Showing 54001 words to 57000 words out of 182942 words
Chapter 19 - NAJEEB COMPLETE BOOK Document writing Maryam Obama.txt
Salis dake bayansu yace ibtisam, idan Kinje ki rokeshi ya baki text din da bakiyi ba, domin 20mrk ba wasa bane
Ibtisam tace kana ganin zai yarda inna rok'eshi?
Salis yace Am not sure zai yarda, but try May be ya yarda, tunda mutum ne kuma yasan Allah
Zarah tashi tayi tana fad'in bari inje inyi sallah, in tafi lecture
Koda ibtisam ta fita itama taga Aisha ita da wasu mata a zaune suna ta surutu, kuma duka firan akan in sunje club ne ga yanda zata kaya,"ibtisam tace suko kunya basaji, "club din da babu abunda ake sai iskanci da shaye shayen giya
Aisha ce ta katse mata tunani da fad'in ibtisam har kun fito?
Ibtisam ta saki murmushi tare da fad'in eh yanzu muka fito, "naga kinzo kin koma.
Aisha tace Aiko na shigo korana zaiyi wlh, baida mutunci ko kad'an
Sauran matan da Aisha take fira dasu suka zuba ma ibtisam ido, "wata Mai suna kubra tasha attachment brown da wando an matse tace wannan fah? Ban taba ganinta ba sai yau
Aisha tace d'akinmu d'aya sannan course d'aya muke karanta
Kubra tace OK, amma shine bakwa zuwa club tare
Aisha ta kalli ibtisam tace Kinji abunda take cewa, wai bama zuwa club tare
Ibtisam murmushi kawai tayi, "amma cikin ranta tace Allah ya rabani da zuwa club, kuma ina muku fatan shiriya, ku tuba ku daina...
Kubra ce ta katse ma ibtisam tunani da fad'in ibtisam koh?
Ibtisam tace eh
Kubra tace Sunan yamin dad'i, Sunan larabawa
Ibtisam murmushi tayi tare da fad'in ngd
Kallon AISHA ibtisam tayi tace plz zaki rakani wajan Dr jibril.
Aisha tace ni? Rufamin asiri Mai zakiyi a wajansa?
Ibtisam tace yace yana son ganina
Aisha tace toh fah, Allah yasa dai lafiya, kodai shima d'an hannu ne, ya gani ya kyasa?
Kubra ta saki dariya tare da fad'in uhm kibar lecturers dinnan, suna da iskanci, "amma Dr jibril ban tunanin zaiyi haka fah.
Aisha tace ke ba'a shaidan mutum wlh, "yanzu mutum zai nuna Shina Allah ne anjima kiga ba haka bane, rayuwa kawai Ayi sha'ani kawai
Kubra tace nikam ibtisam muje in rakaki, inje inji gulma komai zaice miki
Ibtisam kam kunyar jerawa da kubra take, domin irin shigar dake jikinta, Wanda mutumin kirki dan musulmi bazaiyi ba, "amma babu yanda ta iya dole ta bita suje tare tunda tana neman dan rakiya, musamman da taji ana fad'in kodai dan hannu ne shima, "sai taji ta tsorata dan dama tasan ana cewa lecturer suna iskanci da student d'insu in ta'ki yarda sai su fadar da ita a course d'insu
Har office din Dr jibril suka isa, da yake kubra tasan office din, nocking sukayi yace yes coming
Bud'e kofar kubra tayi ta Fara shiga, ibtisam na bayanta kallo d'aya zaka mata ka gane jikinta yana d'ari d'ari
Karatun al'qur'ani yake saurara
Ganin Sun shigo yasa ya kashe karatun tare da kallon kubra yace lafiya?
Tace sir cikin d'ari d'ari na rakota ne.
Yace OK you can leave
Fita kubra tayi da sauri
Ibtisam kanta na k'asa idon Dr jibril na kanta ganin yanda ta tsorata ba tare da ance wani abuba, inda zaiyi ihu da karfi zata iya zabura
A hankali yace you can sit
Zama tayi akan kujeran daya nuna mata
Yace ya sunanki?
Tace Amina, but ana cemin ibtisam
Yace OK
Tare da fad'in mai yasa kika fita a lecture Rannan da zan bada text, ko mark dinne bakya so?
Da sauri tace a'ah
Yace so tell me why kika fita?
