Showing 87001 words to 90000 words out of 165901 words

Chapter 30 - SAMARIN SHAHO Completed Book Surayyhms.txt

Advertisement

Surayya   

06 Jun 2024

13903

amma bai samu daman yin haka ba


Cikin ransa sai ya fara tunanin kar dai yaji shiru ne ya sa ya zo dakan sa?
Kai amma ban kyauta masa ba..is not easy mutum yayi rayuwar sa cikin ciwo nadama da tsangwamar mutane..


Gashi ni da na masa alkwarin samun sauki ban kula ba..


Da haka ya sa ya sauko cikin azama yayi kansu,
Sosai yaji wani irin gani su anan din.


Yana isowa suka mike tsaye, zasu gaishe sa sai shi ya riga tanbayar su da cewa yaushe suka zo?


Shikam sageer bai gane sa ba amma baba babaji ya so ya fahimci fuskan sa.


Yaxeed Yace" kamance dani ko?
Nine nazo wani lokaci nace zan sa akawo ka offishin sarah,


Murmushin bazata baba babaji ya sake Yace Allah na gode maka,nan ya gaya masa cewa ai saratun da kanta ta zo amma abunda yafi bata masa rai yanzun wulakancin da aka musu ne akan ganin ta.


Yazeed ya dauka ko duk kauyanci ya sa suke refering dinta as saratu,
Sai ya ga kuma sun nace suna magana akan haduwar su da ita,yanzu haka ma rokon sa suke yi ya taimaka su ganta..


Basu damu da yunwa ko gajiyar da ke damun su ba muddin zasu hada ido da ita..


Tuni wani abu ya basa maybe is a personal issure... amma sosai yake so yaji don ya sha mamaki kuma kansa ya daure matuka"


Me hadin sarah da wayannan? How did thy know her,ko tayi musu alkawarin wani abu ne? To meye wannan din..


yasan dole sai ya yaudare su kafin ya san kan zancen,sai yace kuyi hakuri tukunna kunga yau sarah tana da manyan baki bazai yuwu ku ganta ba,
Amma ni zan je daku ku huta ku ci abinci gobe da kaina zan sa sarah ta saurare ku..


Murna akan murna baba babaji har da rusunawa kasa wajen sa ma yazeed albarka mai cike da godiya da karamcin nasa


Haka ya sa su a motar sa ya kaisu wani karamar hotel, anan ya odering musu abinci mai shegen dadi da tsada kaji ne nasha nasha mai qamshin dadi ga abubuwan jika magwogro.


Yana daga gefen su suka haura kai ham ham kamar dan wuta yaga gasashen nama,


Baba babaji naci hr zufa na saukowa akan nasa kamar wanda ke cikin Shower..


Duk yana kallon su, sai hiran santin suke
Time to time yana sa musu baki


Cikin salo yazeed din yace amma da cahn kasan sarah ne ko?
Anan ba wanda yake zuwa ganin Ta kai tsaye sai akan lokacin da ta basa...


Baba babaji ya dago a sanyaye ya dube yazeed yace "nasan ta sosai..shiyasa ma kaga na zo don na same ta.
Saratu ai yata ce...


Sageeer yace haka ne, yar sa sace ,ai wannan daka ke gani oga, shine mijin mahaifiyar saratu
Bayan mahaifin ta ya rasu,


Cikin tsananin mamaki yazeed yace ohhhhhhhh
Kenan kai mijin maman sarah ne? Amma ai mahaifiyar ta bata da wani miji a yanzu haka..
Ban fahimce ka ba.


Baba babaji Yace ai mun rabu ne,


Yazeed yace ohhh ayyah..
Toh meya faru ko zaka iya fada min,?
Kar ka damu aiki na ne taimako zan taimaka muku..


Su kan sun yarda da yanayin yazeed beside shekaru aru aru kenan babu wanda ya dube su da idon rahma har ya kashe kudin sa akansu ya basu muhalli da abinci sai yau..


Gashi har ya na cewa zai taimake su...rabon baba babaji yaji wani mutum na daban haka kawai yace zai taimake sa ai ya mance.


Sai abun ya taba zuciyan sa anan ya taso ya zauna shi da sageer..


