, ɓacin ransa na ƙara ninkuwa. Yanzun ya lura yan uwansa da wadanda ma suka tsani Amina da Aminu a baya da kuma wadanda dama ke sonsu, duk sun hada kai, shi aka ware. Wani bakin ciki ya ji a ransa, karshen satinnan zai tattara ya je Adamawar tunda akwai bikin yar gidan ƴar uwarsu, Gwaggo Karime. Tunda gaba daya za'a hadu, zai kara zaman meeting da yan dakinsu ya ji dalilin wannan sabon sauyin.


***
Bakwai da mintuna, Ramlat ta hada lafiyayyen friedrice da gashin kifi wanda a gefensa ta soya dankali ta saka sai sauce. Ta yi zoɓon da ya ji kayan kamshi ta sanya a firij. Sosai ta saki jikinta musamman wayar da suka yi da Amrah ta kara ba ta shawarar yanda za ta tafiyar da Hussein har ya fahimci shayi ruwa ne.


"Sannunki, sai a je a kimtsa jiki. Allah Ya yi albarka."


Ta juya bayan ta dora komai saman tebur, ta dubi Hajiya da ke fitowa daga ɗaki. Murmushi ta yi kawai ta kauda kanta. Ita kadai ta san me ta ke kissimawa a zuciyarta. Kwafa ta yi don gani ta ke komai ma za ta iya kawai don Hussein ya fahimci ya ƙuntata mata.


Maimakon kimtsawar, sai ta zube saman gado, wayarta ta jawo. Missedcalls har uku duk daga Baban Hanif. Kafin ta gama shanye mamakinta sai wani kiran ya kara shigowa. Ta ɗaga da sallama, ya amsa.


"Allah Ya huci zuciyarki Maman Affan, ina ta kira an ƙi a saurare ni ballantana kuma a yimin uzuri."


Ta mike zaune.


"Ka yi hakuri, ba haka bane. Ba na kusa. Ina wuni ya gida?"


"Lafiya kalau. Babu damuwa, na yi."


Shiru ya ɗan biyo baya kafin ya ɗora maganar.


"Na so maganar da zan maki ya kasance gani ga ki, amma ba na tunanin yanzu ina da wannan ikon na zuwa kofar gidanku. Da farko ina mai ba ki hakuri bisa dukkan wani abu da ya faru a dalilin aurenmu. Na yarda haka Ubangiji Ya tsaramana. A gaskiya Ramlatu, tun fara zancen aurena da ke, iyayena suka dakatar da ni bayan bincikensu yasa sun binciko tarihinki. Sun kuma gane cewar aurenki biyu ba kamar yanda ki ka fadamin cewa aure daya ki ka taɓa yi ba. Duk da labarin aurenki na farko da aka ban, hakan bai sa na gwuiwata ta sare ba. Na ci gaba da zuwa wurinki, idan ba ki manta ba, kin sha tambayata meke damuna, na ce maki ba komai. Wallahi wannan shi ne dalili."


Ya ɗan tsahirta, itama ba ta ce komai ba don dama ta san hakan kan iya faruwa, sai dai ba ta zaci za ta ji zafin abin har haka ba.


"Kina ji na?"


Ya tambaya, ta amsa da Uhm. Sannan ya ɗora.


"A takaice dai, wancan dalilin shi ne yasa iyayena suka ce sam ba da yawunsu ba muddin na aureki. Ina kokarin shawo kansu ne sai ga kira daga Kawunki (Baba Dakta), ya yimin maganar turo magabata, na ba shi bayanin halin da ake ciki. A karshe ya nuna ya kamata na hakura tunda har iyaye ba su so. Koda an yi ba dadinsa za'a ji ba. Amma wallahi Ramlat ina sonki. Ba yanda..."


"Karka damu, komai ai nufin Allah ne. Allah Bai kaddara zan zama iyalinka ba. Mu bar shi a haka. Allah Yasa ya zamemana alheri."


Ajiyar zuciya ya saki har tana jin hucinsa kafin ya amsa da amin. Daga nan suka yi sallama tare da yiwa juna fatan alheri.


