Showing 105001 words to 108000 words out of 194085 words

Chapter 36 - KUDI KUNBAR SUSA COMPLETE BOOK By Surayyams.txt

01 Sep 2025

1124

ta 300 ko 450vip ma 08060712446,ko ta acct 0152983148 surayyah muhammad suleh gtb.kuji tsoron Allah kubar masu shi

Sunday night kayan da hajya tayi oder suka iso bata bude kowanne ba se akwatunan laces datayi oder su a kamfani dan sune take sakaran zasu zamto idon zakara acikin kayan lefen da zasu hada
"Vicuna alpaca da cashmer fabric guda daddaya,se origanal handmade venetian laces da wasu irin shegun cord lace da materials masu beads da aka kawo daga kamfanin
Solstiss a france da aldo bianchi daga italy duk sunyi matukar kyau sosai dan bakaramin jin swavroski stones, bead,sequins and crystals sukayi ba

Ita kuma kayan data zata sa sophia hallete ce ta zabar mata acikin tulle and laces guda shida wanda aka kera su da glass buggle beads with heavy embroidery.

Hakama duk wani gwalagwalai da sauran abubuwan kayan lefe masu tsada wanda baza asame su nigeria ba duk ta kimtsa su.

Washe gari sassafe ta sauka a lagos daga nan sukaje sokoto state tare da aliyu domin a saka ranan tabbatarwa.

Aliyu Yana waya da abbakar amma kullum sai ya tsinci kansa cikin jin kunyar sa alhali abbakar din bema san meke faruwa ba.shi baima samu lokacin jud ba musamman dayaga kamar hamdiya tafi hamida kula masa da komai ayanzu.

Jud kuwa ta samu sabun habit daga an zauna zata sabule ta bar wajen taje ta kulle kanta a daki ita kadai in kaga tana walwala to anti hamdiya ce take koyamata abubuwa daga harkan data keyi na saida kayan mata dana qamshi, dan sosai ta kakkara mata turare da tricks na gyaran jiki duk dama ba hakan ta so ace suna rayuwar su da uwarta ba

Ranan Hamida tana zaune suna yar maganan su da hamdiyar Musamman akan watsar da lamarin yarta datakeyi a gidan kwana biyu

Hamidya ta matsu sosai tana tuhumar ta akan abubuwan daya wakana amma haka hamida ta nace wajen kare kanta dacewa babu abunda batayi ma jud ba babu abunda bata dora ta akai ba...Hamdiya tace amma ai baki jata ajiki ba,tace bazata iya ba ita batada lokacin haka bayan bata tara komai a duniya bane xata ja yarinya ajiki?wannan ma ai shashancine da rashib sanin ciwon kai..musun da sukeyi kenan sai ga sakon tex na waya ya shigo inda buguwar kirjin hamida ya dada tsanan tawa
Sabuwar sunan campanin ramat Wato "ramat royal oil and gas share holding campany saudi arabia.katin gayyata ne suke watsawa Ranar bakwai ga wata na gaban zasu yi babban hidima a babban hotel din masu kudi a america can las vegas inda akeyin caca.

Daga ganin an sauya ma hidumar tsari hamida tasan Wannan duk shawarar bilksu ne dan bilkisun ta tabbatar ma ramat cewa su bar maganan dawowa nija su baje basirar su suje america suyi partyn anan zasu hadu da masu kudin duniya daga china hawai turkey dubai qatar japan russia honkong kuma tana da yaqinin zasu goge harma ramar ta zo dede da mijin ta aliyu Kuma dama burin ta kenan.

Dan haka ta kara fadada shirye shiryen ta suka cillasa wani watan aka kuma kaisa babban hotel a america.

