Showing 150001 words to 153000 words out of 231786 words

Chapter 51 - KARFEN KAFA Book 1 COMPLETE (By Rufaida Umar).txt

a sake.


"Sai dai kamar ban shaida fuskar ba."


Murmushi Ramlat ta yi.


"Eh gaskiya ba ki san ni ba Anti. Sunana Ramlat Khalid Mu'azzam. Kusan sanadin AlHassan Aminu Mamman dake Adamawa na san gidannan. Kwanakin baya ma sun zo biki nan suka biya ta gidanmu."


Kawai sai ta ga Rasheeda ta sa dariya haka Amarya.


"Ke ce Mamin Fatima ko? Mai zaɓamata takalmi? Ya bamu labari."


Da wani irin salama na jin dadin kalaman Rasheeda itama ta yi dariyar kadan.


"Ni ce, ai kema ina ganinki na shaidaki don ina yawan ganin hotonki a status din Hafsat."


Jin haka Amarya sai ta samu nutsuwa sosai da Ramlat, dama tun farko ba ta yi mata kalar mace marar kamun kai ba. Nan aka kara gaisawa da tambayar su Hajiya wanda ba karamin mamaki ya ba Ramlat ba. A karshe Ramlat ta gangaro kan abinda ya kawo ta.


"Ina neman izni ne, ina son ganin Kawu Modibbo."


Jin haka Anti Amarya ta amsa cikin kwarin gwuiwa.


"Wannan ba matsala ba ce Ramlat. Bari na yi miki iso, ina zuwa."


Hakan ya faranta ran Ramlat, ta dauka ganinnasa zai mata wuya ko kuma wani ko wata zai nemi sanin dalilinta na son ganinsa, sai dai akasin hakan ce ta faru. Ko ba komai ta gaskata kirki na Amarya, wanda ya sha bamban da na Hajja Fatuma kamar yanda ta ɗan ji kaɗan cikin labarin matannasa a bakin Hafsat. Yarinyar akwai hira idan ta so.


Jim kaɗan sai ga Amarya ta dawo, yanayin sanyin jikinta sai ya sa Ramlat shan jinin jikinta itama. Amarya ta daure tana murmushi mai kama da yaƙe.


"Za ki iya jira har bayan Magriba kuwa? Ina gudun kar ki dare."


Nan ta gano matsalar, don haka ta saki fuska.


"Lah ba komai Anti, Allah Ya kaimu."


Amarya ta yi murna da hakan, ta kunnamata kallo ta ba ta remote koda za ta sauya tasha daga nan ita kuma ta koma bakin aiki kasancewar girkinta ne. Ba jimawa da kunna kallon aka dauke wuta, nan take jin Amarya na ba Rasheeda labarin wai Hajja Fatuma ce ta ce tunda ba lokacinta ba ne sai ta yi hakuri da duk wani baƙonta da ke son ganin Modibbo, idan na ta lokacin ya shigo ta yi duk irin damun da ta so yiwa furarta.


Murmushi Ramlat ta yi na yaƙe, ta dai lura akwai takun saƙa tsakanin matan gida. Waya ta fiddo ta kira Hajiya ta fadamata.


"Anya kya zaunar musu har Magriba? Ba kya dawo ba ki hakura zuwa gobe?"


Girgiza kai Ramlat ta yi.


"Hajiya lokaci zai ƙuremin idan ya kai gobe, mu dai yi hakuri tunda kinga biyar da rabi ma ta wuce, kamar yanzu ne za'a kira sallar in sha Allah."


"Ai shikenan, Allah Ya kaimu anjima. Sai kin dawo."


Ta amsa da amin suka yi sallama. Ba ta kai ga ajiye wayar ba, kiran AlHassan ya shigo. Suka gaisa.


"Dole ta tsayar da ni a Gombe sakamakon lalacewar abin hawa. Na so kwarai na shigo yau, amma gobe da sassafe in sha Allahu zan taso."


Hakan ya dan yiwa Ramlat dadi, ko ba komai lamuran zasu tafi yanda ta so.


"Ayya ba komai, Allah Yasa hakan ya zama alheri."


"Amin, sai dai kin ƙi sanar da ni komai game da abinda na nema."


Sauke ajiyar zuciya ta yi.


"Ka yi hakuri, idan ka shigo har wanda zai ba ka mamaki duk zan faɗamaka kuma zan kaika ka ganewa idonka in sha Allahu."


Ya dan yi shiru, shirun da yasa Hussein faɗomata a rai, shi ya saba yi mata hakan. Kewar Hussein sosai ta ke ji ta kuma kudurce ko bai mata magana ba ita kam yau za ta taɓoshi ta whatsapp.


