Showing 207001 words to 210000 words out of 231786 words

Chapter 70 - KARFEN KAFA Book 1 COMPLETE (By Rufaida Umar).txt

Hanif na neman yimin shigar sauri. Sai dai ban sha wahala da shi ba saboda takanas Baba Dakta ya neme ni ta waya lokacin muna Adamawa ya ce idan har dagaske nake to shi kam hankalinsa ya fi nutsuwa da ni, bai kuma tunkareni ba sai da ya ji ta bakin Hajiyarmu. Bai fadamin dalilin da yasa aka bar maganar Baban Hanif ba, ya dai bani damar na turo magabatana tunda har kin bar masa wuƙa da nama, to shi kuma ya zaɓamaki ni a matsayin mijin aure. Na ji dadin lamarin sosai. Anan ne muka yi shawara da iyayena, ba ɓata lokaci muka taho Kano tare da ɗan uwana da Kawu Adamu. Aka shige gaba aka yi duk abinda ya dace. Kin ji dukkan abinda ya faru."


Ta gyada kai tana murmushi, ya saki hannunta ya miƙe, kayan kallo ya shiga kashewa kafin ta ga ya soma rage fitilun falon bayan ya tabbatar kofar falon a rufe ta ke gam! Ganin haka sai ta mike ta tayashi da rufe kofar fita na kicin da kuma kashe fitilun da rufe kofar kicin din gaba ɗaya. Koda ta juyo sai suka ci karo, ya yi saurin riƙota. Goshinsu haɗe wuri guda kowannensu na maida numfashi, za ta zame ya yi saurin riƙeta da kyau. A hankali kuma ya ja baya.


"Ban gama ba ki labari ba, ki yi shirin kwanciya ki zo, ina jiranki."


Daga haka ya yi gaba tana kallo ya buɗe ƙofar ɗakinsa ya shiga. Ta sauke ajiyar zuciya, ba ta daina murmushi ba kamar yanda ba ta gaji da jin wannan daddaɗan labarin da ya ke ba ta ba. Ta tuna Kawu Bello da ya ce dama Hussein din ya taɓa neman aurenta wurin Baba Dakta bai samu ba sai a wannan karon. Da wannan tunanin cike da wata iriyar kasala ta ƙarasa ɗakinta. Sai da ta ƙara wanka don ƙamshin da ta ji Hussein yana yi sai ta ke ji kamar ita banda wari ba abinda ke fita daga jikinta. Loko da saƙo duka sai da ta bi ta wanke kafin kuma ta fito ta goge jiki ta shiga mulka turaruka masu kamshi kala-kala. A ƙarshe ta fiddo wata doguwar riga mai hawa farare ƙal ta sanya, ta ɗora hula da ya rufemata gashinta. Duban kanta ta ke yi a madubi, rigar ta ciki da kaɗan ta wuce gwuiwarta sai top din da ta ketare zuwa ƙaurinta. Girgiza kai ta yi, a haka ma kwarjini Hussein ke mata ina ga kuma ta isa gabansa a haka? Da saurinta ta karasa wardrobe ta fiddo zani. Ido ta fiddo waje kirjinta ya harba jin hannuwansa zagaye a ƙugunta.


"Kin yi kyau, shi ne ki ke kokarin rufemin abinda Allah Ya halarta min gani?"


Ta lumshe idanu, kunya sosai ta ke ji, ta kasa kataɓus. Juyo da ita ya yi suka fuskanci juna. Har lokacin ta kasa buɗe idanun. Kallon fuskarta kawai ya ke yi yana jin sanyi a zuciyarsa. A ƙasan ransa banda hamdala babu abinda ya ke yiwa Ubangijinsa. Jin shirun ya yi yawa ne ta bude idanunta ta dubeshi. Ganin idanunsa har sannan a kanta suke sai ta yi azamar ja baya ta cire jikinta daga nashi.


"Ki yi alwala." Ya juya ya koma ɗakinsa, ta sauke ajiyar zuciya. Hussein zai kasheta da kala-kalan soyayyarsa. Jikinta ya yi sanyi da ta tuna ba ta da sallah, daga yanayin Hussein ba sauki. Sai kawai ta ji ya ba ta tausayi. Ta kashe fitilu ta rufe kofar, tana tafe tana tuna aurenta da Aliyu, ranar da aka kawota sam ba ta da walwala ko misƙala zarra, wannan karon kam Allah kadai Yasan yanda ta ke jin zuciyarta musamman idan ta tuna yan uwanta da ma abokan arziki duk suna son aurenta da Hussein. Wannan ma abin ta ƙara godewa Allah ne. Fatanta Allah Ya basu zaman lafiya da iyali nagari.


