Showing 18001 words to 21000 words out of 165901 words

Chapter 7 - SAMARIN SHAHO Completed Book Surayyhms.txt

Advertisement

Surayya   

06 Jun 2024

13862

kyasan yadda zakii sa rayuwar ki anan garin marasa imanin..


Anan umma har ta kawo bakin asibiti,


Idon ta sun bushe amma karya ka kalle ta baka dago tana cikin ha'ula in rayuwa ba..


Kai tsaye ta shigo tana neman likitan daya rubuta mata magani.


Lokacin Ana neman kiran magrib nam ya samu ya dube ta
Acikin kudin nan ta zare ta bashi 15 da yan kai..


Kwata kwata ya rage mata saura dubu hudu da dari biu..


Anan tayi tsayin daka ga jikin ta har yanzu ba wai ya sake ta bane don ko kimtsa kanta bata samu tayi ba,


Takaici ke dawainiya da ita tana zagaye abakin dakin aikin..


Anan aka shafi kusan awa uku ana kintsa ni..


Wannan saurayin da da chan aka hado umma da shi shi ya zo ya dauke ta suka koma gida bayan likita yayi bayanin cewa an kammala komai
Amma yace bazan tashi ba sai gobe zasu cigaba da bani magani..


Anan ne data iso gidan tayi wanka ta kintsa kanta ta biya sallolin ta ta dada kai kukan ta wajen Allah..duk dama zuciyan is full of hatred and bitterness



Sahura da dan aikan ta kuwa ba karamin Mamakin yadda umma ta samo kudi da wuri suka ji ba


Dan haka sahura ta qudiri niyyar sa ma umma ido ko zata san ya take yi jiya jiya ace ta zo kano ,kanon ma bayan gari amma har ta san yadda zatayi shige da fice ta samu kudi mai yawa..


Ranar Ummah ko bacci batayi ba Washe gari da safe
Ta mike ta shirya,
Sallama tayi ma sahura tace ni zanje asibiti..


Sahurah Tace ma ummah insha Allah zata zo itama taga jikin Nawa..
Duk dai ko zata gane wani abu game da ummah amma shiru


Nikuma tun misalim karfe 4 saura na bude ido na warau na ke jina sai dai kananan ciwon ciki da dan jini da nake yi ba sosai ba..


Koda ummah ta ganni a haka ba karamin kuka da godiyan Allah tayi azuciyan ta ba, amma sai ta kasa furta komai sai sannu sannnu take min..




Na dauka duk tausayi na ne amma gaba daya sai na soma gane cewa ummah na fama da wani bakin ciki ma musamman a yau din.
























_Share_










*WATTPAD VOTE AND FOLLOW @SURAYYAHMS*








*OFFICIALCATTY🐈*
[2/23, 23:02] ‪+234 802 646 5734‬: *🅱BRILLlANT WRITERS ASSO🖊*
{ _pens of freedom,home of exceptional and magnificient writers_ }
™\jan\2019
🍒🍒
*SAMARIN SHAHO*
🍒🍒
*#lovestory:#destiny@fault#purefic#thriller:#romance,any resembelance of life or story shud be considered as a coincedence i give no permission for copy or comparison#copycat*
_A true sensational story_
*VOTE STORY AND FOLLOW WATTPAD@ SURAYYAHMS*
🐈


_PAGE6_


Kallo na bi ummah da shi a nitse tsawon mintinu na 10 amma kamar bata ma sani ba
Duk ta bi tayi tagumi ta bata shiru cikin tunani...


Nace ummah,ummah,
A nan ta dago a dan fakaice tana goge siririn hawayen ta da ta dade tana boye wa bata iya cewa komai ba


Murya na na rawa Nace ummah lpya kuwa ?


Ummah dan Allah kar kisa komai a ranki ki dena zubar min da wannan hawayen naki
..duk da duniya ya juya mana baya bazan rusuna wajen ganin farin ciki a fuskan ki ba..


Ummah nayi alkawari kuma na dauki alwashi duk inda halak yake zan nemo shi don na sa ki farin ciki a duniya
...ummah dan Allah ki dena kuka
Anan nima kukan ya kufce min na kife kai na ina yi.....