Ta kurawa wayar idanu cike da tunani, kenan wai wannan abu da ta kusan aikatawa har ake fasa aurenta dominsa, da ace ta aikata yaya kenan? Nan da nan ta ji kwalla ta cicciko a idanunta. Da yanzun tana cikin yanayi irin wanda Halima ta tsinci kanta, da yanzu ita an ma kashe ta. Tausayin Hilal da ya fadomata a rai ta ji, rabonsa da Kano yanzun wata kusan biyu kenan. Tun sadda ya zo ya yi musu sallama akan ya samu sauyin wurin aiki zuwa Benue ba su ƙara jinsa ba sai jefi-jefi idan ya samu hawa online a whatsapp sukan gaisa.


"Uncle oyoyo!" Muryar Ansar da Affan ta ji daga falon, wannan ya nunamata cewa Hussein sun shigo din kenan. Ta mike ta shinshina jikinta, gaba daya kamshin girki ta ke yi, dolenta dama ta yi wankan ko ba don shi ba don haka sai ta rage kaya ta ja zanin wankanta ta fada bandakin.


Bayan ta fito ta shirya tsaf cikin doguwar rigarta na material, ba ta shafa komai a fuskarta ba, shimfida darduma ta yi ta zura hijabi ta hau sallar isha'i. Hajiya ta shigo har sau biyu tana magana. Na farko ta shigo tana wanka, na biyun kuwa yanzun tana sallah. Koda ta idar a gaggauce ta ninke dardumar ta fita. Ba ta son Hajiyar ta ƙara dawowa a karo na uku ta san rai ne zai ɓaci. Ba tare da ta cire hijabin ba ta fita.
Su biyu ne da shiga iri ɗaya, shadda ce ruwan blue, hatta da karamin aikin da aka yi musu iri guda ne. Hular kansu ma hakan ta ke, sun yi kyau har sun gaji. Su biyun ne kadai a falon, Hussein na zaune a ƙasa yayinda AlHassan ke saman kujera yana danna waya su Ummi zagaye da shi. Sallamarta ya sanya shi ɗago kai ya dubeta. Ta wani ɗaure fuska babu wani zumudi balle har ta kalleshi. Sai kawai shi din ya ci gaba da kallonta ƙasa-ƙasa yana kokari ya ga sun hada idanu. So ya ke ya karanci idanun ko zai gane manufar sauyawar fuskarta. Ta karaso gami da zama a hannun kujera ta gaishesu.


"Ranki ya dade Mrs Hussein, girman kujerarki ne ai. Idan laifi muka yi a yafemana, irin wannan shan ƙamshi, fitowar sai an ga dama?"


Kalaman AlHassan suka sa ta murmusawa, tana jin nauyinsa hakanan kawai.


"Ba haka bane, sallah na tsaya yi ne."


"To dafatan an samu a addu'a? Allah Ya amsa."


"Amin. Ina zuwa."


Daga haka ta mike ta nufi kicin, sarai ta na kallon Hussein ta gefen idanu, kallonta yake sosai, ta yi mamaki kwarai ganin ba ya daga cikin ɗabi'unsa.
Kayan abincin ta hada komai a tebur har ruwa da lemu ta ajiye kafin ta dawo falon ta yi musu iso zuwa saman teburin.


"Nikam da dai za ki sa a ƙasa ya fi min dadi. Kai fa?"


AlHassan ya fadi gami da duban Hussein. Ya gyada kai alamar hakan ma ya yi. Ta amsa da toh sannan ta koma kicin ta dauko katuwar ledar abinci wacce da wuya su yi amfani da ita idan ba azumi ne ya taho ba. Yanzun kam gashinan a kusa-kusa. Falon ta dawo ta matsar da centertable sannan ta shimfida. Bisa kuskure idanunta ya kai kansa, ta kauda kai lokaci guda tana kara hade fuska. Juyawa ta yi bayan ta ba Ummi umarnin bin bayanta. Marasa nauyin ta dinga ba ta ta kawo falon, ita kuma ta ji da masu nauyin. Komai ta jera, tuni AlHassan ya sauko, tana ji yana jan Hussein da hira amma yana amsawa tamkar ba ya so, a karshe sai shima ya kama girmansa ya watsar da shi ya maida hirar ga Ramlatu don tuni ta kora yaran ɗaki da kallo kawai. Sun san halinta, muddin aka yi baƙi zasu ci abinci to fa basu isa su zauna ba musamman ma tunda sun ci.