Nn Suka shiga bada yazeed labarin saratu da ummahn ta in è best way thy can..


Sai dai cikin nuna nadaman su da neman yafiya suke bayanan nasu,
Sannan suka tabbatar masa da cewa lallai sarah itace saratun su.




Mamaki da rudani ya hana yazeed magana,sai baki yake basu yana gwada masu babu komai shi xai taimaka


Amma cikin ransa is full of questions .
Musamman fannin ta ya akayi sarah ta kufce ma wannan mummunan qaddara ta har ta zamto haka?
How did she make it? Yasan dai a waje tayi karatu kuma mum din ta na da sana'ar ta da kudin ta but how did thy make it?


Amma ace a haka suka taso?Toh ya akayi suka samu duk wannnan rayuwar?Sata sukayi ko karuwanci?


ai yasan cewa ummahn sarah har yau bata sake aure ba bare ace arxikin mijin ta ne,but how?


Kenan akwai boyayyen sirrin sarah da ba wanda ya sani sai ita..


Ya dade yana kawo tots daga bisani yace ma su baba babaji,
Kar su daga hnkalin su,
Shi yasan yadda zai yi suga sarah amma su daure su bashi zuwa gobe,
Godiya sukayi ta masa sai dai hankalin sa bai ya wajen su,
Tunanin kawai yake yi kala kala akan sirrin rayuwar saratu daya dan ji yqnzu...
Now he knows where her abject inspiration to help the needy is coming from.


Babu shakkka jajircewar saratu ya samo asali ne daga ciwon qaddarar ta dake makale a zuciyan ta..


But this is not the end yana so yaji ya akayi ta cimma burin ta har tayi,ilimi da kudi haka..


according to baba babaji cewa yayi da ya fara nadama ya shiga neman su a da chan ance masa sun tafi birni a motar kano.


Kenan a kano saratu da ummah suka yi kudi?a kauyan cin nasu??,damn but they r oll women...thy r suppose to be weak,inma ba haka ba ai zai yi wuya ace mace ta shiga wannan halin sannan ta mance da shi so easily har ta tashi ta daga rayuwar ta..


Sai ya sa aransa dole sai yaji sauran kwaf kwaf din sannan ya samu nitsuwa


A daren daya koma gida sai ya tura makudan kudi ma wani mai suna zulkhi cewar sa ya hau jirgi ya taho su hadu gobe a gidan sa.


Anan su baba babaji suka kwana,


Washe gari da sassafe yazeed ya kawo wani agents dinsa ya hada su tare yace akai su ga saratu..


Daga nan shi kuma ya wuce wajen zulkhi bai bari ma sarah ta san da shi ba..


Anan ta karbe su ba yabo ba fallsa ta kaisu wani wajen daban suka samu zama.


Kamar a mafarki suke ganin realityn su,ita kuwa bata boye musu ba ta fada musu itace din,..


Duk dama ta sha mamakin ganin su amma sai bata nuna ba,..


Anan duk suka dada warware mata duk munafurcin Da suka mata cike da nadama da neman yafiya
Suka roke ta don ta yafe musu..


Dukan su kuka suke yi har da ita don Tasan za'ayi hakan ya sa ta sa suka bar office din gaba daya suka je wani waje.


Bayan sun fahince juna ta kaisu gida har wajen ummah,anan ma suka nemi gafarar ta.


Dan itakam ummah addini yanzu ya shige ta sosai halayen ta ko da ba ace ba kasan imani ya ratsa zuciyan ta ya mamaye shi..


Duk da bata iya hade baqi ba,takan zauna ta kunna karatun qur'ani tana ji yana mata dadi sosai.


Tsaban naci har ta haddace wasu surorin cikin sauki ta haka.


Kuma zata iya daukar fiye da awa 4 tana kallon wa'azin malaman nan bata gaji ba.


Gashi dama da saratu ta samu cin gaban rayuwa sai ta rage mata zuwa aikin ta, yanzu haka managers din ta ke lura mata da gidan gonan ta da gidan kajin ta.


Su baba babaji A duk yadda suke ganin saratu tayi musu karamci bai kai yadda suka ga ni wajen ummah ba,don sosai ta mance da komai sai ma nasiha mai shiga rai data yi musu..