Tace saboda ban San abunda zan rubuta ba, sai yasa na fita, ranan shine farkon shigana lecture
Yace amma ai an dad'e ana lecture why baki Fara attending ba sai ranan?
Tace akwai problem din da yasa ban fara attending da wuri ba, sai daka baya aka yarda inzo
Yace which problem?
Shuru tayi tana d'an nazari, can tace "sir is family issue
Murmushi yayi tare da fad'in oh ok sorry for asking you
So yanzu kinyi missing 20mrk kenan right?
Ibtisam tace plz kayi hakuri ka bani inyi, tunda ranan na fara attending kuma kona rubuta I will fail, that is the reason da yasa naga gwara kar in rubuta din
Idon Dr jibril na kanta yana kallon yanda take magana, ba kaman daba da take kaman a tsorace, "yanzu ta dan sake
Yace OK zan baki text, but not now kizo gobe by 5pm sai in baki.
Da sauri ta d'ago ta saki murmushin da yake k'ara Mata kyau, tare da fad'in "nagode sir
Yace karki damu you can go
Tashi tayi cikin murna ta fita..
Dr jibril da ido ya bita yana murmushi.
Koda ibtisam ta fita taga kubra tsaye tana jiranta.
Bayan ta fito kubra ta kura mata ido tun daka sama har k'asa
Ibtisam tace lafiya irin wannan kallon?
Kubra tace ina son insan koya miki wani abune, "Sai yasa nake kallonki inga Ina ya taba .
Ibtisam tace auzubillah "wlh kinyi mishi sharri domin ba haka yake ba, kuma ko maganan banza baiyi min ba, "infact ma magana yayi min akan Mai yasa da yace zai bada text na fita? "shine na fad'a mishi dalili, har yace zai ban text din inyi, "ni Bama yanda nake tunanin ana fad'a akanshi Nayi ba, mutum ne mai sauk'in Kai a yanda na Lura raini ne kawai baya so, "sannan yana kama kanshi ne da shaidanun student masu kaima lecturer tallan kansu.
Kubra tace uhm ibtisam kenan, daka had'uwa dashi yau yau har kin Fara bada shaida a kansa haka?
Ibtisam tace ba haka bane, kubra Ina son ki gane wani abu, koda yanzu kika had'u da mutum indai kuka zauna kukai maganan minti biyar Zaki dan iya fahimtar Waye mutum da kuma irin abunda mutane ke fad'a akanshi
Kubra tace toh ba girin girin badai, "Allah yasa Dai kar nan gaba inji kina tsine Mai, kina fad'in Ashe haka yake
Ibtisam tace insha Allah bazaiyi abunda za'ace tir ba, domin koda Yana aikata wani mummunan Abu, yanayi a boye Toh Allah zai iya shiryashi tunda a boye yakeyi "amma wanda yakeyi a fili shikam sai dai ace Allah ya kyauta, mutum ya dinga Abu baya tsoran kowa, baki'i uban kowa ya gani ba, Kinga wannan yayi nisa baya fatan shiriya,"kuma shaidan duniya itace ta k'iyama daka ranan da mutum ya mutu za'a turo mala'iku suzo suji abunda mutane ke fad'a akan ka
Idan mutane na fad'in oh an rage mugun iri, ka bani
Inko aka samu ana yabanka ana fad'in mutumin kirki, koda kana aikata sabo a boye babu wanda ya Sani, sai Allah to Allah zai yafe ma mutum tunda wannan tsakanin Allah da bawa ne, kuma sirrin da Allah ya rufe babu Mai tona shi
Kubra tace Allahu Akbar, "Ashe ibtisam din malama ce?
Ibtisam tayi murmushi tare da fad'in daliba dai, muna koya ne
Tafiya sukayi daka wajan inda suka nufi d'akin su ibtisam din, suka iske Aisha na zaune tana waya
Ita dai ibtisam zama tayi tana jiran gobe tayi taje Dr jibril ya bata text din, d'auko littafi tayi ta Fara karatu
Bayan Aisha ta gama wayar ta kalli kubra tace ya kuka kaya dashi?
Kubra tace korana yayi da muka shiga
Aisha tace ita d'aya kika bari? Maiya mata?
