Showing 216001 words to 219000 words out of 231786 words
Chapter 73 - KARFEN KAFA Book 1 COMPLETE (By Rufaida Umar).txt
gafararta cike da shagwaɓa. Murmushi Dada kawai ta yi gami da jinjinawa Ramlatun. Ta tabbatar aikinta ne.
***
A ɓangarenta kuwa, ganin fitilu a kashe ya ba ta mamaki matuƙa, ita dai ta san ba ta kashe ba. Haka ta ci gaba da tafiya a hankali har ta kai ga makunnin, kafin ta kunna ya riga ta. Ta juyo ta dubeshi, kafin ta kai duba ga cikin falon. Baki da hanci kawai ta saki tana dubansa ta kuma maida duba ga abinda idanunta ke gani.
I just published "BABI NA SITTIN DA HUƊU" of my story "Ƙarfen Ƙafa". https://www.wattpad.com/1028701620?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Rufaida-Umar&wp_originator=0Ip%2BQlXDoaoxyM7eqonDyl6cCNMjLR7b13cfWz0PO6rluIvQeUuu1jHeHigNXBE4IV%2Fm159PS%2BDsIeqGDHiIXMY5fTO3p4OINuf3vYe6Dx12trWJCYsK2knobbhhwa9y
🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️
_*Rufaida Umar*_
Bismillahir Rahmaanir Raheem.
64)
_*Assalamu alaikum yan uwa Barkanmu da wannan lokaci. Ku yi hakuri kun sha jira, da yardar Allah kiris*_
Wani ƙaton enlargement ne na ɗaya cikin hotunanta da ya ke da su, ta karkace kai tana murmushi har fararen haƙoranta sun fito, sai wani ƙaton kwali da ba za ta iya cewa ga abinda ke ciki ba sai kuwa akwatuna jere reras har guda sha biyu. Ta kai dubansa gareshi, murmushi ya ke sakarmata sosai. A hankali ya matso ya kama hannunta suka karasa cikin falon. Wani ƙaramin kati mai adon heart da fulawoyi ne ya soma daukar hankalinta don haka ta sa hannu ta ɗauka ta bude.
_*From the moment I first laid eyes on you, I knew you were a perfect match for me. I love everything about you Heart.*_
Ta juyo ta dubeshi, yana tsaye kawai hannuwansa cikin aljihun wando yana zubamata murmushi. Da ido ya mata nuni akan ta ci gaba da buɗewa. Ba musu ta kai durkusa ta kai hannu ta bude wani karamin gida na zobe, ai kuwa zoben ne mai matukar sheƙi, ya fi mata kama da na azurfa. Ya yi masifar burgeta, idanunta ya ƙara kaiwa saman wani kwalin karami da aka ɗaure bakinsa da igiya mai ƙyalli, ta bude, ganin mukullin mota kawai sai ta ɗago ta dubeshi, idanunta nan da nan suka cicciko da kwalla. Ta ajiye kafin ya taimaka mata da bude akwatinan, kaya ne maƙil, kowanne da set dinsa. Yanda dai ku ka san lefe irin na budurwar yarinya don wannan ma ya fi na budurwar kyau da tsari. Ko iyaka haka aka tsaya a na budurwa sai sam barka. Laces, atamfofi, mayafai, shadda, yadika, abayoyi da dukkan sauran kayayyakin shafa da sarƙoƙi ba abinda ba'a haɗa ba. Wannan ya bata tabbacin ba yau ya soma haɗawar ba. Bayan sun mayar da komai ta dubeshi, tuni hawayen da ta ke dannewa sun zubo. Ya kai hannu da sauri ya ɗaukemata su. Ba ta bar kallonsa ba ta soma magana.
"Allah Ya saka da dumbin alheri, na.."
Ya kai yatsa saman lebbanta.
"Shii...Ba kalar godiyarnan nake so, buƙatar fin haka nake. Kar ki manta kuma haƙƙi ne na maki sutura da ma duk abinda bai fi ƙarfina ba wanda zai farantamaki. Kin cancanci fiye da haka."
Ya ƙarashe gami da ɗagamata gira. Kunyar ta nema ta rasa, kawai sai ta juyo gaba ɗaya ta rungumeshi har bayansa na jingina da kujerar. Ya kuwa ba ta kyakkyawan mazauni a kirjinsa, kafin kuma kiɗa ya sauya salo.
***
KANO..