Yana saman darduma, ga dukkan alamu sallah ya idar, ba ta shiga dakin ba tun da aka kawo ta sai lokacin. Sosai ya burgeta. Dardumar da ta ga ya shimfida sai ma ya ba ta dariya ta danne. Ganin ta koma gefen gado ta zauna ya sanya bayan kammala addu'arsa ya dubeta.


"Sallah fa?"


Ta kalleshi ta sunkuyar da kai, daga yanayinta ya gane cewa ba maganarsa. Don haka ya mike kawai ya yi nafilarsa ya yi addua, tare suka shafa ya miƙe.


"Taho mu kwanta na ƙarasa ba ki labari."


Yana fadin hakan ne yana nufar makunnin fitilun dakin, kashesu ya yi gami da kai hannu ya kunna na gefen gadon. Hasken ba yawa, kwanciya ya wuce zai yi kai tsaye.


"Ɗan tsaya." Ta dakatar da shi, ya ja ya tsaya kawai yana kallonta. Abin rufar ta ja ta kakkaɓe gadon ta gyara zaman filon kafin ta dube shi da murmushi.


"Bismillah."


Ya kwanta itama ta kwanta, fitilar ya kashe. Ɗakin ya yi shiru na wani lokaci, numfashinsu na gauraya wuri guda kowanne na shaƙar daddaɗan ƙamshin jikin ɗan uwansa. Ya kai hannu ya zame hular kanta, yana shafa kitsonta, ta lumshe idanu. Ya soma magana.


"Heart, kin yi zaton ba sonki nake ba, kamar ma dai kawai zan aureki ne. Ba ki san cewa Hussein ya soma sonki tun kan ki soma sonsa ba."


Duk da cewa babu haske sai da ta zaro ido. Kunya ta sanya ta runtse idanunta. Dama ya san tana sonsa?


Shi kuwa jin ta yi shiru sai ya kai hannu saman fuskarta, murmushi ya yi mai sauti.


"Kar fa ki yi mamaki, na sani. Sai dai ba karamin nishaɗantuwa na dinga yi idan naga kin yi narai-narai kina son yin kuka duk a tunaninki na bana sonki. Sai Hisham wanda yake sanya ni nishaɗi idan ya sauya fuska yana tayaki yaƙi. Kuma yasan sarai ina sonki amma na nunamasa nifa a'a."


Hannunta ya kai saman kirjinsa. Ta nutsu tana jin yanda ya ke bugu da ƙarfi.


"Kamar yanda kike jin zuciyata na bugawa a kowane daƙiƙa, wallahi Ramlat haka nake jin sonki a kowane dakika. Kwakwalwata ba ta taɓa samun hutu daga tunaninki ba, kar ki ƙara ji a ranki cewa zaman doya da manja zamu yi. Kar ki ƙara sanya wa a ranki wannan bawan Allahn ba ya sonki. Kinji?"


"Uhm." Ta faɗi a hankali, hakan yasa shi janyota ba shiri ya shiga aikamata saƙonnin da suka birkita tunaninta har ta shagala itama wurin maida martani. Nan fa ta ruɗa Hussein, ita kuwa shawarwarin yayyunta da su Amrah ke yawo a kwakwalwarta.


_*"Kar ki wasa da kowacce dama, kar fa ki manta Hussein bai san soyayya ba sai a kanki. Don haka ki saki jikinki ki rike mijinki da hannu bibbiyu."*_


Ta tuno kalaman Maman Twins.


***
WASHEGARI....


Tana jin sadda ya maida kanta saman filo madadin a farko da yake a saman kirjinsa, ya gyaramata ya ƙara rufe ta da tattausan bargon sannan ya miƙe. Murmushi ta yi ta buɗe idanu, banɗaki ya buɗe ya shiga, nan ya fahimci Asuba ce. Ta kai hannu a hankali ta shafi makwancinsa, so da kaunarsa marar adadi na kara ninkuwa a zuciya da gangar jikinta. Idan ta tuna manyan kalamai da kuma yanayin ruɗewar da ya yi duk a kanta, Hussein kuka na hawaye ne kawai bai mata ba, ya yi wani furucin da dole ya ba ta tausayi a sannan wato inama a kanta ya soma aure. Jin motsin fitowarsa bai sa ta rufe idanunta ba saboda fitilun ɗakin a kashe suke. Ganin yana laluben makunni yasa ta saurin rufe idon. Kimtsawa ya yi ya fice masallaci a gaggauce don ya so ya makara.


