Showing 36001 words to 39000 words out of 182942 words

Chapter 13 - NAJEEB COMPLETE BOOK Document writing Maryam Obama.txt

Mai shiga waje daban daban yana bukatar mace Mai ilimi,"babu wanda zai yarda ya auri wannan matar Mai kama da monkey a matsayin mata


Mum shuru tayi, maganan yaron Nata duk da akwai rashin kunya babu da'a a ciki, amma ya fad'i gaskiya, "bai kamata a aura mishi wacce batai boko dinba, duk da tayi na addini, toh amma yata iya, tunda mijin Nata ya ku'ke ya kuma dage akai, kota bashi shawara baji zaiyi ba, kuma tasan indai aka d'aura auren kaman yanda Najeeb yace Wlh zai aikata sakinta zaiyi, tunda taga baya shakkan kowa balle yaji maganan mutane.


Najeeb yace Mum nidai gobe zan wuce, in kuna bukatar dole sai kun ban mata sai kuban dai dai ni, balle bana bukatar a zaba min matar dazan aura, ni dakai na zan zaba, "basai Kun zaba min ba, "inada idon da zan Zaba matar dazan aura dakai na, so Please kuban sometime zan Kawo wacce nakeso, in aura, yana fad'in haka yayi waje yana fad'in gobe zan wuce


Mum shuru tayi, ita yanzu abun yafi karfinta, "Toh maiya kamata tayi yanzu? " Hmmm Gaskiya Najeeb yana bukatar mace Mai ilimin addini dana boko, duka"maganan dan nata hakane, "amma zataja bakinta tayi shuru, yanzu in tayi magana sai a Mata wani Fassaran, sai mijin Nata yaga kaman ita ke zuga shi, inta nuna itama abar maganan auren.


Karfe 9 dai dai duka iyalan gidan suna zaune akan dinning suna cin abinci, amma banda Granny dake zaune akan kujeran falon, sai Najeeb da baya wajan shima


Najeeb fitowa yayi daka d'akinsa, kai tsaye dinning ya nufa, gaida Dad d'inshi yayi tare da zama, Granny tace yaro dai kwanan nan zaka koya fulatanci inka aura Hanne..


Najeeb hararan Granny yayi domin yasan dashi take dan yaga idonta na kanshi


Tace ai ban San ka iya harara ba sai naga idon a k'asa miskili kawai, mummuna.


Zarah ta kwashe da dariya tare da fad'in kai Granny, kuma fah dake yake Kama


Tace wa?


Badai dani ba, wannan mummunan yaron mai miskilanci, ni ban son namiji kyakyawa da yawa wlh, in kyau yama mutum yawa sai kiga yayi muni.


Dariya Zarah ta saki, Sosai


Ita kam ibtisam ko magana batai ba, dan haushin Najeeb take Sosai, domin har yanzu hannunta bai daina Mata zafi ba, "ita gaba d'aya bata son taji ko maganan shi anayi ma.


Najeeb kam wayarshi ce ta Fara K'ara, d'auka yayi yaga Gina ce, yace I will call you back tare da kashe wayan.


Ibtisam kam tsaki tayi mara sauti, karaf a idon Najeeb, wani irin kallon tsana yayi mata, kwata kwata baya son yarinyar nan, bata da kunya da wani mummunar fuskanta.


Ibtisam ganin irin kallon da yayi mata yasa itama ta galla mishi harara tare da tashi tabar wajan ma, "Najeeb ji yayi kaman ya janyota ya mareta but Koba yanzu ba I will teach her a lesson, saina cire mata hannunta da taji ciwo idiot.


Dad yace maganan tafiyanka gobe Ina son ka d'aga, saboda tare zamu yola dakai.


Yace Dad mai zanyi a yola kuma?


Dad yace maganan daurin aurenka


Murmushi yayi tare da ciro wata takarda yace wannan takardan na rubuta saki uku, so idan kun d'aura auren saiku duba ku gani, "Dad Wlh bazan aureta ba in kuma kuka aura min ita Wlh nan take zanyi abunda za'ayi da'an sani, yana fad'in haka yabar wajan Fuuuuu


Granny tace ikon Allah miye haka kaman iska, Mai yake fad'a ne?


Dad shuru yayi cikin bacin rai, lallai Najeeb yana son yayi Fito na fito dashi, ya kamata ya koya mai hankali


Mum bata ce komai ba, sai Zarah data tashi ta nufi Granny tana fad'a mata abunda Najeeb yace, tare da fad'in Wlh Granny tunda baya so inaga Ayi hakuri kawai kar Ayi abunda za'a zo ana dana sani.