Wutar da ta tashi a wani gida dake unguwar ya sa mutane duk suka fito, cikin dare ne da misalin karfe biyu da mintoci. Banda salati da kokarin kashewa ba abinda ake yi. Da yawa suna aikin kashe ta amma fadi suke don kawa kar wutar ta haɗa da nsu gidajen ne amma banda haka dama sun gaji da Maigidan, bokancin da ya ke yi musu a unguwa yana tare matasa abin ya ɓaci.
Gora kuwa yana daga ciki banda ihu da neman agaji ba abinda ya ke yi, ya rasa ta inda aka yi wuta ta soma cin gidansa, babban abinda ya ƙara haukata shi neman jakar kudadensa da ya yi ya rasa, ga yaronsa ba ya nan. Wannan ya ɗan ankarar da shi cewa cin amanarsa ya yi. Nan fa ya haukace, tun akwai hanyar ficewa har ya zamana ya rasa ta inda zai bi ya tserar da rayuwarsa daga halaka. Haka dai kafin mutane su yi nasarar tsayar da wutarnan, Gora rai ya yi hali.
A ɓangaren yaronsa kuwa har da shi cikin masu kokarin kashe wuta kamar gaske, har ya tafi sai ya yi tunanin gwara ya tsaya ya tabbatar da mutuwar Gora kafin ya gudu, idan kuwa har aka yi rashin sa'a ya tsira, to ya tabbatar duk inda ya shiga a duniya ba zai tsira daga ta'addancin Gora ba. Ganin an fito da Gora a mace ya sanya ya ji wani sanyi a ruhinsa, ajiyar zuciya ya sauke kafin ya hau mashin dinsa ya wuce can filin makaranta inda abokinsa Jabir da suke kira da Jabson ke jiransa su wuce. Yana zuwa suka cafke su na dariya. Nan ya ba shi labarin komai, ya dubeshi da kyau.
"Jakar fa?"
Jabson ya yi wani malalacin murmushi gami da mishi nuni da aji. Ya bubbuga kafadarsa suka dara kafin ya shige gaba zuwa ajin, sai dai shigar ya yi daidai da sokamishi wuƙa a baya ta ɓullo ta ciki, Jabson ne. Sai da ya tabbatar ya kashe shi har lahira sannan ya ɗauki jakar ya tsallakeshi. Mashin dinsa ya haye ya bar wurin a miliyan. Shi da garin Kano kuma sai nan da wasu shekaru.
Misalin ƙarfe sha biyu na rana, labarin ƙonewar Gora da tsintar gawar yaronsa ɗan aikensa Salmanu, ya karaɗe unguwar. Ko'ina maganarsu ake yi, ga Jabir abokin Salmanun da aka nema sama ko ƙasa aka rasa. Dama almajirai ne, wannan yasa aka shiga tunanin ko sace Jabir din aka yi bayan kashe Salmanu. Daidai sadda ake wannan hargitsin, motar Hajiya Zeenatu ta tsaya. Tun kafin su fito cikinsu ya ɗuri ruwa ganin yanda gidan Gora ya zama kango lokaci guda.
"Ke Zeenatu, anya gidan ne?"
Hajiya Zeenatu ta kasa amsawa Hajiya Batool, kokari ta yi kawai ta yi parking suka fito, yaran almajirai na ciki su na ta ɗage-ɗage ko za su yi tsintuwa. Daga ƙasan bishiya wasu samari suka hangosu. Ɗayan ya ce.
"Waɗannan su ne na goma sha takwas kenan, wannan mutumin fa yana wankar mata, yanzu haka ma wani mugun aikin su ka zo ya musu."
Wani ya mike.
"Bari mu je mu ji, idan ma shi suka zo nema mu ba su labari ko Allah zai sa su tsorata da lamarin rayuwa su shiryu."
Ganin haka sauran ma suka mara mishi baya don ba za'a yi babu su ba.
"Hajiya wurin Gora ku ka zo?"
Hajiya Batool da Zeenatu wadanda sun rasa ta ina za su soma, su ka dubi saurayin kusa a tare suka amsa da eh.
"Ayya, ai a daren jiya gobara ta cinye gidansa tas babu abinda ya tsira. Shima ya mutu ɗazunnan aka dawo daga binne abinda aka tsinta na gangar jikinsa. Shima dai yaronsa Salmanu an tsinci gawarsa a filin makarantar Firamare an kashe shi."