Tana jin fitarsa ta kunne bedside lamp ta mike zaune rungume da bargo, murmushi take kamar wata sabuwar kamu, ta gaji da murmusawar ta koma ta kwanta bayan ta kashe fitilar. Har Hussein ya dawo ya hau gadon ya jawota jiki, idanunta ƙirr. A hankali kuma wani sabon daddaɗan bacci ya soma fisgarta.


Ita ta riga shi farkawa wuraren karfe bakwai da rabi na safe, miƙewa ta yi ta nufi dakinta. Kai tsaye brush ta soma sannan ta faɗa wanka tana ji kamar an mata albishir da gidan Aljanna. Ba ta da wani sauran buri mai yawa a yanzu face na ta kyautatawa mijinta hakanan da addu'ar Allah Ya rayamata yaranta, Ya ja kwanan Hajiyarta mai sonta.


Koda ta fito shiryawa ta yi cikin doguwar rigar atamfar da ta matse daga sama, ƙasan kuwa ya buɗe amma ba sosai ba. Ta yi kyau musamman ma kwalliyar da ta yiwa fuskarta. Sai da ta shafa turare a gaggauce kafin ta fito da zummar shiga kicin. Sai dai ƙarar wayarta ya katse hanzarinta, ganin sunan Hafsat ta ɗaga. Suka gaisa.


"Dama kira nayi na ji ko kun tashi. Ganinan zan kawomaku abin kari."


"Toh Hafsat, sai kin karaso."


Daga haka ta ajiye wayar, ba jimawa aka kwankwasa ƙofar. Buɗewa kawai ta yi don ta san Hafsat ce. Suka yiwa juna murmushi. Ta karaso ta ajiye kayan hannunta saman tebur. Duk yanda ta so akan ta tsaya su yi ƴar hira amma ina ta ƙi.


"Rufamin asiri Adda Amal, zan dawo anjima dai in sha Allahu. Ban shiryawa faɗan Hamma Hussein ba."


Dariya ma ta ba Ramlat, suka yi sallama ta tafi. Ciki ta koma don ta ga ko ya farka. Tsaye ta iske shi daga shi sai gajeran wando sai kuwa tawul yana faman goge sumar kansa. Sunkuyar da kai ta yi gami da kokarin fita. Caraf ya damƙo hannunta.


"Dodo na zama?"


Ta girgiza kai tana murmushi ba tare data juyo ba. Dawo da ita baya ya yi, ta kasa kallonsa. Karshe ta wayance da gaidashi. Maimakon ya amsa sai ya sumbaci kuncinta.


"Kin yi kyau sosai."


"Na gode." Ta furta a hankali.


"Tunda ba za'a taya ni ba, a zauna a jira na kammala."


Ba musu ta karasa gefen gadon ta zauna, ganin ya juyamata baya yana kallon madubi yasa ta ɗago kai tana ƙarewa mijinta kallo da irin baiwa da ni'imar da Allah Ya mishi na kyawun sura. A fakaice yana kallonta, dariya ma ta dinga ba shi, satar kallon na mene alhalin shi ɗin nata ne halak malak? Har ya kammala da gaban madubin ya juyo bai bar murmushi ba, ganin ya juyo kuwa ta yi saurin kauda kai. Ƙananun kaya ya fiddo ya sanya. Ya koma gaban madubin ya fesa turare, a ranta ayyanawa take son ƙamshi irin na Hussein ko mace sai haka.
Kafin ma ya tunkarota ta mike, suka dubi juna kowanne da abinda ya ke saƙawa a ransa. Ta sunkuyar da kai.


"Barka da Asuba, fatan ka tashi lafiya?"


Ya kama hannunta ya jawota ya sa a jikinsa sosai.


"Lafiya na tashi, ina fatan kema haka?"


Suka kwashi ƴan sakanni kafin ya hau yi mata raɗa a kunne, kunya ta sa ta tureshi tana murmushi.


"Mene hakan wai?" Ta faɗi kamar za ta yi kuka. Ya taɓe baki.


"Gulma ce bana so."


Hararar wasa ta mishi ta juya da sauri ya kuwa bi bayanta yana fadin.


"Ni kike wa wannan kallon?"


Ganin dai kokarin cafketa ya ke yasa ta juyo tana dariya.


"Don Allah ka yi hakuri, na tuba."