"Wai nikam Ramlat a ina kika koyi girki haka? Kamshin kadai ya mamaye hancina har yawuna ya tsinke tun kafin na kai baki."


Ba ta san sadda ta yi dariya har fararen haƙoranta na fitowa ba.


"Wurin Hajiyata mana. Amma dai ka bari ka ci kafin ka yanke hukunci."


Ta karashe gami da turamasa plate din da ta shaƙe da shinkafa ta kuma ɗoramasa kifin a gefe, ga zoɓo har turiri yake a kofi.


AlHassan ya jinjina.


"Gaskiya ne. Amma ko a ido ai an san mai dadi."


Ba ta ce komai ba banda murmushin, ta ja plate ta shiga zuba wa Gogannata wanda ya hau danna waya amma kacokan hankalin a kan hirarsu yake, shi kansa ƙamshin abincin dukan kofofin hancinsa yake yi, ya haɗiyi miyau ya fi a ƙirga. Ƙamshin zoɓon da ya ji citta da abarba da su flavour, yana kara kwaɗaitamasa son sha.


"Bismillah."


Ta fadi da wani salon kashe murya kamar ba ita ba. Ya ɗago kai ya dube ta. Hankalinta na ga zoɓon da take tsiyayawa a kofi ammafa kirjinta wani bugu yake don ta san idanunsa a kanta su ke kamar yanda jikinta ya ba ta.


"Na gode."


Ya fadi a ciki-ciki, ta ajiyemishi zoɓon, ta mike ta bar falon. Koda ta kai ƙofa, ta dan saci kallonsa, har sannan ita ya ke bi da ido duk kuwa da cewar ya kafa kofin zoɓon a baka. Mamaki ya sa ta saurin kauda ki ta shige daki.






Wani dadi ranta ya yi tana jin kamar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha. Wato dai haka Hussein ke ji idan ya na mata wannan shan ƙamshin. Ta yi dariya ita ɗaya a ɗaki kafin ta kife saman gadon cikin annashuwa. Sai da aka kwashe mintuna talatin sannan Ummi ta shigo kiranta. Ta maida hijabin ta fito, sun kammala har ma Hajiya ta fito, kayan kuwa ta tabbatar Ladidi ce ta kwashe tunda ba ta kai ga tafiya ba.


Hussein ya miƙe ya fita tare da Ansar, zuwa can sai ga Ansar din ya dawo.


"Mami, ki zo inji Uncle."


Ta dan saci kallon Hajiya da AlHassan, hira suke abinsu kamar uwa da ɗa, ganin ba su damu da kallonta ba yasa ta miƙewa ta shiga daki. Sai da ta ɓata mintuna fiye da biyar ba don kuma wani abun ta ke shafawa ko gyarawa ba, can kuma ta fito ta fice.


Yana tsaye a jikin motarsa ya harde kafafu hakanan hannunsa a harɗe a kirji. Tun tahowarta ya ke kallonta. So da kaunarta na ratsa dukkan wani ɓangare na zuciy da gangar jikinsa sai dai shafe mintocin da ta yi ba ta fito ba ya yi masifar sosa ransa. Don haka koda ta tsaya sai shima ya ja baki ya yi shiru. Ramlat ta soma gajiya da tsayuwar don haka ta dubeshi babu fara'ar a zo a gani.


"Shikenan ina iya tafiya?"


Kallon da ya watsamata yasa ta kallon gefe guda.


"Idan har ba ki daukeni a bakin komai ba, kina iya tafiyar."


Shiru ya biyo baya, jin ba ta ce komai ba sai ya sauke ajiyar zuciya.


"Akwai abinda na yi maki? Ko kuwa duk baƙin cikin na rabaki da masoyinki karo na biyu ne?"