Har yau kuma bata daga wayar aliyu ba in tayi kkri ne ta amsa sakonnin sa dan har yau nuna masa take tana fushi da shi sosai ta hada harda kulle estate dinsa dayayi a saudi batare da cewarta ba

taso ace ya barmata amma kawai bazata iya sauke kai ta roke sa bane,tana so bayan duk abun datakeyi masan nan shi ya sauko ya bata hakuri sannan ya bata estate din kyauta Data ga alaman bazaiyi hakan ba seta kawai ta dada jin hausin sa aranta

Hamida dake rike da katin bata san lokacin data ja tsaki ba tayi ta sakeyi tana yatsine tuni taji kirjin ta na mata wani irin zafi,ai kamaar jira take hamdiya ta tambayeta meyaa faru kamar zata hadiye rai ta mutu haka ta dinga bayanai akan ramat cikin bacin rai tana nuna kishin ta a fili,rasa abun cewa hamdiya tayi ta yi shiru tana kallon bakin ta,har sanda abbakar ya kira tukun ta sarara
Tasa wayar akunne maganan minti biyar sukayi ta katse wayar ta mike tsaye tace aikin banza,shima tafiyar sa yayi yanzu ai da ya dawo munyi maganan tafiyar ko?
Gaskiya zan je wajen ramat ki ba wannan watar ba amma de dani zaayi abun nan...hamdiya tace kidaiyi tunani bata kulata ba tace jud..wai ina jud take ne?ani me aiki ce ta bayyana cikin tsawa da masifa tace ke jeki kiramin jud yanzun nan baban ta ya bani sako in gaya mata,hakri hamdiya take ta bata koda xata sausauto amma ina kamar wanda aka mata lefi hakan take ta kumbura tana kananan surutai

Mai aiki taje ta dawo kusan da rabin awa jud bata sauko ba aikuwa a matikar harxuke hamida ta haura sama a fusace da zimman zata je ta same ta anty hamdiya ma ta bi bayan ta babu wani knock hamida ta banke kofar dakin jud din inda sukayi ido hudu da ita tana kwance cikin wata kafurar shigar banza tana daukar selfies tana turawa a computarta

Tuni Jud ta rude ta mike zaune tana sauri sauri zata rufe computer ta da jikin ta,wani irin runtse idanu hamida tayi tsaban bacin rai
Da sauri kuma a masifance ta ta tureta gefe ta kwace comptr ta bude ta shiga dubawa..

Jud ta hau bari duk jikin ta ya soma rawa ta rasa meke mata ddi...muryan ta na rawa..tace mumy pls dont open kiyi hakri kar ki budemun wallh na shafa'ane jikin ta sai rawa yake sosai Allah y so ta ma aliyun ya sauka ne tace bari ta tura masa hotunan ta,Hamida tana shiru tana latsawa tun tana sake nishi cikin mamakin abunda take gani karshe ta karkace ta sakar masu ihu kamar mahaukaciya ta juyo a raunane ta fauce wayar jud daga hannun ta ta shiga dubawa dan ta dada tabatarwa

Kukan na shuga uku jud ta fashe da she dan batasan ya akayi ta sulale kasa tana rawan dari ba hakri kawai take bada hamida tana yarfa hannu tana dora hannu aka da alama yau tagama yawo...
Hamida kuwa se dada xurfi take tana karanta dukan sakonnun su hannun ta rawa yakeyi sosai ga wasu irin zafafan hawaye dake zuba mata na takaici da mamaki

Ganin abun is gting out of hand yasa hamdiya ta karaso to tunkan ta iso kan jud hamida tay jefa da wayar ta cakumo wuyarta ta da karfi cikin ihu da raxana da tambaya me firgirtawa ta shiga kifa mata maruka tana kwallo da ita

"tace jud kin cuceni dama abunda kikeyi kenan dan ubannki
karuwanci kika komawa yi agida na?da abokin babanki dan ubanki?When has this start....tell me,me kukeyi da aliyu are you sleeping with him?tsaban kaduwa da razana nunfashin jud kamar zai dauke ta shiga girgiza kai tana ihu tana kuka hamida tana faman mata jan mahaukata,tell me...yau sai kin gada min.. ta shiga daka mata tsawa kamar zata kashe ta,"dan ubanki ki fada min abunda kike yi da aliyu ko na kashe ki,Kin bashi jikin ki akan abun duniiya ko?
A tsananin raxane Jud tace ahh ma mmm ummmm am umna ummma dan Allah ki tsaya kiji,wani saukan maruka hamida ta sauke mata ta ko ina sanda hamdiya taji hawayen ta sun sauko ..in tsaya inji miki me..zaki renamin hankali ne bayan duk abunda nagani,cikin kuka hamida ta juyo tace hamdiya kizo kigamin abunda yarinyar nan takeyi,ta kalle jud tana share hawayen ta" ure sending ur naked pictures to ur dad...juuuuuddd"