Hajiya Zeenatu sai da numfashinta ya bar motsi na wani lokaci kadan, ta kasa magana sai kawai ta ɗora hannu a kai ta fashe da kuka. Jiki na rawa Hajiya Batool ta ce.
"Shikenan Gora ya mutu dai ku ke nufi?"
Suka bisu da kallo kamar taɓaɓɓu, kusan ma duk kalar ruɗewar da sauran matan da suka zo suka yi, bai kai na wadannan Hajiyoyin ba. Mai magana ɗazu ya matso.
"Eh ya mutu. Duk wani mugun aiki da ya ke shukawa ya kare. Ya koma gidan gaskiya inda zai girbi abinda ya shuka din. Kuma ya kamata ku ji tsoron Allah ku tuba daga tafarkin shaidan tun kan lokacinku ya ƙure. Idan har ba so ku ke yi kuma ku zama tarihi ba, ku tafi a wofi."
Hajiya Batool ba ta ce uffan ba balle Hajiya Zeenatu da ke faman kuka, ashariya kawai ta ke narkawa Gora kamar ta mance da cewar ya mutu. Har dai dakyar Hajiya Batool ta maidata mazaunin kusa da direba ita kuma ta tuƙa motar suka bar layin, yara duk an cika ana binsu da kallo.
Haka suk isa gidan Hajiya Batool hankali a matukar tashe. Ita kanta Batool din dakiya kawai ta fi Zeenatu, amma ba ta ga laifinta ba don kuwa ta fi ta zazzage bakin aljihu a wannan harkar. Nutsuwa ta gagaresu, Hajiya Zeenatu kawai zama ta yi kamar kayan wanki a saman kujera tana ci gaba da surfa ruwan bala'i ga Gora da ya jima a gushewa.
"Yanzu shikenan Hussein da Ramlatu haka zan zuba ido ku cigaba da cin amanata?! Shikenan wai hakan na nufin sun yi nasara?! Wallahi ko zan yi yawo tsirara sai na ga bayan Ramlatu da Uwarsa! Sai Hussein ya dawo karkashin ikona. Ba zan dauki wannan dumbin asarar ba! Batool nemomana Maryama a waya! Zuwa Nijar ya kama mu, ya zama dole mu kara gwada aikin Bokansu. Buzaye ne!Za mu yi nasara, za mu yi nasara."
Ta na maganar kamar wacce ta samu taɓin kwakwalwa. Itama Batool ta gane zuwannasu Nijar din kawai shi zai zame musu mafita don haka ba musu ta zaro waya ta dannawa Maryama kira lokaci guda kuma tana sharce gumi. Magana sosai suka yi, ba ta ɓoyemata duka asarorin da ya hau kansu ba. Maryama ta jajanta musu sosai karshe ta ce musu za ta yi musu booking na layin ganin Boka Buzu, kawai dai da zarar sun saka ranar zuwa su fadamata.
"Gobe ma zamu taso jibi mu iso."
Hajiya Batool ta katse ta da gaggawa, ƴar dariya Maryama ta yi kafin ta amsa da toh hadi da musu fatan zuwa lafiya.
Washegari kuwa da sassafe suka kama hanyar Nijar, direba ne ya kaisu. Yardaddan direban Hajiya Batool, Audu. Wannan karon ma sun tattara maƙudan kudade don ita Hajiya Zeenatu ba ta bi ta kan Manajanta ba, ta nemi manyan gwala-gwalanta har biyar ta shiha kasuwa ta siyar. Itama dai Hajiya Batool sai da ta haɗa da siyar da kadara, kowaccensu ta taho cike da burin samun abinda aka je nema. Idanunsu ya rufe, gani suke yi tamkar ga su ga burinsu har ya cika tsabar imanin da suka yi da abinda zai kai su.
Wuraren karfe sha biyun rana da mintoci suka iso Damagaran, anan suka kwana washegari da sassafe suka kama hanyar Niamey. Sun sha tafiya sosai kafin su isa Niamey, kai tsaye suka kira Maryama a waya. Da kwatance da tambaya suka iso katafaren gidanta wanda ya sha kayan alatu. Ta musu kyakkyawar tarba, ba kamar wancan lokacin ba, wannan karon gidanta ne na kanta ba na Maigidanta ba. Tun bayan rasuwar Mijinta ta siya gida inda ta ke harkar safarar yara zuwa Ƙasar faransa da ma wasu ƙasashen yawon bariki. A yanzun da su ke zaune a falon suna cin abinci bayan sun yi wanka, ba tare da kowaccensu ta damu da kallon gabas ba, ƴan mata ne ke safa da marwa cikin shiga mai ƙayatar da masu iri halinsu na bin maza. Babu wacce ba ta fito ta gaida baƙin Madame dinsu ba, a karshe Hajiya Zeenatu ta kora ruwan sanyin da aka ajiyemusu ta dubi Maryama.