"Shikenan. Allah Ya jisshemu alheri."


Ta amsa da amin cike da tausayinsa. Dan uwan da Allah kadai yasan tun sadda ya ke bulayin neman ɗan uwansa. Ta ji idanunta sun cika da kwalla daidai sadda suka yi sallama. Ta shiga whatsapp ta aikawa Hussein saƙo, ta jima tana kallon profile dinsa wanda bai dora komai ba a idanunta tana wassafo hotonsa, karshe ta sauka.
Ba jimawa aka shiga kiraye-kirayen sallah, Rasheedat ta jagorance ta zuwa ɗakinta. Alwala ta ɗaura ta tayar da sallah saman dardumar da ta iske an shimfidamata.


Ta jima tana addu'ar nasara akan lamarin Hussein, shi kansa ta yi mishi addu'a kwarai kafin ta shafa ta miƙe.
Abinci aka zubomata, dolenta ta ci tana kallon tsarin yaran Amarya gwanin sha'awa. An idar da sallah ana kuma neman haddar karatun da aka biya na Islamiyya. Can kuma sai ga Amaryar ta fito sharr kamar sabuwa, ta shirya cikin riga da siket na leshi ta cakare abinta tsaf. Da fara'arta ta dubi Ramlat.


"Yi hakuri fa Ramlatu, bari idan na shiga zan miki magana sai ki zo."


"Toh Anti. Kin yi kyau tubarakAllah."


Hakan da ta fada ya ba su dariya har yaran. Amarya ta yi godiya ta wuce ɓangaren Mijinta. Sosai abin ya ƙayatar da Ramlat.


***
Taimakon gaggawa likitocin suka shiga ba Hussein har Allah Yasa ya dawo hayyacinsa. Hajiya Zeenatu ta rasa sukuni, banda safa da marwa babu abinda ta ke yi a harabar bakin kofar dakin da Hussein ke kwance. Can ɗaya daga cikin likitocin ya fito, da hanzari har mayafin na sulalewa ta ƙarasa.


"Dakta ya farfado?"


Daktan ya yi murmushi gami da gyara zaman gilashinsa.


"Alhamdulillah Hajiya, ɗanki ya farfaɗo, ki kwantar da hankalinki."


Ta tamke fuska.


"Mijina ne."


Mamaki karara a fuskar likitan kafin kuma ya haɗiye don ba abinda ya shafeshi ba ne.


"Ok, idan ba damuwa ki biyo ni zuwa ofis."


Daga haka ya yi gaba.


"Matsalar Hussein damuwa ce da ta haddasa masa ciwon kai mai tsanani. Sai jininsa da ya hau, sai kin kula sosai da cimarsa har ma da walwalarsa domin irin ciwonsa na bukatar kulawa kuma ba ya son yawan tunani."


Hajiya Zeenat ta yi shiru a ranta tana jin takaicin Hussein da zai sa damuwar wani abu bayan ita ce duniyarsa.


"Kin ji abinda na ce?"


Tambayar ta katse tunaninta. Ajiyar zuciya ta saki.


"Naji kuma zan kiyaye. Yanzu ina iya ganinsa?"


Likita na ƙaremata kallo ya gyada kai.


"Eh Hajjaju."


Ta mike tana watsa masa kallo mai kama da harara, ba shiri ya janye idanunsa tunda ya san shi ya jaza wa kansa da ya bita da kallon kurilla. Ba kuma don sha'awa ba, sai don ya ga abinda ya kwaɗaitar da mara lafiyarsu da ta kira da Hussein har ya ji ita ya ke da muradin zama abokiyar rayuwarsa.


"Su ta shafa." Ya ƙarƙare tunanin ta hanyar furta hakan a fili.


Hajiya Zeenatu ta shiga ɗakin da Hussein yake, wannan karon babu kowa sai shi ɗaya. Idanunsa a lumshe, a farko ta yi zaton bacci ya ke, sai dai rufe ƙofar da ta yi yasa shi kallonta. Ta sakarmasa murmushi tana mai ƙarasowa ta zauna gefen gadon ta kama hannunsa.


"Sannu Hussein, ya jikin?"


Gyadamata kai kawai ya yi ya kara kauda kansa.


"Ba zan kwana a nan ba, su sallame mu."


Yanda ya yi zancen ka san iyakar gaskiyar kenan ba wasa. Cikin rarrashi ta shigo kokarin fahimtar da shi kuskuren hakan, sai dai yanda ta kafe haka ya kafe har abin ya tsorata ta. Aikuwa dai karshe sai sallamar aka ba su da lodin mgunguna bayan an ƙara jaddada masa akan ya kula sosai da jikinsa.