Anty hamdiya itama ta share hawayen ta nan ta dau wayar tana dubawa itama batace musu uffan ba dan sosai taji ba dadi aranta

Kukan fitar rau jud take tana birgima

Hamida tana faman azalzala mata masifa cikin ihu...ohhh now i see shiyasa ya tula maki kayan duniya sabida kin riga kn basa jikin ki?daga jud ta budi baki hamida xata kikkifa mata mari

Hamdiya tayi sauri ta riko hamida baya tana danne ta cikin tsananin fushi tace ki sakeni wlhy sai tagayamin,me ban mata ba da zatai karuwanci me ban bata a duniya ba,Hamidya tace hamida calm down..
Tace dont tell me to calm down yarinyar nan ta cuce ni duniya da lahira kuma sena karkarya ki yau,jud tana ta kuka,fincikewa tayi ta jawo ta cikin kwakawaa da anty hamdiya dake janta tana fizgewa dukan ta hamida ta shiga yi ta ko ta ina tana kukan itama tana maganaganu ba abunda jud takeyi se ihu tana bata hakri
" umma kiyi hakri dan Allah umma baxan sake ba.ni wallhy banyi komai da shi ba wayyo Allah na anty hamdiya ki cece ni wayyo umma kiyi hkri

Hamida tace "Allah ya isa tsakanina da aliyu
ke kuma yau se na kasheki agidan na sekin gayamin wanda ya koya miki karuwanci nide bazaku kasheni kisamin hawan jinii
Ba.

Jud tayi laushi sosai har muryan ta bai fita Da kyar hamdiya tajanye hamida tayi waje da ita suka barta a dakkin..

Ita xafin dukan ma be dame ta ba
Ihu takeyi tana birgiman tuno me xai same ta yau in abban ta yaji wanan labari

***har daki hamdiya takai hamida ta xaunar da ita akan gado ta debo ruwan sanyi ta bata ta akan ta sha duk da haka ba shi ya hanata kukan ba tace hamdiya na shiga uku na lalace jud ta tona min asiri innallhi waailaihi rajiun...abokin mahaifn ta mijin aminiyata?.menene jud take nema a duniya haka ..yanzu duk damuwar da nake ciki arayuwa bai isheni ba seta karamin da wannan bakin cikin?

Me zance ma duniya,ramla zatace nice na hada wannan abun dan naci amanar ta..

Ni Ki ban wayata in kira abbakar kawai ya dawo yau din nan a hada ta da komawa waye ne suyi aure in dena ganin ta agidan nan

Wallhy bazata gurbata min rayuwana ta samin bakin ciki ba hamdiya na gaji da jud...na gaji fa lamarin ta koma miye tayi ni de yanxu babu ruwana da ita

Jiki a matukar sanyaye hande ta zauna gefe tana rarrashinta dn ta lura abun ya taba ta sosai kukan takaici da na bakinciki takeyi sosai har tana neman ficewa a hanklin ta

Pls calm down hamida,in baki nitsu ba bazamu san me zamuyi ba

Tace wallhy Ni nasani
Nasan me zanyi da jud kawai kuban waya ta in kira uban ta karma ya shiga jirgi dan baxatayi kwana biyu a gidan nan ba wallhy aurar da ita zanyi i dont care anymore

Hamdiya tace Jud fa yarki ce kuma baki da wata bayan ita"U dont care fa kikkace a yarki?look
U wont do anything now harse munji kan maganan nan ta bakin ta.