"Komai nufin Allah ne. Haka ya tsaramin a rayuwa. Na kuma karɓa da hannu bibbiyu."


"Hakane, sai dai kina nufin ba da son ranki ba?"


Yanda ya yi maganar da wani irin sanyi, yasa ta yin murmushi kadan.


"Kamar yanda kaima ba da son ranka ba, haka nima yake a wurina. Ina ganin dai mun yi anko."


"Yaushe kika fara duba? Me kike nufi da mun yi anko?"


Daga muryarsa ta gane ɓacin ransa, ta kara gyara tsayuwa gami da ɗan dubansa.


"Daga ni har kai, mun yarda da kaddara mai kyau da marar kyau saboda mu din musulmai ne. Kamar yanda na ji batun aurenmu da kai daga sama, haka Allah Ya bani ikon karɓar lamarin matsayin kaddarata kuma mai kyau. Ko ba komai na shaida kana da ɗabi'u masu kyau daidai gwargwado. Hakanan iyayena da suka haɗa ni da kai, na tabbatar ba za su cutar da ni ba har abada. Bana so na ƙara yin gangancin saɓa umarninsu."


Tana kaiwa nan ta sunkuyar da kai don ba ta kaunar kallon da yake jifanta da shi da ta kasa ganewa.


"Ba wannan na tambayeki ba. Tambayar da na maki, kenan ba...Shikenan dai. Hakan ma is good."


Ya fasa nanata tambayar, sai ya share. Can kuma ya kara magana.


"Ku mata kun fi kaunar wadanda za su tsaya su na furtamaku kalaman so a baki alhalin idan aka yi auren ba lallai su iya tafiyar da lamuranku yanda ake so ba. Ina da tabbacin har da wannan a bahagon tunaninki."


"Me ya kawo batun so? Ai bana jin akwai shi a tsakaninmu. Ba ka san cewa ko ba aure ana yin so ba?"


Ya ji zafin kalamanta don haka shima ya shirya ramuwa.


"Shiyasa ki ka kasa hakuri da auren da babu so?"


Ta dubeshi, wani murmushi ya ke ganin ya ci galaba ta fusata. Ta kasa haɗiye maganar da ke cinta, ta maida mishi martani nan take.


"Yanzu ai gashinan zan yi. Ko ba komai a rayuwa ana koyon darasi, da auren so da wanda ma babu soyayyar, duk darasi ne a gareni. Na kuma gani. Idan a baya na yi na soyayyar, yanzu na hakura zan jarraba wanda babu soyayyar na ji yanda ake ji. Ko itama tana dauwama ko aa."


Tana kaiwa nan ta soma tafiya da zummar barin wurin, ya riƙo hannunta ta dawo baya. Ta juya da sauri gami da kokarin janyewa amma ina karfin ba ɗaya ba.


"Ka cikani tunda dai ka riga ka san cewa haramun ne."


Idanunsa tuni sun kaɗa. Shi Ramlat ke nufi da ba ta so ko me?


"Idan wasa ki ke yi, bai miki kyau ba. Ina miki rantsuwa da Allah, ko yankar naman jikin Hussein za ki dinga yi kullum kina gasawa tsabar ƙiyayya, sai kin zauna da ni muddin aka ɗaura aurenmu. Idan kika ga kin fita daga gidana, to ki sa a ranki, ƙasa ce za ta zama makwancinki a ranar. Babu fitar yaji ko kuma saki. Kar ki shigo gidana da makami, zan miki tanadin kala-kala sai wanda kika zaɓa. Zan iya mutuwa, amma har abada kar ki ji a ranki za ki shigo gidana kuma na rabu da ke. Har abada Ramlat."


Ta dubeshi da idanunta da suka cicciko, ba karamin fusata ya yi da zantukanta ba. Jikinta ya yi sanyi, ya saki hannunta ya faɗa motar gami da rufewa da karfi. Ta ci gaba da tafiya kamar wacce kwai ya fashewa a ciki ta bar harabar wurin zuwa ciki.