Granny shuru tayi tana nazari.


Hanne ce ta fito ita da d'anta a hannu, Tace Sannunku?


Granny tace Hanne lafiya kuwa?


Tace nidai gaskiya bana son wannan auren, dan Allah ku maidani gida, wlh bana son wannan auren, ni nasan yafi karfina, kawai ku maidani gida


Granny tace ikon Allah, mai kike fad'a Hanne?


Tace eh ni bana son auren


Granny tace ikon Allah, keda nake tausayawa saboda d'anki shine kike fad'in haka?


Hanne tace Idan saboda d'ana ne, kawai a taimaka min yafi, bana bukatar inyi auren da ba'a sona, ni nasan yafi karfina nesa ba kusa


Granny ta tashi ta nufeta cikin sigar rarrashi Tana fad'in haka Hannatu kodai yayi miki wani abu ne? Karki damu Ina nan babu abunda zai faru ki kwantar da hankalinki Kinji Hanne na?...... Toh Bari muji yanda zata kaya




Plz need ur prayers Wlh banda lafiya
















Read and leave it, dnt share to anyone


*IDAN KIKA KARANTA BAKI BIYA BA INA BINKI BASHI, KUMA NAUYI NE A KANKI*


*WACCE TAKE SON BIYA ZATA TURA 200 TA ACCOUNT NUMBËR DINNAN*


3138831065 Firstbank Maryam Alhassan


*SAI A TURO SHAIDAN BIYA TANAN 08060860886 IDAN KUMA KATI NE MTN SHIMA TA NUMBER DIN ZAKI TURA 200 NAIRA ONLY*


*KARKI MANTA KINYI ALKAWARI, BAZAKI FITAR MIN DA NOVEL BA, IDAN KIKA FITAR DASHI KEDA ALLAH, KUMA KINA D'AYA DAKA CIKIN MUNAFUKAI, DOMIN ALAMAN MUNAFUKI GUDA UKU NE, 1 IDAN ZAIYI MAGANA YAYI K'ARYA 2 IDAN AKA AMINCE MASA YAYI HA'INCI 3 IN YAYI ALKAWARI YA SABA, KIN DAI JI, KINCE KIN MIN ALKAWARI, IDAN KIKA SABA KIN ZAMA MUNAFUKA, KUMA WUTAR MUNAFUKI DABAN TAKE, IDAN KIKA FITAR KINMA KANKI*




Hanne tace kiyi hakuri Baba, bazan iya auren shiba gaskiya,


Granny salati ta saki, tare da fad'in oh ni aminatu, waike Hanne kanki d'aya kuwa? Maiya sameki haka?


Hanne kuka ta saki tana fad'in ita bata san wannan auren, kawai a Mai data yola.


Mum ganin haka yasa tace kiyi shuru, Kinga kina son saka d'anki kuka.


Zarah kam murmushi takeyi, domin ita d'aya tasan abunda ta k'ulla,"Wanda ko Najeeb bai sani ba.


Granny tace Hanne ko anyi miki wani abu ne? Janta tayi sukai d'akin da sauran matan suke, "suna ganin Granny suka fara gaidata, tare da k'okarin boye kud'in hannunsu Wanda Granny ta shigo taga suna kirgawa.


Granny kallonsu ta tsayayi tare da fad'in "wannan kud'in fah? Daka ina suka fito?


Nan su duka suka fara kame kame tare da sunkuyar dakai, "Granny tace bada ku nake ba? Cikin tsawa.


Nan Hanne ta Fara bata Labarin abunda ya faru, tare da fad'in koda kanwarshi ta kawo kud'in ta fad'a mana gwara mu amsa ince bana son auren "dama ni ko batace haka ba, wlh baso nake ba, dan Nasan bamu dace ba, "kuka Hanne tasa tana ro'kan Granny akan tayi hakuri ita Kar Ayi wannan auren dan zata cutu tunda baya Sonta.


Granny shuru tayi,lokaci d'aya ta Fara magana "tare da fad'in ya isa haka, ku kwanta zuwa gobe, insha Allah zamu yola kunji? "suka amsa da Toh ,"Granny fita tayi daka d'akin.


Granny iske Dad tayi a falo shida Mum, daka gani suna jiranta ne, "zama Granny tayi tare da d'aura hannunta akan fuskanta tana d'an bubbuga k'afa alaman ranta a bace yake.