Haduwan su da ummah ya dada zafafa zafin nadaman da baba babaji keji aran sa....lallai ya kasance hasararre ya kaskatar da rayuwar gambo amma Allah ya nuna masa cewa gambo ce mai nasara tun a duniya.


Kwana biyu suka yi anan gidan su saratu cike da goma na alheri suka koma gida...


Sarah ke tabbatar masa da cewa idan sati biyun ya cika zata sa a dawo da su a fara masa jinya...


Tsaban dadin yanayin da suka samu yafiya cikin sauki ya sa suka mance da yazeed don haka basu ko fada ma sarah cewar sun hadu da shi ba har aka rabu


Ita kam dama yanan nade a zuciyan ta amma kwana biyu data ga kamar ya share ta ya sa ta dan bada hankalin ta wajen ayyukan dake gaban ta


Amma yau da su baba babaji suka tafi


Tana Dawowa sai ta wuce straight offishin sa ko zata lallaba sa taji meye matsalan ,


Amma da mamakin ta sai ta ga offishin sa a
kulle
Ta sake kiran layin sa shiru shi ba off ba shi ba ringing ba.


Ko da ta tambaye farida secteryn sa ce mata akayi
Kwana biyu sukan su ba su gansa ba kuma basu san inda yake ba.












*Writers coments continued*
_samarin shaho is also to ladies that have everything in life but give less important to their god,sarah na daya daga cikin wanda suka mance da wani muhimmin bangare na rayuwa...misali, Ku dubi yadda sarah take mance da yin sallah akan lokaci idan suna tare da yazeed,ku fada min meyasa hakan bazai faru da ita ba?...yan mata ku tsaya ku kalle rayuwar sarah nan gaba... its very important...."kenan dan wani mummunan qaddara ya faru da kai arayuwa sai ka sa burinsa agaban ka fiye da komai har kula da ubangijn ka?toh wa zai taimake ka akan mugayen maza kamar samarin shaho?wayon ka ko ilimin ka?..,Kuma ina kira da kar kuyi ma labarin hanzari ku dan sassauta min i want to give more pages,nasan labarin baida dadi sosai amma sakon dake ciki is kind of more realistic than fictional#relax fans im also with you on this#sakallahu khairan,wah saka biljannat awaiting ur heartouching coments always😍_












*Official cat*
[2/24, 08:55] ‪+234 802 646 5734‬: *🅱RILLlANT WRITERS ASSO🖊*
{ _pens of freedom,home of exceptional and magnificient writers_ }
™\jan\2019
🍒🍒
*SAMARIN SHAHO*
_The scorned_
🍒🍒
*#lovestory:#destiny@fault#purefic#thriller:#romance,any resembelance of life or story shud be considered as a coincedence i give no permission for copy or comparison#copycat*
_A true sensational story_
*VOTE STORY AND FOLLOW WATTPAD@ SURAYYAHMS*




_28.._




Abun bai daga mata hankali sosai ba, sabida tasan maybe yar fushin nan Ne daya saba idan bata bashi attention dinsa ba,..


Hakan ya sa ta koma bakin aikin ta tana yi tana gwada layin sa amma babu wani sauyi,


Haka har ta tashi daga aiki ta koma gida bata ji shi ba.


A chan bangaren yazeed kowa haduwar su da zulkhi ya sa ya tambaye sa yadda za'ayi su samu tarihin sarah da mahaifiyar ta a garin kano shekaru da suka wuce.


Ya nuna masa hotunan sarah da na ummahn ta,


Sannan ya bashi dan detail din da ya samo daga binciken sa akan ummah da shekarun da ummah ta zo lagos.


Toh shi zulkhi shiya binciko musu cewa ai gidan kaji da gidan gonan da umma ta mallaka na shahararren Mai kudin nan ne alhaji abdul azeez shayal...

Daga nan yazeed ya sha dammara suka wuce kano ba bu wanda ya sani,suka shiga neman diddigin labarin ummah dana saratu..


Da kyar da wahala suke samun bayani daya sabida rayuwar su sunyi shi ne a cikin sirri wanda akalla sahura ce kawai ta san komai..