Ibtisam dake karatu tace babu komai, tare da bata labarin abunda ya faru
Aisha tace kodai yana miki wayau ne nan gaba ya fito da mayyatarshi, dan naga nashi Abun kaman da salo yakeyi
Ibtisam tace Wai Mai yasa kuke mishi mummunan zato ne? Dan Allah ku daina Wlh babu kyau, tunda baice komai ba Kubar mishi mummunan zato, ku dinga kyautata zatonku akanshi plz
Aisha tace lallai ibtisam ke yarinya ce baki San mai duniya ke ciki ba, kin ganni nan, "babu irin iskancin da ban sani ba, "sannan babu wani salo dana miji zai kawo in kasa gane inda ya dosa, "kuma Wlh zaki ce ni Aisha na fad'a miki, wata rana saiya fito miki da manufarshi
Mutumin da baya wasa, baya sakar ma kowa, in bakayi text d'inshi ba, kokai Waye kayi missing kenan, 'amma ke har yace kije office d'inshi sannan ya yarda zai miki, uhm akwai wata a k'asa Dai
Ibtisam cikin ranta tace Wai Mai yasa mutanan da suke aikata sabo suke ganin kaman kowa ma haka yake.
Lallai maganan da malamin su ya taba fad'a musu gashi yau ta tabbatar, in mutum yana Abu sai yaga kaman kowa ma irinsa ne, sai yaga kaman kowa ma yana irin abunda yakeyi," mutumin kirki shine wanda yake ganin kowa kaman na kirki ne, na banza yana ganin kowa na banza ne. "Amma a fili sai tace nidai bayyi min Kama da mutumin banza ba
Kubra tace bazaki gane ba, gaba muke miki tunani kuma zakice mun fad'a
Tashi kubra tayi tana fad'in bari inje in dawo tare da kallon Aisha tana fad'in "anjima 8 akwai birthday din fatin d'akinmu ta fad'a miki kuwa?
Aisha tace eh ta fad'amin Zanzo
Kubra tace OK tare da kallon ibtisam tace Kema Ina inviting d'inki Tana fad'in haka ta fita
Aisha ta kalli ibtisam tace ina fatan zaki je koh?
Ibtisam tace Kai Anya kuwa
Aisha tace a cikin skul ne ba wani waje ba
Ibtisam tace OK tunda cikin skul ne Zanzo nida Zarah
Aisha tace OK saimu je tare gaba d'aya
Koda zarah ta dawo ibtisam tace su shirya zasu birthday din wata cikin skul din za'ayi
Zarah tace ok, amma fah ni bana son shiga iri irin wannan Abun.
Ibtisam tace nifa da Farko nace ba zani ba, saida akace a skul za'ayi
Zarah tace ok.
Ibtisam da zarah sun shirya duka cikin dogayen riga, ita Zarah doguwar rigan atamfa tasa, ita kam ibtisam jallabiya sunyi kyau Sosai duk da ba makeup sukayi ba, sai dai ita Zarah ta shafa powder
Bayan sun gama shiri, suka zauna jiran AISHA Dan tare zasu, dan ita ibtisam ba sanin d'akinsu kubra din tayi ba.
Aisha ce ta shigo cikin riga da wando, tare da fad'in ku muje, na tsaya amsan abune
Fita sukayi, har bakin gate Aisha ta tsaida mota suka shiga
Ibtisam tace kunce cikin makaranta?
Aisha tace eh amma a cikin gidan wanda suka Kama d'akin waje za'ayi...
Ibtisam bata k'ara cewa komai ba, har motar da suka shiga Aisha tace ta tsaya a nan.
Fita sukayi Aisha ta biya kud'in suka shiga wani Gida inda d'akuna ne Kala Kala a kalla yakai 30 daka ganin dai gidan d'akin dalibai ne, "baka jin k'aran komai saina kid'a da ihun Mata ana rawa, ko wacce ta tsuke cikin shiga mara kyau
Ibtisam da zarah kallon juna sukayi
Samun waje sukayi suka zauna inda suke kallon irin rawan da sukeyi, gaba d'aya babu maza sai mata, ibtisam tana cikin wannan tunanin saiga maza sun Fara shigowa kaman ana turosu kuma duk dalibai ne mazan student
Nan wajan ya k'ara kacamewa da ihu, inda maza da mata suka fara rawa cikin rashin kamun kai da fitsara
Suna rawan a manne da jikin junansu, basa kojin kunya.