Musamman gani danayi maganan dana ke yana dada sa ummah na shiga wani irin halin tsumayi da rudewar tunani....


Ita kam dai tana shiru
A hakan ta daure ta shiga share hawayen ta a hankali ta dawo daf da ni ta kamo hannu na...
Tace"Saratu, kiyi hakuri saratu ki yafe ni...bawai na daga hankali na bane akan rayuwa abubuwan duniya ne kawai suke bani mamaki,rayuwa da ciwo sarahtu .sai dai duk da haka insha Allahu bazan dena kula da ke ba... duka duka ke kadai nake da shi a duniyan nan, kece abun alfahari na...nan tayi ajiyan zuciya tace
Allah ya baki lpya saratu
Kar ki damu dani kinji? Duk zan warware




Cikin sheshheka na dago zan yi magana ta sake min wani murmushi mai tarin nauyin zuciya tace in har farin ciki zaki bani ki daure ki cire komai aran ki saratu, ki dauka wannnan ba yin mu bane ba son ran mu bane,qaddar mu ne. Amma tunda yanzu mun samu kan mu tunanin abunda zamu yi mu tada rayuwar mu kawai zamuyi nan gaba.kinji?


Ba yadda na iya haka Na gyada kai da kyar ina kuka mai dauke da tarin takaici ,shiru ne ya ratsa wajen ummah ta shiga shafa ni gently tana bani karfin gwiwa batare da tace komai ba..




Haka nayi kwana anan gadon asibiti sai da na dan warke sarai sannan aka sallame mu


Ba laifi dukan mu muka soma sawa ranmu ruwan sanyi musamman fannin kau da nadama da koke koke duk muka bada hankali wajen nema makan mu mafita arayuwa ,ummah bata so na kawo wani magana game da komai sai na warke amma kowa da nashi a zuciyan sa kullum sai na saka na warware.


Cikin kwanakin anty sahura ita kadai take zuwa dakin mu wani bin tare da yaron nan daya taimaka ma ummah na.


kamar dai dukan su tausayin mu suke ji sosai duk dama ita bata wani nuna mana akan fuskan ta ..


Har aka sallame mu muka dawo gidan
Anan ne zamantake wa tsakanin mu da anty sahura ya dan fara samun fahimta..


don yanzu har akan gaisa a mutunce wani bin har abinci takan kawo min tace naci
Gashi ta bani rifa da skirt ummah na ta bata zani ya zamto muna sa wanda zamu na sauyawa


Hakan muke zaman mu a bariki zaman fadi tashi, Sai dai yanzu ummah na ke bada matsala


kullum sai naga ta bace shiruuu ta zurma kanta cikin wani irin yanayin kunci da tunani amma ko da na tambaye ta sai tace babu komai...tana lissafin rayuwar mu ne kawai..




Bayan wata guda lokacin har na mike tarwal jiki na ya dada bayyana wani sirrin girma kadan sabida abubuwan da suka faru dani har nonowa da kugu na suka dan taso sosai ba yabo ba fallasa ban rame ba..
Hasken fata na ne kawai ya rago.


Babban damuwa ko ince baban matsalar mu baki daya da ni da anty sahura shine ummah..


don kuwa sosai abun umman ta keyin gaba gaba shiru shirun umma ya soma daga mana hankali..


Gashi kullum a buga buga take neman kudi bata zama amma ko da ta tafi a kullum in banda zallan wulakanci da takaici babu abunda take karba wajen mutane


Munyi fama da Rashin sa'a kamar wanda aka mana mumumman baki Cikin kwanaki da abubuwa suka tsanan ta har anty sahura ta yafe mana biyan kudin dakin da muke ciki"
Tace kawai mu zauna anan din batare da wani fargaba ba sai dai dakin namu babu ko wutar lantarki,dama daga tabarma ne sai dan tsumman kayan mu da baifi kala biyu ba


Ni kaina da na fara tunanin ko tsaban yadda ummah take cin karo da mummuman rashin sa'a da takaicin mutanen birni ya ke sa ta wani yanayi amma sam abun yaki zama sosai araina..