Amma da shike abubuwan mamaki da yawa sun faru, a ko yaushe idan wani sirrin ya fito sai ya dada sa ma yazeed din son yaji karshen bayanin..


Yanzu haka har kudi ya biya ana nema masa inda zaiji gaskiyan lamarin rayuwar su.


Anan kuma lagos sarah day by day tana shiga tashin hankalin rashin samun yazeed


Tunani dayawa ta kawo aranta nacewa ina zai je wanda har iyayen sa basa zu sani ba


Don ta tambayi kowa har gidan sa taje amma shiru babu shi ba labarin sa


Gashi yau ya cika wata guda chasss bai dawo ba.


Shikuwa da sannin sa yake yin haka ,so yake ya kwaba mata lissafi
Don shika dai yasan me ya ke shirya mata one big time...


Haka ta lalace da tunanin sa, bata iya cin abinci sosai bare bacci,


Saukin abun ma shine yanzu hapsy ta dawo nan branch din ta..


Ita kanta hapsy tausayin sarahn ke damun ta
A ko taushe da duba wayar ta sai taga dialled calls din yazeed yafi a kirga


Har ta gaji ta sa ta gaba tace,sarah dan Allah ki sassauta makan ki mana,
Ai inda ya damu dake bazai bace miki rana guda kiyi ta neman sa baki same sa ba..


Please this is getting too much baki ganin yadda kika dawo ko?


Abun na damun ta sosai duk dama kullum idan hapsy ta kawo magana bata tankawa yau kam sai taji dole ta sawwake ma zuciyan ta ko zata samu saukin zafin da yake mata.


Tace hapsy wallhy na kasa ne,kaina ya daure
I just cant hepl it na shaku da shi sosai...sai ta dan fara sauke hawaye..


Hapsy na shiru itama din tunani take yi,chan ta taso ta zo kusa da ita ta dafa ta
Sarah"?
Dago ki kalle ni,


A hankali ta dago.


Tace kina son yazeed ko?


Wasu hawayen ne suka taro mata lokaci guda tace eh hapsat ,ena son shi..kuma nasan shima yana so na
But we dint make it official


Hapsat tace ohhh crab .. now thats your problem,ya za'ayi ku rinka azabtar da kanku haka? Wai shin baku aminta da son dakuke ma wa juna bane ko yaudarar kanku kuke da bazaku furta shi ba?


Idan dukan baku bar wannan wasan banzan ba fa zaku yi illah ma zuciyoyin ku.


Cikin kuka ta ce to ni ya zanyi hapsy,nice zan ce ina son shi ya aure ni,ko shi zai fara fada min haka.?


I just dont get him...kinsan kuwa ranar da na vata masa rai ma haka nayi ta neman sa ban same sa sai daga baya ya zo yana gaya min wai bazai iya jure rashina kusa da shi ba ne"


I think don ban samu time dinsa sosai kwana biyun nan ba yasa ya tafi ya barni,this is tooo much for me
Yau kusan wata kenan Ban sake ganin sa..
Im feeling the pain i love him sooo much..


Kuka ta keyi sosai har da kife kanta akan teber gwanin tausayi..


Itakan ta hapsy yanzu tana cikin rudani


To wannan wani irin salon soyayya ne sarah ta dauka makanta..


Nan dai ta shiga rarrashin sarahn tana bata baki har ta nitsu tare da bata karfin gwiwar cewa tabbas akwai babban dalilin da yasa yazeeed yayi haka


Idan kuma ta yadda da yana son ta tayi hakuri ta bashi dama.


A cewar hapsyn maybe yana cahn yana shirya rayuwar su ne yadda idan ya dawo sai taga komai ya wuce..


da haka ta samu gwarun gwiwa


Amma sai dai kamar ko wani rana kara mata zafin son sa ake yi aranta


Kewar sa duk sun nakasa hanyoyin jinin ta,tunanin sa ya gauraye brain din ta..


Sometimes ji take kamar ta hadiyi ranta ta mutu
Da bakin cikin rashin sanin inda yake da dalilin sa na boye mata..


Haka rayuwar ta kasance
Hapsy ke jan ta da nasiha da shawarwari har ta samu tana sakewa


Kowa anan offishin sai da ya gane cewa rashin yazeed sosai ya taba walwalan sarah.