Please Relax ni zanje na daukota in yaso duk abunda ta fada se mu yanke hukunci akai but for now no phones calls kar ki kira mijin ki a wannan yanayin ai seki dora masa hawanjini Just relax ina zuwa ok

Da kyar hamida ta gyada kai ta rusuna anty hamdiya ta bude kofar ta nufo hanyar dakin jud,a kasa ta same ta ta hade kai da gwiwa se faman kuka takeyi kamar zata cire ranta har anty ta taho kanta bata sani ba,hannu ta dora akan kafadun ta a tsorace ta dago jajayen idanun ta

tace jud ki bar wannan kukan naki,ki tashu muje kibada mahaifiyar ki hakri...jud ta girgixa kai cikin shehka mai zafi tace ah'a anty ni fa bazanje ta kasheni ba,mesa umma bazata saurara ni wallhy ba abunda take tunani bane...Dady aliyu fa aure na yace zaiiyi

anty hamdiya tace will u shut up my friend,nace ki tashi muje gaban mahaifiyarki ki bata hkri... yanzu".. ta daka mata tsawa

Kuka ta dada fashewa da shi ta mike da kyar duk jikin ta yayi laushi fuskn ta yayi ja,tana tafiya tana kukan tana kukkunin zuci,itade abarta tana son aliyun ta.agaba anty tasata suka kai har dakin hamida tsaban tsoro ta koma baya ta rabe sanda hamdiyar ta shigo sannan ta biyo ta abaya abaya".
kallo daya hamida ta mata ta dauke kai fusknta a shake se kada kafafun ta take tana dada hawa, ido anty hande tayi ma jud akan ta je gaban ta ta bata hakir,da kyar ta je ta dan rusuna tana dan kuka tace umma kiyi hakri kuskure aka samu umma dan Allah ki saurareni zan miki bayani,amma dan Allah kurufa min asiri kar abba yaji maganan nan...
A zafafe hamida tace what?kar yaji?ai kamar ma yaji ina de auren kike so...ta girgixa kai tana tare hawayen ta a tsawace tace bayan aliyu se waye kuma kike tura masa tsaraicin ki?
Jud xatayi magana ta dungureta da karfi tace dont u dare lie to me,nace suwaye sexual patners dinki?who have you been sleeping with

ran jud ne ya baci sosai tanaji kamar ta kurma ihu komai ya tarwatse wani kara sautin kukan ta tayi ayayin da anty hamdiya ranta ya baci ta fara magana ma hamida da sautin fushi

"Shikenan yarinya bazatayi magana ba?wannan wani irin abune

hamida ta mike tsaye har jikin ta na rawa tace bazatayi ba me zata gayamin?what she did is enough hamdiya..wallhy senayi ma Aliyu rashin mutunci ke kuma aure zan maki gobe goben nan bari ubanki dakike jin tsoron yazo..

Jud tana kuka sosai tace mumy meyasa bazaki saurare ni ba
I have my xplanations wallahy. yanzu shikenan bazaku saurareni ba zaki gaya ma abba na yamin aure,ni ban tabayin iskanci da kowa ba

Wani wawan mari hamida ta sake mata a fuska sanda ta gigice ta kwala ihu.anty hamdiya ce ta raba tsakanin su da sauri tace wai kashe ta xakiyi? hamida wannan wani irin zuciya ne.

tace i dnt knw...ni ban taso agaban iyaye na ba amma banyi karuwanci ba so banga dalilin daya da yata zatayi ba
..she Have nothing to say gobe zanje in nemi aliyu sena yaga masa rigar mutunci kema dan ubanki se kin gaya min sauran yan iskan mazan da kike bi anan Jud ta fusata kwarai cikin kukan me zafi tace umma ni bana karuwanci ni ban taba yi,daddy aliyu ne yace yana so zai aure ni kuma nima ina son shi,umma bantaba kwanciya da namiji ba i swear
I swear u swear..

Pls Na rokeki karki bata ma dady aliyu suna wajen abbana
Ai ni nace xan tura masa hoto shifa baice in tura masa hoto na...umma in baki saurare ni ba bazaki gane komai ba,we really lov each oda kuma ni shikawai zan aura..

Cikeda da mamaki da masifa hamida ta hayayako zata bugeta tace nace bazan saurreki ba,i care not abt ur lies..munafukar banza wawiya kawai...just wait till tomwr in naje nagama da aliun nan ne zaki san baki da wayo...Now will u get out of ma room?Jud ta runtse ido ta wani irin jan numfashi

tace i said get out....