Dad yace mama lafiya kuwa?


Tace audullahi d'anka baida mutunci, "tsorata y'ay'an mutane yaje yayi tare da basu kud'i, akan karsu yarda da auran.


Dad yace mama ban gane ba.


Nan Granny tace dama yaushe zaka gane?


Yanzu dai abunda za'ayi gobe zanje yola in maida yaran nan, badai auren bane baya so? Sai musa mishi ido ai.


Dad yace a'ah mama kar Ayi haka, kaman yanda aka tsara hakan za'ayi, goben zamu a d'aura aure, insha Allah, "kaman yanda muka shirya


Granny tace ai wannan maganan auren babu shi, tunda ita yarinyar tace bata so, " ya tsorata


Dad yace Wlh mama sai an d'aura wannan auren ko baya so, koda kuwa zai mutu,.


Granny dai shuru tayi tana nazari, can ta tashi Tana fad'in Allah ya kaimu raida lafiya tare dayin cikin d'aki ta kwanta.


Washe gari da safe tunda sukai sallah asuba suka Kama hanya su duka," amma banda Najeeb damin bai tashi daka bacci ba, sai dai Mum ta mishi message akan sun tafi yola


Sai wajan 10 Najeeb ya tashi Kai tsaye toilet ya nufa yayi wanka, tare dayin alwala, sai a lokacin yayi sallah, Bayan ya gama shiri ya d'auko wayarshi sai a sannan yaga sa'kon Mum, wani irin tsaki yaja tare da fad'in mai suke nufi?


Kenan sunje d'aura aurena kenan?


Kai ya girgiza tare da fad'in no no baza suyi wannan mistake d'inba, am sure.


Kawai sunje maida yaranne suba parent d'insu hakuri akan d'auko su da akayi, wannan tunanin da Najeeb yayi shine ya bashi daman cire komai a ranshi, shima daukar jakarshi yayi, yasa a mota driver yaja sukai hotel din da Gina take, baiko shiga ba ya kirata a waya tare da fad'in "come out, "yana fad'in haka ya kashe wayanshi .


Bata jima ba sai gata ta fito d'auke da k'aramin akwatin ta, kai tsaye motar ta shiga Bayan driver yasa mata akwatinta a booth, wani irin peck kiss tama Najeeb akan goshi tare da rungumo shi, tana fad'in oh baby I miss you so much


Wani irin kallo ya watsa mata Mai kama da kin cika jaraba, yaushe muka rabu,.


Ganin baice mata komai ba yasa ta k'ara manne shi, shidai driver tuki yake yana Allah wadai da irin wannan rayuwar


Kai tsaye airport yakai su, inda suka sauka, driver ya d'auko musu akwatin yana ja musu.


Shiko Najeeb da Gina suna manne da juna, kai tsaye Najeeb ya wuce domin ansan pilot ne, ba'a tsaya wani duba kayanshi ba, suka shige cikin jirgi shida Gina, Bayan an gama shiga 11:20 dai dai jirgin ya d'aga zuwa k'asar America.


Su mum sun isa yola, inda suka sauka a wani babban hotel, Kafin gobe su shiga kauyen su Hanne, "koda Abban ibtisam yazo shima a nan ya samesu, ibtisam tasha ko harda ummi za'azo sai taga bada ita bane


Washe gari da safe suka Kama hanyar kauyen su Hanne, inda sukai tafiyan awa biyu, Kafin suka k'arasa, "kauyen gidana irin na Fulani sai wajajan kiwon su.


Sauke su Granny sukayi a gidan y'an uwanta tare dasu ibtisam, su kuma Su Dad suka nufi wajan sarkin anguwan suka nufa, wanda shine sarkin fulanin gefen wajan, inda aka amshesu cikin mutunci da girmamawa, nan Dad ya fad'ama sarkin abunda ya kawo su,inda yayi na'am ya kuma bu'kaci a kira kawun Hanne.


Hakan ko akayi aka kira kawunta, inda ya tubure akan Wlh bazai amince da wannan aure ba, domin an mata miji cikin dangi akwai wanda yace zai aureta saboda yaronta zai ri'ke mata shi, yace sarki yanzu Kaga ni gwara muba na gida akan muba na waje.


Sarkin Fulani yace wannan hakane, amma ai suma na gida ne, tunda suna jin fulatanci suda yaransu duk da ba'a nan suke da zama ba, Koba haka ba? Tare da kallon Dad


Dad yace eh Toh gaskiya nan d'aya, yaron dai bayaji, sai dai mu muna ji


Nan kawun Hanne yace Toh ku kad'o ne koh?