"Kin tabbatar dai goben babu fashi a zuwanmu wurinsa ko?"
Wani murmushi Maryama ta yi ta dauki tuffa ta gutsira.
"Haba Hajjaju, zan maki ƙarya ne?"
Ganin haka Hajiya Zeenatu ta saki fuska.
"Ba haka nake nufi ba, kin dai ji komai ai daga bakin Batool, banda haka nan da kike ganina duk sadda zan runtse idanu ba abinda nake haskowa sai Mijina tare da waccan karamar karuwar. Gani nake duk kwana daya tamkar shekara ce."
"Ki sa ranki a inuwa, za ki sha mamakin yanda komai zai lalace. Mijinki ya dawo kamar kwai a hannunki sai yanda ki ka yi da shi."
Dariya suka yi har da cafkewa, nan da nan zuciyoyinsu suka ɗan waske sai dai ko ya ya suka tuna asarar da ta hau kansu na miliyoyi sai sun tsinewa Gora. Basu ma batun nemar masa gafara.
Kamar yanda Hajja Maryama ta fadi, hakan ce ta kasance. Washegari bisa jagorancin yaronta sai dai ba wancan na farkon da ya taɓa yi musu rakiya ba, suka rankaya gidan Bokansu Buzu. Koda suka tsaya babu layi sosai, kamar wani layin asibiti haka aka basu kati karami mai dauke da numero (number). Wannan dai ba ɗayan bane, wani sabon Boka ne gagarumi da Maryama ta tabbatar musu cewa aikinsa wane wancan! Daga yanda ma ake yi a wurin ba ka ganin kalar talauci a wurin ka san harka ce ta manya don kowacce ta sha shadda mai dandasheshan kyau sai kuwa daidaiku masu leshi. Su da suka yi shigar atamfa ma sai suka raina tasu kwalliyar. Ba don komai ba sai don ba su zo da tsadaddun ba na gani a faɗa. Hankalinsu na kan aikinsu.
Sai da layi ya iso kansu suka yi zumbur suka miƙe, ganin su na kokarin shiga tare mai tsaron wurin ya dakatar da su. Cikin Hausarsa da ba ta fita sosai ya dakatar da su.
"Ba'a shiga mutum biyu komai kusanci."
Jin haka suka dubi juna jin abin banbarakwai wai namiji da suna Hajara. Ba su taɓa zuwa an musu iyaka da shiga wurin Boka tare ba, karshe dai ganin mutumin na harararsu ya sa Hajiya Batool ta ja baya.
"Soma shiga bari na yi jira."
Hajiya Zeenatu ta shige ita kuma ta koma ta zauna.
Kwarjini iyakar kwarjini mai bada tsoro shi ta gani a fuskar wanda aka kira da Gamsheƙa, fuskarsa babu ɗigon walwalwa. Tana zama babu tambaya ya nemi sanin sunanta kawai kafin ya soma motsa wasu irin ƙaho da duwatsu da ke cikin wani ƙaton abu kamar tire kamar kuma ba shi ba. Sai da ya gama ya dubeta ya shiga kora jawabi.
"Mijinki da kika yiwa asiri mai suna Husseini, ya dawo hayyacinsa ya sake ki, ya kuma auri wacce a duniya kika tsana, kuma burinki bai wuce na ganin kin hallakata ba. Sai dai kuma ki sani, tuni kin makara don soyayyarsu babu karfin shaiɗancin da zai iya hallakata. Amma ina mai tabbatarmaki juya tunaninsa abu ne mai sauki idan kin aikata duk abinda za mu sanya ki babu musu."
Hajiya Zeenatu wacce idanunta ya rufe nan da nan ta hau gyada kai tamkar ƙadangaruwa.
"Wallahi a shirye nake, ko menene zan aikata idan har burina zai samu cika."
Ya jinjina kai da yin murmushi mai kama da na mai jin kashi.