Yayin da wasu ke zaune a gefe suna shan shisha wasu kuma suna shan codeine kuma duka student Abun dai babu kyan gani
Zarah ta Katse ma ibtisam tunani tare da fad'in jiba birthday din babu ko tsari, wannan Aiba birthday bane, ni ko cake ban gani ba
Ibtisam tace uhm, kawai dai sun had'a party suyi rawa, "ni tashi mu koma dan ban son kallon wannan iskancin wlh
Zarah tace a'ah mu tsaya Kinga dare yayi saimu fita muda yawa, mu zauna a nan iya kacin mu kallo
Ibtisam tace Allah ya kyauta
Zarah ta amsa da Ameen
Haka suka zauna suna ta kallo ashe anyi cake, an ajiye ne a ciki lokaci d'aya aka d'auko birthday girl ta yanka nan suka saki ihu ana tafi
Su ibtisam na nan zaune saiga kubra tazo, tace zan kuka zauna? "kuzo kuyi rawa mana.
Ibtisam tace a'a barmu kawai a nan
Kubra tace haba miye haka? Duka fa nan student ne babu bare, plz ku tashi mana, janyo hannun ibtisam tayi wanda dole yasa ta tashi sannan ta janyo zarah itama, tare da fad'in muje kuyi rawa
K'aran wayan ibtisam ne yasa ta janye hannunta daka na kubra tana kallon wayar cikin tsoro ganin sunan Ummi ne a cikin wayar tana kiranta, "gashi wajan k'ara yayi yawa, "janyo Zarah tayi suka fita daka wajan amma still k'aran kid'an har waje
Saida sukayi nisa da wajan sannan ibtisam ta tsaya "Zarah tace miye kike ta jana lafiya?
Ibtisam tace ummi ce ta kirani ban San mai zata cemin ba, gashi wajan k'aran kid'a yayi yawa, "bari in kirata inji mai zata ce
Kiran Ummi tayi, "ummi ta d'auka tare da fad'in ina aka shige aka ajiye wayar?
Ibtisam tace ummi wayar na silent ne tunda na fito daka lecture Ashe ban cireta a silent ba
Ummi tace ok, Nayi magana da abbanki, gobe zai bada wayar ta Mota a Kawo miki, zaiba driver din number d'inki saiki je ki amsa
Tace toh ummi tare da fad'in nagode ummi na.
Ummi tace akwai abunda kike bukata?
Tace a'a ummi bana bukatar komai, ina Granny?
Ummi tace bari inkai mata
Ummi taba granny waya, ibtisam tace Granny shine ko kirana bakyayi a wayarki koh?
Granny tace yaushe zan kiraki yanzu kin zama y'ar jami'a Kema zaki fara fitsara irin na miskili, in kira a fad'amin ba dad'i
Ibtisam tace Granny lallai kince wani abu, Sharrin da zakiyi min kenan koh?
Granny ta tsuke baki tare da fad'in ke yanzu kin fison zama a wani gari koh?"zaki sa aita miki kallon y'ar iska, ni wannan Abun kunyar har Ina, haba takwara ta ki dawo gida mana in anyi bikin naku keda kabirun sai kici gaba a dakin ki, Kinga babu wanda ya gani balle yace
Ibtisam tace Kai granny wai Mai yasa kike haka ne? Ni ginka sai anjma
Granny tace ai kyace sai anjima tunda ba'a son gaskiya, zan kira kabirun ai inji dalilin da zai yarda yace kije wani gari karatu tunda shi baida kishin kanshi
Ibtisam dariya ta saki tare da fad'in Kinga Granny sai anjima tare da kashe wayar
Zarah itama dariya tayi tana fad'in Granny ba dama hala mita take miki
Ibtisam tace Wlh kuwa, mitan na'ki aure kin San ita magananta kenan, ta matsa inyi aure ansa rana amma duk da haka bata kyaleni ba, ita wannan bokon ne dai bata so, na rasa dalili tsohuwa sai jaraba.