Su na komawa gida ma'aikatan suka tarbeshi tare da yi mishi sannu.


"Dalla Malamai ku matsa! Ba kwa ganin yanayin jikinsa ne?"


Hussein ya dubi Hajiya Zeenat, a fuskarsa ta gane bai ji dadin abinda ta yi ba. Ya tsaya ya amsa gaisuwarsu ita kuwa ta yi gaba tana tsaki. Godiya ya yi musu san nan ya shige ya bar su da gulmarta.

Sallar Magriba ya soma yi san nan ya shiga wanka. Yana fitowa ya kimtsa, Hajiya Zeenatu kuwa tana ƙasa ta na bada umarnin abinda za'a girkawa mijinnata.


Ya dauki wayarsa, ya ga missedcalls din Hisham sai kuma na wani abokin aikinsa. Data ya kunna ya leƙa whatsapp. Shiru ya yi ya ƙurawa sunanta idanu yana kallon saƙon da ta aiko ba tare da ya buɗe ba, ya hangi dai sallama da gaisuwa, sauran ne bai da masaniya. A hankali aka zare wayar daga hannunsa. Hajiya Zeenatu ce, gabansa ya faɗi.

"Haba Yallaɓai, yaushe ma ka farfaɗo da za ka ɗauki waya? Ba dai ka manta sharuɗɗan Dakta ba?"


Ta ƙarashe tana duban wayar, tuni ta shiga key, shima yanda ta ke kallo haka ya ke kalla, ganin ta rufe ya sanya shi sauke ajiyar zuciya. Gaba daya ta kashe wayar tana mai duban soyayy duk a kokarinta na gudun kar ya sauya shawarar da ta kawomasa a ɗazun.


"Wayar a hakura a bar ta zuwa gobe. Yanzu mu je ƙasa ka jira abinci sai ka sha magani."


Ta faɗi gami da riƙe hannunsa. Ya ciji leɓɓansa, haka nan ya ji bai kyauta ba bisa rashin ba da amsa ga Ramlat sai dai maganganun Hisham na faɗomasa a rai sai ya yi gaggawar fidda tunanin.


***
Mintuna kusan goma sha biyar sai ga kiran Amarya a wayar Rasheedat.


"Muje na yi miki rakiya."


Haka kawai Ramlat ta ji faɗuwar gaba, ta amsa da toh tana mai haɗiyar yawu mai ɗaci.


Da sallamarta ta sa ƙafa a falon. Dattijo cikin shigar kamala, kana ganinsa ka ga cikakken bafulatani. Tundata shigo yake yiwa fuskarta kallon tsanaki don son tantance ko akwai inda ya santa ko kuwa yau ne farkon ganinsa da ita. Ta karasa ta gaishe shi, Amarya tuni ta mike zuwa ɗaki. Hakan kan faru, idan har Modibbo nada baƙo, sukan ba shi wuri ya gana da ita.


"Baiwar Allah daga ina?"


Ya tambaya cikin hausarsa da har sannan ba ta ginu kamar ta Bahaushe ba.


Ta hadiyi miyau gami da ambaton Allah. Ta gabatar da kanta sannan ta ɗora bayan ya shaidamata eh ya san Malam Abdullahi kakanta kuma ɗan unguwar da yake, Yakasai.


"Kawu dama magana ce da ta danganci Hussein, dan uwan AlHassan da ake nema."


Shiru-shiru, ba ta ji ya ce uffan ba don haka ta ɗago kai. Yanayin dake shimfiɗe a fuskarsa ya tsorata ta, ya kuma kaɗa hanjin cikinta.


"Kina da labarinsa? Ke wace ce?"


Wannan ne tambayoyin da ta samu da suka ƙara cilla ta a kogin tunani da mamaki.










I just published "BABI NA ARBA'IN DA BIYAR" of my story "Ƙarfen Ƙafa". https://my.w.tt/gqyFr6qwCcb








🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️


_*Rufaida Umar*_


Bismillahir Rahmaanir Raheem.


45)


ALLURA TA TONO GARMA...






"Kurma ki ka koma?"


Ta dawo hayyacinta ta kalle shi gami da girgiza kai. To me za ta ce bayan ta gabatarmasa da kanta?


"Ina gargaɗinki da ki cire kanki a abinda bai shafeki ba. Idan kina son tsira da lafiyar kwakwalwa da na gangar jikinki ki fita hanyar Hussein da Zeenatu."