"Shikenan, a yanzu za sadu da ke ta gaba da kuma baya, daga karshe zan ɗebi abinda ya fita daga jikinki na najasa na haɗamaki wani ƙullin magani wanda za ki tabbatar kin yi yanda ki ka yi, kin fesa a fuskarsa. Sai kuma wani tulu da zan ba ki wanda ke dauke da zucciyar mutum soke da allurai, shi ne mafi hatsari cikin ayyukan da zan maki. Kar ki kusa ki bari ya fashe, muddin ya fashe ki sani komai zai iya faruwa da ke, wannan hukuncin ya rage ga aljanun da suka satomin zucciyar. Don haka kin yarda kin amince za ki iya?"
Hajiya Zeenatu wacce tun sadda ya yi batun saduwa ta baya ta yi turus, kirjinta ya shiga dukan tara-tara, abu ne da ba ta taɓa aikatawa ba, bar ta dai da aikata zina shima a baya ne kafin shigowar jarumi kuma namijin duniya Hussein rayuwarta. Daga shi babu waki namiji da ta ƙara yiwa kallon abin marmari.
'Ki tuna fa, wannan namijin kike kwaɗayin maidoshi rayuwarki yanzu Zeenat, kada ki yi sake. Wannan ce kadai mafita.'
Wani ɓangare na zuciyarta ta mata tuni, nan da nan ta dubi Gamsheƙa da har ya soma gundira da shirunta.
"Na amince. Zan kiyaye dukkan sharuɗa."
Ya miƙe tsaye ya ba ta umarnin ta biyoshi. Daga haka ya nufi uwar ɗaga bayan sakin labulen window, hakan ya sa Maitsaron ya fahimci shugabannasa ya shiga aiki. Wannan yasa bai yi gigin lekawa ba.
Sun kwashe kusan fiye da awa ana abu ɗaya don Gamsheƙa dai ya samu ya da yake so, a karshe ya fito ya bar Hajiya Zeenatu da ɗibar abinda ya umarceta a kwalba sannan ta mike ta fada bandaki ta dauraye jiki ta fito. Koda ta dawo ta iskeshi har sannan ba walwala kamar ba shi ne ya gama kukan mage ba.
Gani ta yi ya haɗamata komai ya miƙamata sannan aka yi bayanin kudade ta biyashi da kudin Ƙasar don tun a Damagaran suka yi chanji.
Koda ta fito mai tsaron ya ba Hajiya Batool damar shiga, ita kuma ya ce ta fice don baa kara zama idan an fito, hakan laifi ne babba. A gaggauce ta fita, yaron Maryama zai karbi tulun hannunta dake cikin kwali ta yi saurin dakatar da shi ta ce ya bar shi. Don ji ta ke idan har ba ita ce ta riƙe ba to fa komai zai iya faruwa. Duk fargaba ta cika zuciyarta.
Tana nan zaune a motar har kusan shudewar awa guda kafin Hajiya Batool ta karaso, ita har da hawayenta ma don ita kadai ta san me ta ke ji a bayanta tun abinda ya gudana tsakaninta da Gamsheƙa. Hajiya Zeenatu ta kalleta kawai don ta san duk kanwar ja ce. Ita ba tulu sai wani kwalba a cikin kwali, ba su ba junansu labari ba sakamakon ba su daya ne a motar ba, haka suka kama hanyar gidan Maryama kowannensu da abinda ya ke saƙawa. Kamar yanda kowanne ke tunanin bala'in da zai sameshi idan har suka yi gangancin ɓata aikinsu.
***
ADAMAWA
Kwanakin da suka biyo baya, banda soyayya ba abinda Hussein da Ramlat ke gurza, gaba dayansu sun sauya sun kara wani fresh da kyau. Hafsat ba ta bar aron wayar Ramlat a faƙaice ba tana gaisawa da Tahir. Ita dai Ramlat a tsorace take da hakan sai dai ganin Hussein bai taɓa kamata da laifin ba yasa ta ɗan ji nutsuwa kaɗan.
Ranar da ta cika sati ɗaya cif a garin Adamawa, tana zaune a falonta, dawowarta kenan daga sashin Dada. Hussein ya shigo fuskarsa kaɗai ka kalla za ka san yana cike da tsantsar farin ciki. Hannu kawai ya waremata ba musu ta ƙarasa ta rungumeshi. Ya kuwa ɗagata cak yana juyi da ita, dariya ta yi bayan ya sauketa ƙasa yana nishi da riƙe ƙugu.
"Heart, kin fa ƙara nauyi."
Ta turo baki irin na shagwaɓaɓɓun yara, ya yi murmushi da jan karan