Tace umma baxaki saurareni ba?
Xaki rabani da ddy aliyu batare da kinji ba?umma kimun adalci ki saurare ni.
Nasan nayi kuskure but I truly love him

Yadda take maganan da zuciya da taurin kai ya sa hamida ta birkice da fushi a fusace ta yunkuro xata kamo ta ant hamdiya ta riko ta tana me hadiye nata dauriyar

Tace Kice mata ta bace min a daki nace aliyun baxai taba zamowa saarki ba yar banza yar iskan yarinya get out

Jud ta kalle anty hamdiya cikin wani irin yanayin kuka me tafe da zucia tace
She is sending me away she is always sending me away bazata taba saurarar abunda zan fada mata ba,i said iv neva slept with a man,i love daddy aliyu kuma wallahy bazan rabu da shi ba sede in kasheni zatayi..

...xatayi magana anty hamdiya tace
Get Out jud nace ki barnan...seta fice da gudu tana me rusa ihu.KKSPls inbaka biya ba karka karanta game bukatar sayan littafin ya turo katin mtn ta 300 ko 450vip ma 08060712446,ko ta acct 0152983148 surayyah muhammad suleh gtb.kuji tsoron Allah kubar masu shi_
[7/11, 6:54 PM] SURAYYAHMS: _KKSPls inbaka biya ba karka karanta game bukatar sayan littafin ya turo katin mtn ta 300 ko 450vip ma 08060712446,ko ta acct 0152983148 surayyah muhammad suleh gtb.kuji tsoron Allah kubar masu shi_

48: *** kuka hamida takeyi sosai harta nemi waje ta kwanta tana kanyi dan arayuwan ta dade bata shiga wannan yanayin ba.

Anty hamdiya dake tsaye akan ta duk ta rasa abun da zatayi sai da tayi shirun minti goma sannan ta sauke ajiyan zuciya ta taho ta zauna agefen ta cikin sautin magana me sanyi amma a sigar fada da nuna rashin jin dadi tace hamida mekenan kike aikatawa?anya kina cikin hanklin ki kuwa?da yar cikin ki kike sain sa meyayi zafi shi ba wuta ba..whats wrong with tsayawa da warware wannan matsalar meyasa zaki na dukan ta kamar jaka ita ba yar cikin ki bane?please who doesnt make mistake shikenan zaki ruining life dinta gaba daya dantayi kuskure guda?what if tayi wanda yafi wannan.
Kuka hamida ta dada fashewa da shi anty hamdiya tace Hamida,nasan akwai abunda ke damun ki na daban ba jud ba ,amma shawarata shine karki saukar da fushinki da frustration dinki akan yarki dan nan gaba kece zai dawo miki...U knw Ure frustrated deal with it mana let the girl be Tunda bazaki saurareta ba,ke yanzu bakiji kunya ba,ko bakiji me tace bane.."ita wallahy baxata rabu da shi ba sede in ko kashe ta xakiyi?to ina amfnin wannan abun fusabillahi.
Can u pls calm down hamida

Mikewa daga kwancen hamida tayi tana dan share hawayen ta,tace hamdiya naga alaman baku gane komai ba game da yadda nakeji,
Im hurting so much nikadai nasan zafin dake cina ayanzu,im done for....yarinyar nan ta cuce ni.
She ruined my life meyasa baxan dake yar banxa ba naso yau da a asibiti ta tsinci kanta..kuma wallhy ta sake furta maganam aliyu agabana sena mata dukan mutuwa agidan nan

"Anty tace Subhannala hamida what is wrong with you

Cikin kuka tace evrything hamdiya.

Jud is my only child bazan iya misalta miki burin dana dora akan rayuwar ta ba,i want her to be decent, have a good life. .Bana so namiji ya raina ta,ta rasa abun da zata sakamin da shi shine ta tura nonowarta da jikkn ta ma namiji?wannan ai tsantsar karuwanci ne

Anty tace pls
Stop judging her

Pls dont tell me to stop,kudi na gaba daya akanta nake kararwa,tana ganin yadda inna take zagi na akan tarbiyan ta,mahaifin ta bai taba min da sauki ba akanta..har kudi ya biyani har yarjejeniya munyi akan kulawa da yarinyar nan yanzu me zance musu?

Nd aliyu...mijin ramla ne fa babbar aminiyata na rantse
Miki

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login