Nasan Dole akwai babban abunda ke cinta a rai amma taki sam ta fada mana daga ni har anty sahura..


Ana cikin wannan yanayin matsin wata
Ranar da yamma bayan ummah ta fita nima mana abun sawa a baki, Sahura ne zaune akan dakalin kofar dakin ta tana gyaran farcen ta sai ga umman ta dawo


Fuska ba yabo ba fallasa Tace sannu da dawowa gambo,


Ummah ta sauke murmushin gajiya da tunani tace yawwa mutan gidan ne a tsakar gida
Nan Ta karaso ta dan zauna kusa da ita..


Murmushi suka maida ma juna as usual sahuran ta ce yau kuma me aka samo?


Tare da sauke ajiyan zuciya ummah tace ,hmmm bari kawai ni abun ma ya soma isana akwai wahala anan sannan har yanzu ba abunda na tara na azo agani...ace kai kenan sai dai ka samu na cin yau na gobe sai ka sake fita? Kai ni dai kullum ina fada rayuwar birni babu abun gani aciki sai tarin wahala..a gajiye take maganan kamar ba ita ba


Sahura Ta tabe tace ai ke ki kaga dama gambo, na sha gaya miki ki kyale yarinyar nan taje ta nema muku wani abun ko dan aikatau din na bazata rasa ba ,gata da kyaun fuska da kuruciya ba mai ki ya bata aiki,amma kina nan tsofe tsofe kin nace saam kin sa wahala ma kanki ga yarinya tana so ta taimake ki amma kinki...


Jin sahura ta fadi hakan yasa sai da taji wani iri aranta
'Hmmmm ummah ta sauke ajiyan zuciya.. abubuwan dayawa ke dawo mata arai


Tace sahura kenan,duk abunda nake gujewa kenan amma baki gani,wallhy bazan taba yarda yata ta fice cikin gari nan ba kam sai dai nayi ta wahalan har duniya ta nade..
Allah ya kiyaye ...uhm uhm


"Nan ran sahura ya dan soma baci she juzt wonder how adamant one can be bayan ga uban wahalar data ke sha,


Tace ni fa ban ma gane miki ba ne kwata kwata gambo,ke kince baki tare da mijin ki, to na yarkin fa? Ko shima baya tare da ita ne?...to wai mijin yarkin ne kike tsoron sa da baki so taje ta nemi na kanta ta rufa muku asiri ke ki dan huta,? Shi din ina yake da zai dau nauyi ba ya barki da wahala wai shin wani rin rabuwa suka yi ne? Wannan wani irin rayuwar wahal dakai ne kike yi ne gambo?


Ummah tayi shiru tana mamakin ta yadda anty sahura ta dau abun da zafi


bisa ga dukkan alamu Sun gaji ne da damuwa da yadda take wahalar dakantan ba dare ba rana ni kuma ina zaune a gidan bana komai..


Ummah ta dan murmusa tace haba haj sahura, miyayi zafi haka?


Ke dai ki bar wannan maganan ni na daukar ma kaina hakan kuma zan cigaba da nema har na dace,maganan yata kuma wannan ai rayuwar mu ce ke dai ki ci gaba da taya mu da addu'a kamar yadda aka saba..


A fusace sahura ta mike tsaye tace bazan taya ba, haba ke kuwa baiwar Allah
Ke yanzu a kwana biyun nan da muke zama daku wani irin yarda ne ban gwada miki ba? Ko ce miki akayi a irin halin da na tsince ku akwai wanda zai bari ku zauna masa agida ne baisan ku bai san asalin ku ba amma wai har ina baki shawara kina ki?


Toh wallhy in har irin wannan zaman da zakiyi dani kenan ki tattara ina ki inaki ki bar mani gida...


Anan hankalin ummah ya tashi don bata dauki abun yayi tsamari har haka ba ga sahura sai dada hawan diri take ta shake fuskan ta sosai..