Dad yace a'a mu Fulani ne mana, nan ya fad'a musu sunan mahaifinsu, kawun Hanne yace na sanshi mana, inda ban sanshi ba ai bazan bada Hanne a tafi da ita ba can bariki ba. Yace kenan baya jin fulatanci? Shuru yayi Kafin yaci gaba da fad'in.


kawun Hanne "yace kenan ku rabi da rabi kad'o da Fillo, toh gaskiya bazan yarda ba inba kad'o auren Hanne ba, "Yaje ya kaita shan Bariki ya ajiye ba.


Sarkin Fulani shima tunda yaji ance yaron baijin fulatanci yaji gaskiya wannan maganan bamai yihuwa bace, dan basa bama kad'o auren y'arsu cikin wannan kauyen, duk da sun San su Dad ba kad'o bane Amma ance yaron nasu baya jin Yaren fulatanci ,


Abban ibtisam yace Amma AI Ina ganin wannan ba matsala bane dan yaron baijin yare....


Sarkin Fulani yace matsala ne babba, mu muna mutunta yaranmu, ku kun tafi Bariki bakwa damuwa da nuna ma y'ay'anku yaransu, "Gaskiya kuyi hakuri bama Hanne ba kaf kauyen nan babu Mai baku auren y'arsu Indai sun San yaron bayajin yaren fulatanci, domin dashi da kad'o babu maraba.


Babu yanda su Dad basuyi ba, amma suka kafe, tare da fad'in d'ansu kad'o ne, haka suka tashi suka koma inda suka sauke Granny, yaro suka tura akan a fad'a musu sun dawo, "Mum ce ta fito tana fad'in su shigo mana .


Dad yace a'ah basai Sun shiga ba, tace ma Mama ta fito su wuce kawai.


Komawa Mum tayi ta kira Granny inda ta sami yaran nata a waje, tace lafiya badai har an d'aura auren ba?


Abban ibtisam yace a'a mama.


Tace toh maiya faru?


Yace... Sai kuma yayi shuru


Tace me inaji ku fad'amin mana?


Abban ibtisam yace Wai baza suba kad'o auren y'arsu ba.


Granny tace toh su Waye kad'on Toh?


Abban ibtisam yace Wai Najeeb tunda baya jin Yaren fulatanci.


Granny tace amma dai wannan ko yan wulakanci, akan wani dalili zasu kirashi da kad'o? Babu komai zan nema mishi Mata wacce tafi tanan Wlh, bari inyi musu sallama mu Kama hanya, ni naji zaman nan yama isan,"jikan nawa zasu kira da wani kad'o dan wulakanci tsaki taja tare da shiga cikin gidan inda tace su Zarah su taso su wuce tayi musu sallama Bayan ta basu kud'i.


Mum kam taji dad'in haka Koba komai d'anta yanzu bazai auri wacce baya soba, kuma y'ar kauye ta bakin nashi, "yanzu Abu d'aya zata dage shine ya koma karatun addini tunda ba'a girma da neman ilimi, sai dai Anfi so mutum yayi tun yana yaro, domin lokacin kwakwalwanshi yana saurin d'auke Abu, ba kaman Idan mutum ya girma ba.


Ibtisam kam ba'kin ciki kaman ya kasheta, "Wlh taso a d'aura ma Najeeb Hanne taga ta tsiya da miskilanci, da mugun hali tsaki taja.


Granny tace ke dawa kuma wannan tsakin kaman wata tsaka?


Ibtisam tace Kai granny miye na dangantani da tsaka kuma? "tare da sakin wani tsakin


Granny tace aikin banza, naga koda tsaka tayi tsaki Allah tsine Mata yayi balle mutum


Uhm kawai ibtisam tace tare da kawar dakai gefe guda


Granny ta tsuke baki tace ai inaga keda Najeebu zan had'a Idan Kabiru bai turo ba, dan naga abun nashi wasa ne.


Zarah tayi caraf tace Wlh kuwa Granny Nima haka nake Fata, kawai a had'asu, Kinga sun dace Sosai


Ibtisam banza dasu tayi, amma kallo d'aya zaka mata kasan ta cika tayi fam, a kumbure take, domin haushin wannan maganan take har cikin ranta wlh, gashi Mum na cikin motar balle tayi wata magana, dole yasa tayi shuru suke ta fad'a mata magana akan a had'ata da Najeeb


ita kam mum dariya kawai takeyi.