I just published "BABI NA HAMSIN DA BAKWAI" of my story "Ƙarfen Ƙafa". https://www.wattpad.com/1018053716?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Rufaida-Umar&wp_originator=H1vXb7%2FW6A2U5P8fFwbtuiA8loSGt%2B%2BNft8tDKy3EJM810crtMGUnxqUIIutxZI04rTU84moV3sLlZ4ErYDW%2BHsUJ6yuYaxKr9kgvrgaa2%2BsQQrAwLvUCmdmO42m8ACV










🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️


_*Rufaida Umar*_


Bismillahir Rahmaanir Raheem.


57)




Kiciɓus ta yi da Alhassan dake fitowa, ta yi saurin sunne kai kamar mai jin kunya. Shi kuwa a fisge da suka hada ido ya gane kamar ranta a ɓace yake.


"Har ka fito?"


Ta furta cikin dakiya, ya dan yi dariya.


"Na fito Amarsu, zan wuce. Gobe dai zan koma Adamawa sai ranar daurin aure in sha Allah."


"Allah Ya tsare hanya. A gaidamin su Aunty Kausar da Fatima."


"Zasu ji in sha Allahu."


Daga nan suka yi sallama ta shige ciki shi kuma ya nufi wurin motar yana ta tunani. Koda ya shiga, ya dubi Hussein da ya ɗago kai daga saman sitiyari.


"Lafiya? Na ganka wani iri kamar yanda itama Ramlatun na lura da damuwa a fuskarta. Meyafaru?"


"Nothing."


Ya amsa a gajarce sadda ya tayar da motar suka bar harabar gidan. AlHassan bai kara magana ba banda baki da ya taɓe. Sai da suka yi nisa ne kafin ya ji ya kamata ya ce wani abu ko da shawara ce sanin halin mutumin.


"Idan mutum yana son mace, kwantar da kai ya ke yi ya nemi soyayyarta. Mace ba ta son gadara ko taƙama, mace kulawa ta ke so da kuma a nunamata soyayya a fili kuma a gaban kowa. Ban san me ya haɗaku da Ramlatu ba, amma na kalli abin a mahangar ba ka taɓa soyayya ba, asalima matan ke binka a baya kana yanƙwana su. Idan har ka ce ta wannan hanyar za ka siye zuciyar Ramlatu, abun zai ba ka wuya daga kai har ita. Kar ka yi wasa da damarka."


Hussein tun soma maganar ɗan uwansa, bai katse shi ba, kamar yanda kunnuwansa ba su bar sauraronsa ba. Sai da ya kai karshe ne ya ɗan yamutse fuska.


"Su matan ba za su iya hakuri da kowace kulawa ta biyo bayan aure ba? Dole burinsu tun su na waje a nunamusu?"


Abin ya ba AlHassan dariya.


"Ka taɓa ganin inda aka yi cinikin biri a sama? Ko kuwa su matan kana tunanin sun san gaibu da nan take za su karanci halayyar mutane irinku? Su ba wannan a gabansu, su dai su gani a ƙas. Kuma dama ai amfanin taɗin kenan, a fahimci juna a kuma ga ko za'a iya zama a jure halayyar juna. Na tabbatarmaka idan ka ci gaba da tafiya a wannan shan ƙamshin naka da rashin maida hankali, za ka sha wuya a hannun Ramlatu bayan aurenku."


Murmushi Hussein ya yi don shi mamaki ma maganar ya ba shi.


"Wai zan sha wuya hannun Ramlat? Anya? Don Allah na yi kama da mazan da za su sha wuya hannun mace?"


Murmushin shima AlHassan ya yi gami da gyara zaman gilashinsa.


"Da sauranka ɗan uwa. Bari na kyaleka, gani ya kori ji. Nidai idan ta fara gasa maka aya a hannu, kar na ganka a ƙofar gidana."


Suka yi yar dariya a tare. Shi Hussein dariya yake don ganin hakan yake kamar wani almara ko tatsuniya. Bai ce Ramlatun ba ta da kyau ko tsarin da namiji zai rikito a kanta ba, tunda shi shaida ne, ganinsa da ita tun farko ya ji kawai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login