Ya shafi sumar kansa kawai ya yi gaba zuwa tsakiyar falon.


"Nan za ki kawomin mu ci, bana son can."


Ta amsa da toh kafin ta yi gaba yana binta da kallo kamar za ta gudu ta bar shi. Sai da suka kammala karyawa tsaf sannan ya bata umarnin saka mayafi su je gaida Dada. Ɗakinta ta koma, dama ba nisa mayafin ya yi ba, ta gyara zamansa sosai ta zura flatshoe. Koda suka kama hanya, hannunta ya lalubo ya kama ya murza har sai da ta lumshe ido ba ta yarda ta kalleshi ba. Ɗan matsowa ya yi har kafaɗunsu na gogan juna.

"Wai ni bakin tsiwar naki mutuwa ya yi? Ko na lalubo amsar a daren jiya?"


Ta tsaya cak ta shiga kokarin zame hannunta a nashi, ya kara damƙewa yana dariya.


"Wallahi sai na ɗaga ki cak mu shiga har wajen Dada. Kin san zan iya ko?"


Dole ta hakura ganin akwai ma'aikata a farfajiyar gidan ta kuma tsorata don ta san halinsa dagasken yake.


Dada ta yi farin ciki matuƙa da ganinsu, ita kuwa Ramlat wacce ta samu dakyar ya saki hannunta, kunya sosai ta ke ji don ma Allah Ya taimaka baƙi duk sun watse, wasu yau da Asuba suka wuce.


Anan wurin Dadar ya bar ta ya fice wurin AlHassan.


***
KANO...


*DA SAURAN RINA A KABA..!*








I just published "BABI NA SITTIN DA BIYU" of my story "Ƙarfen Ƙafa". https://www.wattpad.com/1024183736?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Rufaida-Umar&wp_originator=kerlmbTD11RJIZ1OU3cjRAuaKiLriOJD0fY0ly4CVNRLiEciXy1qh%2BgcHslN3fAHkmM%2BuxbSZlMyLFyekdT2BAKcap35wfLbDInDLU%2Bf6jBwfeAcG9qlXUARTAIfqHS%2B








🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️


_*Rufaida Umar*_


Bismillahir Rahmaanir Raheem.


62)


*Assalamu alaikum masoya Karfen Kafa. Ina mai ba ku hakurin jinkirin da ake samu kafin posting. Ku yi hakuri pls. In sha Allah aski ya zo dab gaban goshi.* 🥰






Hajiya Batool ta zabga uban tagumi tana kallon Aminiyarta, ba ta san ta inda za ta fara magance mata matsalarta ba alhalin ita kanta yanzu cikinsa ta ke. Gaba daya ɗanta ya kwashi matarsa sun bar garin sun koma Abuja da zama. Waya ta kira sai ya ga dama yake ɗagawa balle a kai ga aike. Komai na rayuwa ya sauyamata, kasuwancin ya ja baya babu albarka ciki.


Hajiya Zeenatu wacce ta gama kai wa bango da shirun Batool, ta kundumar ashar da faɗin.


"Wannan wane irin wulakanci ne Batool, na kawomaki kukana ina neman mafita shi ne tsabar wulaƙanci ki ka shareni ki ka maida ni wata banza?! Hussein ne fa, kin fi kowa sanin yanda nake son Hussein amma har na gama ba ki labarin cin kashin da ya yimin gaban yan uwansa ki kasa jajantamin?!"


Tana maganar tana faɗa rai a ɓace. Hajiya Batool ta sauke ajiyar zuciya.


"Me zan maki? Wane irin nusarwa ce ban maki ba don Allah? Amma ke makahon son yaron nan ya sanya ba kya ji ba kya gani, ai gashinan ya nunamaki shi na zamani ne!"


Hajiya Zeenatu ta yi kwafa, ba abinda ya faɗomata a rai sai cin mutuncin da ya yi mata a farkon haɗuwarsu, da gaskiyar Batool da ta ce makahon so ya rufe idanunta. Ta sauke ajiyar zuciya.


"Naji, koma me ya faru, ina da hannu a ciki. Amma kuma kin san ba zan zauna haka ba ko? Kin san sai na rama? Ki tashi mu shirya mu leka wurin Gora. Mene a ciki? Zan durkusa na ba shi hakurin laifin da na yi mishi idan ya so ya samarmana mafita."