Tafiya suke har suka k'arasa hotel din da suka sauka, duk a gajiya, Zarah da ibtisam d'aki d'aya, Mum da Dad ma haka, sai Granny ita d'aki daya, sai Abban ibtisam shima d'aki d'aya.


Suna shiga ibtisam toilet tayi domin tayi wanka danta matukar gajiya Sosai, bayan ta fito wayarta ta Fara ruri "Zarah ta mi'ka mata wayan dan yana kusa da ita tace Kabiru na kira.


Hararanta ibtisam tayi domin tana jin haushinta ita da Granny.


Amsan wayar tayi tare da dannawa, "Zarah kam dariya tayi tana fad'in ikon Allah.


Ibtisam na waya ita da kabir, aka fara musu nocking, bud'e kofar akayi inda Granny ta Kutso kai Tana fad'in tare daku zan kwana, bazan iya kwana ni d'aya ba a nan


Zarah tace Mai yasa Granny?


Granny tace haka kawai, "ni tsoran wajan nan nakeji "yama kuke cema wajan?


Zarah tace hotel?


Granny tace eh zatol.


Zarah dariya, ibtisam dake waya itama Katsewa tayi ta Fara dariya,wai zatol.


Granny tace miye kuke dariya kaman kun zare? Ko kuma sabbin hauka?..


Ibtisam tace Granny miye wani zatol, hotel fa akace.


Granny ta tsuke baki tana fad'in kunce zatol, Nima haka nace zatol, "Toh miye ba dai dai ba?..


Kiran kabir ne ya k'ara shigowa ibtisam ta d'auka.


Granny aka tabe baki ana fad'in sai waya amma ya'ki fitowa, "lokaci kad'an na baka, koka fito ko in bata wani, bazan iya wannan tsiyar ba, da kashe kasuwa ba, kai bada fitowa ba, ka tarema wasu waje.


Gashi yanzu anje nema ma miskili aure anki bashi dan bayajin fulatanci, kai wannan rayuwa damai tayi Kama?"yau an nuna min iyakata koda yake suna da gaskiya, Sun nuna muku suna daraja harshen su, amma iyayenku Sun watsar dashi, sun koya muku Yaren aro, Yaren masu jajayen Fata, sai kuma Hausa daba yaranku ba, tsaki taja tana fad'in ai yanzu kwasan darajan yaran naku.


ita kam Zarah cikin ranta cewa tayi Allah yaga abunda ya gani sai yasa Najeeb baya ji, inda yana jin fulatanci dayau an d'aura mishi Hanne, "amma a fili sai tace Granny Suma sai basuyi niyan bashi matar bane inda sunyi niya Aida Sun aura mishi ko baya ji, ina ganin yare bashi bane matsala a aure, yanayin kamalan mutum da kuma addininsa.


Granny taja tsaki tare da fad'in inko kamala za'a duba, babu maiba miskili auren y'arsa, "Yaron da kana fad'a yana fad'a, Allah ya rage ma Aya za'ki dabai iya Hausa ba, inda ya iya Hausa Allah kad'ai yasan irin tsiyar dazai shuka, farin banza da hofi


Dariya Zarah ta saki tana fad'in Kai granny..


Granny tace eh mana "baki ga saboda ba'kin halinsa ba, har Hanne tace bata son auren, duk da harda ke aka had'a baki, amma ita ta nuna bata sonshi dagaske, miskilin banza dana hofi, "ki ganshi a fili kaman mutumin kirki amma inya tafka tsiya Kya rantse bashi bane, munafiki


Zarah tace shine munafukin kuma? Masoyin naki?


Granny tace ai Wlh bai gado mai sunan ba ko kad'an, domin ba haka yake ba, "ke inda Kinga Mai Sunan Aida kince Miskili ba halinsa ya gado ba, domin shi mutum ne mai saukin Kai da sanin darajan d'an Adam, baya raina kowa, "gashi ya iya soyayya kai zamanin mu munsha soyayya Allah yaji qanshi, kai sai kuma ta Fara share kwalla "alaman ta tuna da rayuwarsu tada


Zarah tace wayyo Granny kiyi hakuri Kinji? Allah yaji qanshi yasa ya huta


Granny cikin kuka tace Ameen.


Ibtisam dake waya tace nifa Granny kin isheni gaskiya, ki tashi ki tafi d'akin ki.


Granny ashar ta kunduma mata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login