Zarah tace nikam wlh abunda Granny take fad'i gaskiya ne, ai kinzo jami'ar Kinga irin abunda akeyi a cikinta
Ibtisam tace Aiba duka aka taru aka zama d'aya ba, akwai na Allah Sosai, amma y'an iskan ne sukai kaurin suna
Zarah tace Allah ya kyauta Kinga mu wuce skul kawai, dan bazan koma ba tunda mun fito, machine suka samu suka hau 2 in 1 domin Sun dad'e suna jiran Abun hawa basu damu ba, sai yanzu shine suka haye machine din guda d'aya su biyu
Har cikin skul ya kaisu inda suka sauka suka biyashi sukai d'akinsu, suna shiga kiran kabir na shigowa wayar Ibtisam tace Wai Allah ya soni
Washe gari kaman yanda Dr jibril yace ma ibtisam hakan ko akayi 5 dai dai ibtisam ta nufi office d'inshi tayi nocking ya bata izinin shiga
Bayan ta shiga ta gaidashi cikin girmamawa
Ya amsa tare da sakar mata murmushi yace you can sit
Tana zama wayarta dake hannunta ya fara K'ara, k'okarin kashe wayar ta Fara yace you can answer it
D'auka tayi tare da sawa a kunne
Sallama aka mata tare da fad'in nine akaba sa'ko IN baki gani garage kina ina?
Ibtisam tace ina ABU plz ka taimaka ka Kawo min ban San ko inaba a cikin zaria ba
Yace kai gaskiya kiyi hakuri kiyi tambaya sai kizo ki amsa, kuma kiyi sauri dan nan da awa d'aya zan juya Kano.
Ibtisam tace toh kaban nan da lokaci kad'an zan tambayi inda garage din yake inzo
Dr kabir idonshi nakan ibtisam Bayan ta kashe wayar yace Mai zakiyi a garage?
Tace sa'ko aka aiko min dashi, daka Kano, gashi yace bazai dad'e ba zai koma and....
Sai kuma tayi shuru
Yace and?
Tace nothing sir am ready for the text
Tashi yayi tare da daukan key din motarshi yace muje tare dayin gaba
Binshi tayi da ido tana kallonshi, tare da tunanin Ina zamu????
Ganin yakai bakin kofa bata ko motsa ba, yace I said let go
Tashi tayi da sauri ta fito ya rufe office din
Tafiya ya fara tana bayanshi har wajan daya faka motarshi k'iran Benz, yace shiga muje
Bata shiga ba sannan batai magana ba, domin ita dai bata san ina zasu ba inta shiga, sannan akan wani dalili zata shiga motarshi?
Dr jibril yace Amina Mai yasa idan akayi magana sau d'aya bakya d'auka sai an k'ara repeating din magana?
Tace sir kawai naga ban San inda zamu bane sai yasa
Yace zanje in sai dakine
Da sauri ta d'ago ta kalleshi cikin mamaki
Ganin irin kallon data mishi yasa yayi dariya tare da fad'in calm down am joking,"just enter d car
Ganin bata da niyan shiga yaga alaman tana jin tsoro yace shine matsayin text d'inki, and in baki shiga ba zanyi failing naki
Bud'e kofar tayi ta shiga Tana tunani iri iri a ranta
Shiko ganin ta shiga ya tada motar yabar skul din
Ibtisam kam bata sake ba domin a tsorace take dashi, tana tunanin Ina zai kaita daya d'age saita shiga cikin motarshi, kodai abunda su Aisha suke fad'i gaskiya ne. ....
*nayi na yau da gobe coz gobe inada uzuri bazan samu daman typing ba, sai jibi insha Allah zanci gaba*
Read and leave it, dnt share to anyone
*IDAN KIKA KARANTA BAKI BIYA BA INA BINKI BASHI, KUMA NAUYI NE A KANKI*
*WACCE TAKE SON BIYA ZATA TURA 200 TA ACCOUNT NUMBËR DINNAN*
3138831065 Firstbank Maryam Alhassan
*SAI A TURO SHAIDAN BIYA TANAN 08060860886 IDAN KUMA KATI NE MTN SHIMA TA NUMBER DIN ZAKI TURA 200 NAIRA ONLY*
*KARKI MANTA KINYI ALKAWARI, BAZAKI FITAR MIN DA NOVEL BA, IDAN KIKA FITAR DASHI KEDA ALLAH, KUMA KINA D'AYA DAKA CIKIN MUNAFUKAI, DOMIN ALAMAN MUNAFUKI GUDA UKU NE, 1 IDAN ZAIYI MAGANA YAYI