Showing 231001 words to 231786 words out of 231786 words

Chapter 78 - KARFEN KAFA Book 1 COMPLETE (By Rufaida Umar).txt

A rikice ya karasa su ma suka faɗa jikinsa, ya rungumesu sosai.


"Ya isa my twins, wa ta taɓa ku?"


Suka hau nuna ɗaki.


"Mamiiii" Amina ta faɗi tana kuka da taɓe pink lips dinta. Ya miƙe ransa a ɓace ya shiga ɗakin. Sai dai ganinta a kwance tana hawaye ya sanyaya jikinsa, duban yaransa ya yi ya kuma dubeta, bai ce komai ba kawai ya kama hannunsu suka bar ɗakin. Sai da ya rarrashe su ya basu kayan cakulet din da ya siyomusu ya ga sai washe baki suke da dariya kafin ya sumbaci kowannensu ya mike zuwa ɗakin.


Gadon ya hau ya shafi gefen fuskarta. Ta dubeshi don tuni ta bar hawayen.


"Sannu da zuwa."


Cike da kulawa ya ce.


"Meke damunki? Kukan me kike?"


Ta mike zaune ta fada kirjinsa.


"Ciki ne da ni."


Ya yi murmushi.


"Shi ne ki ke kuka saboda ba kya son haihuwa da ni ko me?"


Da sauri ta ɗago ta girgiza kai.


"Wallahi aa, kawai dai tausayin kaina naji, duka-duka twins ko shekara biyu ba su cika ba."


Ya ɗaga rigarta ya sumbaci cikin kafin ya ɗago ya sumbaci lips dinta yana murmushi.


"Shi ne me? Tun yaushe nake maki fatan samun cikin? Ina ce har zargin ko kima shan maganin hana ɗaukar ciki nayi maki? Ba halak za ki haifarmin ba? Ramlat ko yara goma za ki haifamin akai-akai, wallahi ina son abina. Ashe dalilin da yasa kika huce akam yarana kenan? To ki shirya dagaske sai na rama musu."


Ta harareshi da wasa, ya ɗan ba ta mintsili kuwa a kafaɗa. Ta rike tana kuka shagwaɓa gami da fadin wash.


Haka ya dinga lallaɓata kafin ya jawo ta jikinsa.


"Akwai goron albishir babba, yana nan tafe nan da wata uku."


Ta yi farr da idanunta.


"Watan Azumi fa kenan."


Ya jinjina kai yana murmushi.


***
BAYAN WATANNI UKU..


Kamar yanda ya yi mata alƙawari sai ga shi ta sha mamaki, ashe dama dalilin yi nata Passport kenan? Tafiya ce Umarah za su yi, don murna ranar haka ta rukunkumeshi tana kuka tana sumbatar duk inda bakinta ya kai. Tare da Dada da su AlHassan da matarsa duka za su wuce. A waya suka yi bankwana da mutan Kano da zummar sai sun dawo za ta kai ziyara.


Azumi nada kwanaki goma sha biyar suka tafi. Sosai sun yi ibada. Anan ne kuma Ramlat ta ƙara zuwar ma da Hussein roƙo akan ya yafewa Hajiya Zeenatu, da murmushi ya rungume matarsa ya sumbaci goshinta.


"Na yafemata, Allah Ya yafemata."


Ramlat ta rungumeshi itama da jin dadi.


Koda suka koma ɗaki, kasancewar ƴan biyu na tare da Dada, wata ibadar suka shiga yi. Bayan komai ya kammala ya zubamata idanu sadda ta fito wanka tana goge jiki, garin na Makkah ya karɓe ta sosai, ga cikinta ya fito. Ta kara mulmulewa ga kumatu da suka yi mata kyau. Ƙarasawa ta yi ta yi amfani da jelar gashinta ta watsamishi ruwa a fuska, ya kai hannu zai riƙota ta ja baya. Girgiza kai ya yi gami da sauke numfashi.


"Wallahi ina sonki."


Yanda ya fadi sai da ya ratsa dukkan sassan jikinta, tsikar jikinta ya mike. Ba ta san sadda ta taka zuwa gareshi ba ya kuwa rungumeta sosai suka lumshe idanu. Ji suke kamar su haɗiyi juna.


"Ina maka son a baki ba zai misalta ba My Hussein, Abban Twins. Na soma sonka daga sadda na soma ganinka."


Ya ɗago ya haɗa fuskokinsu wuri guda, maimakon amsa, sai ya haɗa bakunansu. Can kuma ya ɗago kai ya dubeta.


"Sai dai fa a sake sabon.."


Ba ta bari ya karasa ba ta rufemishi bakin da nata. Gaba daya ta ruɗa shi. Ta sakeshi tana murmushi da maida numfashi.


"Na shirya yin duk abinda zai farantamaka."


Daga haka ya sa hannu ya ƙara kashe fitilun ɗakin ta hanyar amfani da makunnin dake gefen gadon. Salo ya sauya.






ƘARSHE..


_*Alhamdulillah. Ina godiya ga Allah da Ya nunan kammala littafin Karfen Kafa lafiya. Ina kuma godiya gareku masoya masu karfafan gwuiwa da kuma hakuri da juriyar bibiyar labarina duk da irin tsaikon da akan samu. Ina kara ba ku hakuri bisa duk wani kuskure da ku ka ci karo da shi, dan adam ajizi ne. Ina maraba da kofofin gyara ko shawara amma don Allah ba ta hanyar cin fuska ba. Allah Ya kara haɗamu a wani littafin nawa. Na gode kwarai. Son so fisabilillah mutan Rof, Rof2, Karfen Kafa group, both whatsapp & Wattpad fans duka ina godiya. Allah Ya bar zumunci.*_


_*Godiya Ta Musamman gareki BARR FIRDAUSI KABIR, wallahi ina maki son so fisabilillah. Kaunar da kike yimin ba zan ce komai ba gareki tare da sister dinmu, FADILA KABIR. Allah Ya bar zumunci.*_


_*Ummu Abdoul my editer, chairlady of Fikra. Allah Ya saka da khairan, Sis Batool Mamman, Donutfairy da ma dukkan masu bibiyar Karfen Kafa marubuta. Ina maku son so. Allah Ya bar zumunci. Ameen.*_

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login