Da wani irin razana ta dubeshi, wannan ƴar fara'ar dama tun soma labarin ya kauda ita a saman fuskarsa sai ya zama kamar wani Mugyambo a idanunta. Kwallar da ta cika kurmin idanun suka soma sharara.


"Ka...ka..san Hussein yana nan? Ban ambaci Zeenatu ba, ka san..."


"Ke Bingel! (Yarinya). Ke wacece da za ki tuhume ni? Ina gargadinki karo na biyu kuma na ƙarshe ki tashi ki binne maganarnan a nan wurin da kike zaune. Idan ba ki ƙi ji ba, ba kya ƙi gani ba. Duk abinda ya faru gareki sanadin fasa wannan zancen, ki yi kuka da kanki!"


Ramlat kirjinta na bugu, hawayenta na kwaranya, kwakwalwar ta tsaya cak ta bar aiki. Ta kasa haɗa kowane lissafi, jin ta take yi kamar ba'a duniyar mutane ba. Kamar wata duniyar ta daban ta ke ciki mai tsananin ruɗani da azaba. Kallonsa ta ƙara yi, girman tuni ya zube ƙasa warwas! Kallo ne kamar wacce ke zaune gaban sa'anta.


"Ka na da hannu a komai? Ka na a ɓatar da Hussein daga zuri'arku? Me ya yi maka haka da zafi?"


"Kina ƙara dulmiyar da kanki cikin tafkin nadama da da na sani, kalaman da kike yi za su rushe duk wani farin ciki na rayuwarki. Ki kama kanki! Ki tashi ki bar min gida tun kina da sauran lafiyar aikata hakan!"


Miƙewa ta yi a sanyaye, har za ta fice ta juyo ta dubeshi yana faman muzurai. Dattijon da bai kama daraja da girmansa ba, babu amfanin ganin ƙimarsa.


"Kawu ka sani, Allah na bayan masu gaskiya. Ƙarya fure ta ke ba ta ƴaƴa."


Daga nan ta bankaɗa labule ta fice, ba ta jin za ta iya jiran yin sallama da Amarya. Babu inda ta ƙara shiga a gidan haka ta fice tana hawaye.


Tafiya ta ke ƙafafun na harharɗewa, kalaman Kawu daki-daki ta ke tunawa tana ƙarin fahimtar dagaske dai akwai hannunsa a cikin ɓatan Hussein.


"Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un!"


Ta ambata a fili, tausayi sosai da wata irin ƙauna ta Hussein ya ƙara mamaye zuciyarta. Ji ta ke komai za ta iya aikatawa muddin hakan zai dawo da Hussein cikin ƴan uwansa. Wayarta ta yi ƙara, Hajiya ce. Yanda ta ke kuka ba ta jin za ta iya amsawa, don haka ta mayar da wayar jaka. Kafin ta bar lungun sai da ta tsaya ta saita kanta ta share fuska. Abin hawa ta tsayar ta faɗa.
"Malama ba ki faɗi inda zan kai ki ba."


Ta haɗiyi miyau. Dakyar ta faɗi sunan unguwar ta yi shiru, kanta ke sarawa ga wani zazzaɓi-zazzaɓi.


***


Tsam! Modibbo ya miƙe ya shiga ɗaki, Amarya na zaune na kallon wani ƙaramin bidiyo na Ibro tana dariya, ganin mutum ya faɗo ba sallama ya sa ta ɗan razana kafin ta sauke ajiyar zuciya. Tun kafin ta nemi ba'asi ya katsemata hanzari.


"Fita zan yi, ki je kawai idan na dawo zan kiraki. Akwai uzurin da zan gabatar."


Ya faɗi a kausashe, ta miƙe jikinta a sanyaye ta fita fuskar cike taf da tarin tambayoyin da babu mai amsa mata sai Ramlatu. Sai dai sama ko ƙasa babu ita, hatta su Rasheeda sun yi mamakin da ba ta biyo ta musu sallama ba.


Fitar Amarya ya ba Kawu Modibbo damar buɗe sif ɗinsa ta kaya, can ƙasan ya zura hannu ya ɗauko wani ɗan akwati mai girma da duk faɗin gidan babu wanda ya isa ya taɓa. Hankalin ma bai kai gareshi ba. Cikin rigarsa ya zaro mukullin da ba ya rabo da shi a jikinsa, ya buɗe, kwakwalwa ce! Kwakwalwa ta ƊAN ADAM! Ta yi baƙiƙirin a madadin jan da ta ke da shi har da jini-jini a shekaru masu yawa. Idanun Kawu Modibbo suka kaɗa.


"Ita ce! Ita ce yarinyar!"