Wasu har tunanin yadda zasu faranta mara rai suke ganin yanzu sam bata samun peace of mind.


Shikuwa yazeed cikin wannan kwanakin suka bi hanya hanya har aka kaisu gidan sahura na da chan.


Anan aka basu labarin zuwan su da rayuwar su, hatta yadda akayi raping ummah agidan alhji sabo ya sani..sai dai suma cewa sukayi basu san inda suka koma ba


Har sai da suka hadu da wannan saurayin da da chan yake zuwa wajen sahura,


Shi ya basu labarin cewa ai ssa danjuma shi sukayi ma aiki


Yasan shi amma baisan inda yake ba yanzun


Daga nan su yazeed suka shiga neman adress da information akan ssa danjuma


In the process suka gane ba mutumin arziki bane, sannan ga sana'oin sa.


Anan yazeed ya san ummah tayi aikin strip club tun kafin ma yaji daga bakin ssa danjumA.


Toh aranar da suka hadu da shi,.aranar yaji sauran sirrin saratu da ummah don kuwa yayi playing cards din sa sosai akan ssa danjuma har ya samu jin Tun daga farkon haduwar sa da ummah
Da duk wani taimakon da ya mata a rayuwa ita da sahura


Sai dai iyakan sa daya hada ta ogan sa bai san ya suka kare ba....


Shima yazeed anan ya dakata da jin labarin nasa sabida jin ance ai alhj abdul azeez ya mutu


Samun wani information akan sa kuma zaiyi wuya
Tunda har shikansa Ssa danjuma bai sani ba...


So, yanzu yana da masaniyar duk wani rayuwar ashah da zubewar mutuncin da ummah tayi akan sarahtu


He just concluded dat tunda har ummah zata iya rawan kan karfe a club ana bata kudi..


To tabbas kwana take yi da alhj abdul azeez


shine ya bata dukiyar da take juyawa yanzu..


Its so clear to him,
Kenan shiyasa ummah ta samu share akan gidan gona da gidan kaji,kenan ummah karuwa ce?


Abun na matukar shakin kwakwalwar sa
Yana jin Tunda aka haifesa bai taba jin yanayin mamaki da tsanstar nazari kamar na yanzu ba




A ko wani dare sai ya yi tunani daban daban akan su..


Sai dai bai kyautata tunanin sa akan su ba ko kadan
Musamman rayuwar ummah na baya..


Ya dauki lokaci mai tsawo yana shirya kansa da plan dinsa wanda daga shi sai zuciyan sa suka sani.


Sai dai wani abu na damun sa,sosai yake jin kamar zuciyan sa tana tsananin kewa da son sarah..


Wani bin idan ya kawo tunanin haka sai ya sha giya akai ya fice hankalin sa Yayi ta dariyar da shi kadai yasan ma'anan ta



Yana nan agarin kano abokan sa kuma suna sane da hakan amma ba wanda ya sani bayan su


A yanzu haka ma shiri yake na tarban su ranar juma'ah ya gayyace su akan Zasu zo masa weeknd Dukan su.




Faisal ne mafi kusanci da shi, dan gidan senator ne
Shine kuma yafi comunicating da sarah
Akan bacewar yazeed din


Sai yaji nata sai yaje ya fada ma yazeed din abayan idanun ta....sometimes har rercoding zaiyi ya tura masa yaji suna dariya..


Sukan su sun sha masa tanbayar ko dagaske yake akan maganan sarah..


Amma har yau yaki fitowa fili ya gaya ma kowa mai yake tsakanin sa da sarah na asali


Bare kuma nufin sa.


Bayan azuciyan sa shikansa fighting yake da yanayin rayuwar sa da sarah amma yaki ya fuskance gaskiyan hakan


Labarin sarah dayaji abun al'ajabi ne kuma abun tausayawa ne,.but sai yaji babu hakan aransa.


Bai san zafin abun ba sabida a labari kawai yaji,bai san me ake nufi da qaddara ba sabida mummunan qaddara bai taba rabar shi ba bare iyayen sa..


Bai san me ake nufi da bakar talauci da cin zarafin mutunci ba sabida rayuwar sa tun da ya taso acikin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login