Hajiya Batool ta yi shiru, itama fa yanzun tana da bukatar hanyar da za ta bi a karkato da hankalin ɗanta gareta, ta kuma amince idan ya dawo ko wacece ya aura idan har hakan zai yiwa Fa'iza ciwo. Abinda ma ta lura da shi, itama kanta Fa'iza tama tsubbace-tsubbacenta shi ne dalilin da yasa ta fi karfinta. Sauke ajiyar zuciya ta yi, ta tuna kowacece Fa'iza, dama tun can ƴan gidansu ba wata cikakkiyar tarbiyya ce da su ba, ganin irin arzikin da ubanta ke da shi matsayinsa na tsohon minista ya sanya tun ɗanta bai wani ba soyayyar da Fa'izar ke mishi muhimmanci ba, har sai da ta yi yanda ta yi ta tursasashi. Yanzun gashinan tana girbar abinda ta shuka.


"Na yarda muje. Idan ma bai sauraremu ba, za yiwa Mariama waya mu wuce Nijar kawai. Na fi yarda da aikin buzayennan ma."


Da wannan suka shirya suka fice wurin Gora.


***
ADAMAWA..


Dada ta dubi Ramlat cikin nutsuwa ta ce.


"Kinga abin Allah ko? Ba ya kyale azzalumi, shiyasa duk abinda aka dage da kai kuka gareShi, watarana zai shuɗe ya zama tarihi. Ba wanda ya fi ban mamaki a lamarin sai ɗan uwana Modibbo, ban yi tsammanin ƙiyayyar ta kai har haka ba, amma ina nan inda nake, shiru ma magana ce. Allah ne zai maganinsa don nikam ban isa nayi ba. Ba na jin wannan karon zan iya yafemishi wannan zaluncin da ya yimin ni da yarana. Duk yanda zan so na ji alaƙarsa da matarnan, zan jira har zuwa lokacin da zai kawo kansa garemu."


Hafsat da ke zaune itama sai ta ji jikinta ya kara sanyi, wayarta ta kara kalla, wani saƙon ne na Taheer ya kara faɗowa, duka dai ban hakuri ne da nuni da yake mata cewar laifin wani ba ya shafar wani. Kalaman soyayya zafafa ya ke jifanta da su, ta yarda so ba karya ba ne, tana son Taheer sosai, duk da son ta ke mishi bai kai wanda shi ya ke mata ba, amma dole za ta sanyawa zuciyarta dangana. Ta san babu ta yanda aurensu zai yiwu. A hankali ta mike ta zame daga falon ta shige ɗaki, hawaye ne ya tahomata sai dai dole ta haɗiyeshi. A yanda ta ke da zafi, ba ta yi zaton soyayyar Taheer zai russunar da ita har haka ba har ma ta ji inama ɗan wani gidan ne daban ba gidan Kawun ba.


Ɓangaren Ramlat itama haka ta koma sashinta cike da tunane-tunane, ta kara ganin girma da ƙimar uwar mijinnata. Tabbas mahakurci mawadaci. Kai tsaye ta shiga gyaran duk inda bai ba ta ba, sai da ta tabbatar gidan ya kimtsu babu sauran dauɗa da kayan datti a kicin sannan ta kara gyara jikinta ta shirya cikin doguwar riga ƴar kanti milk mai adon duwatsu. Sam ba shi da nauyi. Ta feshe ko'ina na jikinta da turare. Saman doguwar kujera ta shimfide ta zurawa ƙaton enlargement na hoton mijinta idanu. Murmushi sosai ta shiga yi tana tuna kalamansa da ma saƙonni da dama waɗanda ya isarmata a daren jiya. A hankali ta lumshe idanunta wani farin ciki na mamayeta, wani lokacin ta kan ji kamar mafarki, wai yau ita ce a garin masoyinta kuma matsayin matarsa. Ta jima cikin tunani kafin wani bacci mai dadi ya kwasheta.


Ya jima da shigowa gidan, sai dai yana sashen Dada su na tattauna. Koda ya karaso gidan, ya isketa tana bacci murmushi kawai ya yi, ciki ya karasa ya rage suturar jikinsa ya ɗan watsa ruwa don ba laifi garin ana ɗan zafi. Gajeran wando three-quarter ya sanya da yar shirt marar hannu, gaba daya ƙirarsa ta bayyana muraran. Koda ya fito ya ci karo da Hafsat da ke faman sallama amma gwanartasa ba ta ji ba. Kofar ya bude ya sanya yatsa a bakinsa yana mata alamar ta yi shiru, murmushi kawai Hafsat ta yi hango dalilin, Adda Amal ke

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login