Ummahh zatayi magana sahura tace, kinga baiwar Allah ki tafi kawai ni nafasa zama da ku kuje chan na fasa karban ko sisin ku ma na yafe kuje kawai ..


Ta juya a fusace zata bar wajen cikin rudani ummah ta riko ta " haba sahura yanzu akan wanannan maganan shine zaki ce haka dan Allah ki rufa mana asiri kiyi hakuri sahura..wallhy na yarda kin mana mutunci kinyi mana adalci fiye da yadda nazo na tarar da garin nan


Nan mah ta dan fashe da kuka, tace bansan ya zanyi bane sahura bazan taba barin yata ta fita cikin irin wayannan mutanen ba ,basu da tarbiya basu da imani gwara ni ayi ta cutar da ni da na kai yata ga halaka,..Allah ya isa tsakani na da duk wanda ya cuce ni...ta dada fashe wa da kuka mai taba zuciya...


"Ni kuma ina chan daki Da shike ana dan taba sanyi Bacci nake yi sosai tun bayan dan hirar da na taya anty sahuran so bana jin komai daga abinda suke fada.


Sahura na shiru tana jin kukan da ummah ta gurfana tana yi, a hankali ta dago ta tace haba wa gambo na san akwai
Dalilin da ya sa kike haka, nifa kika zo kika samu anan garin kuma ma abariki gidan shege da shegiya, ki dube ni da kyau nafi ki sanin halin rayuwa anan


Sai dai ban sha mamaki don kin ki ki gaya min asalin damuwar ki ba dama chan zaman duhu muke kin kasa gaya min komai akanki bare yarki. toh shikenan rike abun ki, gani gaki anan kowa zai gane ma idanun sa..sai dai ki sani duk randa tayi tsami dole zanji,kaiwa nan ta kama hanya ta shige dakin ta.


Anan ummah ta zauna tana jan hawaye,
Tana tuno da yadda cikin kwana kalilan sahura ta karbe su hannu bibbiyu cikin aminci da sauyawar hali,....


amma sam bata da burin tona sirin ta ma wani bare gane take bata yarda da kowa ba yanzun..
kuma gani take kamar in ta tada za'a tsangeme ni ko makamancin haka


Amma ganin yanayin Sahura dazin ya sa tayi tunani" wai shin meyasa ta damu dani haka ? Wai daman akwai masu tausayin mutum har haka ne anan?
Ko dan ni ma mace ce kamar ta ummah tayi tunani cikin nazari mai zurfi..


Bayan nan ta tashi ta shige daki, ta daga ni as usual labarin daya ne babu abunda ya sauya dan abunda ta kalato muka samu muka ci.


Bayan sallahr ishai muna dan hira sa ita mama sai na lura ummah bata cikin hankalin ta kawai jina take ina ta faman surutu, har sai wajen goma saura na kishingide kan tabarma nayi bacci na..


Bayan nan Ummah Waje ta fito,tasan tunda har yanzu akwai haske a dakin sahura to batayi bacci ba kenan tare da sauke ajiyan zuciya ta kama hanyar dakin sahurar....


Wajen shiru sai takun ta tunanin hukuncin data dauka aranta take yi anya abun da zanyi dai dai ne ?wani zuciyan sai yace mata muddin kina so ki cigaba da rayuwar ki dana yarki dole sai kin fuskanci kalubalen ki kin kuma sa wa ranki zaki iya da komai don cimma burin ki ..


Anan ta yi salam bakin kofa kusan minti 2 sannan sahura tace shigo daga ciki....


"Baki bude ummah ke binta da ido ganin yanayin Da ta same ta, bata iya daurewa ba tace
Sahurah? Me nake gani haka? dama kema kina shan wayannan abubuwan ne, tayi nuni da kwalaben codine da totulin akasa an sha guda da alaman zata bude dayan ne..


Sahura na shiru kuma bata sake hada ido da ummah ba, har sai da umma ta zo ta gaban ta suka fuskan ci juna "


kafin umma tace zatayi mata magana kuka ne ya dan subuce ma sahura mai sanyi da ban mamaki...