Abinda ya faɗi kenan a fili kafin hannu na rawa ya maida ya rufe. Gumi ya shiga tsastsafowa daga fatar jikinsa. Ya sa hannu ya share. Tun komai bai ƙarasa lalacewa ba zai yiwa abin tufka. Ya ayyana hakan a ransa yana jin tsanar Hussein tsagwaronsa a fili da ɓoye. Miƙewa ya yi ya dauki waya ya danna kira direbansa.


"Kana ina?"


Daga can aka ba shi amsa kafin ya dora.


"Ka fiddo mota, fita zamu yi."


Daga nan a gaggauce ya dauki hula ya rufe kansa ya fita yana zuba sauri.





***
Ramlat bakinta ya yi mata nauyi, ta kasa ba Hajiya labarin abinda ya faru. Damuwar da ke kwance samam fuskarta yasa Hajiya ta fahimci ba lafiya. Ganin ta shige daki sai ta mara mata baya.


"Ke mene ne wai? Shi Kawun ne ba ki samu gani ba ko wani abin ne ya faru da Husseinin?"


Girgiza kai ta yi. Tunanin ta faɗa ɗin ya rinjayi komai, ko ba komai Hussein na bukatar addu'a, don haka ta karya bille ta labartamata duk yanda suka yi da Kawun. Hajiya ta saki salati.


"Ni Rabi wannan rayuwa da ban mamaki. Ban taɓa jin labari makamancin haka ba tunda uwata ta haifeni. Kai.."


Hajiya sai ta soma hawaye, ita kanta tausayin Hussein ke ɗawainiya da ita. Hatta da abokin haihuwartasa ma tausayinsa take ji. Miƙewa ta yi tana jan hanci.


"Addu'a zamu dage da yi, ke kanki yanzu ki dage da addu'a don mutum idan aka ce mugu ne komai ma zai aikata. Bari na kira Malam na faɗamasa, shima ya tayamu da addu'a."


Daga nan Hajiya ta fita ta bar Ramlat da tarin damuwa. Dakyar ta iya mikewa ta ɗauro alwala ta gabatar da sallar isha'i, zaman dirshan ta yi saman dardumar jefi-jefi tana sharar hawaye.


Addu'a sosai ta yi kafin ta miƙe ta nufi gefen gado ta zauna. Hayaniyar su Affan ta ishe ta don haka ta kora su waje. Waya ta ɗauka ta hau kan whatsapp, babu alamar Hussein ya hau. Yau ɗaya ta ɗaura ɗamarar kiransa. Don haka ta sauka ta danna masa kira. Wayar a kashe. Damuwarta madadin ta ragu sai ta ƙaru, ganin dukan na nema ya yi mata yawa, sai ta miƙe ta koma falo ta yi jugum. Ba jimawa Hisham ya kirata. Ta ɗaga.


"Antinmu shiru, ina jira na ji yanda ku ka yi."


Ta haɗiye hawayenta da ɓacin rai. Komai ba ta ɓoyewa Hisham ba, ya dinga salati da salallami karshe dai ya kwantar mata da hankali.


"Kar ki sanya damuwa a ranki Ramlat, in sha Allah kamar yanda kika ce toh hakan ne, Allah Ya fi su. Mu dage da addu'a."


Ta amsa da toh. Kamar ta tambayeshi ko sun yi waya da Hussein sai ta share.


***
Washegari haka ta shirya ta fita wurin aiki ranta a jagule. Ga wayar Hussein da ke a kashe. Ta gwada kira har cikin dare don tsautsayi amma ba ta shiga. Tuƙi ta ke kusan ba za ta ce a cikin hayyaci ba. Don haka ba ta kawo da cewar an basu hannu ba sai da ta ji wani ruɗaɗɗen Hon daga bayanta. Hakan ya fusata ta, ta madubi ta ke duban mai shi. Ido da ido suka kalli juna, yana cin magani. Wannan karon ba Tinted glass din a motar da yake. Yanda ya ɗaure fuska ba alamun fara'a ya fi komai ruguza lissafinta. Asalima ba wani wawan overtaking da ya yi ya kaɗa hancin motarsa sai da ya daskarar da ita ya jazamata ɗaukewar numfashi na ƴan dakiku.


"Me nayi masa?" Ta ambata a fili, da rawar jiki ta ja motar bayan ta gaji da tsinuwa da zagin mutanen da hankalinta ba'a kansu yake ba. Koda ta gangara sai ta nemi wuri ta tsayar da motar. Hankalinta ya gushe na ɗan lokaci. Tunaninta abinda ta yiwa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login