Cikin rashin fahimta da rudani ummah ,ta zaunar da ita ta shiga rarrashin ta hade da mata wa'azin a nitse cewar bata taba tsammanin Tana shan kayan kwalba ba?
Meye damuwar ta?


Sahura dake jimami ta dau lokaci tana jan shessheka kamar wata sabuwar amarya
,hankalin umma duk ya bi ya tashi ta cigaba da lallabata tana tambayar ta..anan sahura ta dube ummah tace babu komai kawai na tuno da duniya ne....
Cikin damuwa ummah tace habawa sahura, yanzu abunda zaki ce kenan ko dan nima abunda nake fada kenan zaki rama?


Ta ce ko kadan, kawai abubuwan ne dole wata rana zaka ga wasu wayanda zasu tuna maka da naka rayuwar kuma zai maka zafi..


Ummah tace haka ne shiyass nima na zo nan
Dan nagaya miki wacece ni, na yarda da amincin ki sahura kuma na yadda cewa bazan taba iya komai da kaina ba gani ba ilimi ga kauyanci babu kuma wanda na sani anan mai hali nagari na tausayi in ba ke ba


Sahura ta dago a sanyaye ta dube ummah tace ai ciwon ya mace na ya mace ne gambo,kar ki ga wai farkon zuwan ku ban sake muku ba.amma ni tun da na ganki jiki na ya bani kina cikin wani hali bazan boye miki ba ina tausaya miki sosai ,,,


anan ma kukan ya sake kufce mata cikin shessheka ta kuma cewa kuma kinsan Allah a duk sanda na ganku sai na ji kamar kuna tuno min da kaina ne da kuma halin da na shiga ciki a rayuwa adan wani lokaci...


Wannan abun shi yasa na kan sha wannan abun don na samu sauki arai na..


Ummah tace Allah sarki, sahura har akwai damuwar da tafi nawa kenan wanda har zai sa ki cutar da kanki ?


nifa a inda na fito wallhy shan kayan kwalba tamkar zunubi ne babba...
kiyi hakuri ki kwantar da hankalin ki komai na duniya mai wuce wa ne..
Baga shi yanzu kina zaman ki asiri a rufe ba


Anan ajiyan zuciya sahura tayi tace haka ne,
Don dai baki san wacece ni bane gambo, ko kina ganin akwai kwanciyar hankali ga wance ke zaune da tsinuwar iyayen ta ne?


Wani rasss ummah taji...sahura tace
Ni din na ma da kike gani daga kauye na fito, kuma ba wani karatu nayi ba,ina aji na uku a secndry aka min Auren dole bayan fyaden gangami da wasu yan shaye shaye suka min wajen tallar abinci da umma na ke daura min a tashan garin mu kowani yamma ..


Naki auren nan amma sam suka turje sai na aure shi, cewar su ai babban mutum ne ga shi da dukiya da rufin asiri.. yaya na harda min wa'azi akan na amince Ni dama Sam sam banyi karatun allon nan ba haka na amince da su..


"Gambo, nayi hakuri na zauna da miji na ..sabida ba yadda bai nuna amanan sa wa iyayen mu ba ,amma daga bisa ni kadai nasan azaban da na sha hannun sa...


Nan Ta bude ma ummah gadon Bayan ta wanda ke dauke da layi layi bakake da wasu patches suma sun dishe sunyi manyan tabo tace har yau bazan manta yadda mijina ke duka na ba, ya zage ni ya ci mutunci na,kuma yayi min gorin cewar sa ai ya sayi bakin iyaye na sun bada ni a banza...


Cikin tsananin mamaki da magiya ummah tace shine baki kai karar sa ba kin ga jikin ki kuwa sahura?


Cikin kuka tace,wani kara kuwa gambo? Ai gaskiyan shi ne basu ganin laifin sa don yana basu kudi yana musu alheri yana nuna musu ina zaman lpya da kishiyoyi na...


shiyasa kuma kullum idan na kai magana sabanin haka a gida ake ci min mutunci sosai wata rana ma har a korana ni da duka..haka nayi ta zaman kunci gashi yana da mata har biyu nice na uku


Ke Ban

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login