Showing 144001 words to 147000 words out of 194085 words

Chapter 49 - KUDI KUNBAR SUSA COMPLETE BOOK By Surayyams.txt

01 Sep 2025

1167

ta da kyakkyawar murmushi suka gaisa a mutunce

Safiya tace ta sauko hajiyar aliyu ce take neman ta,cike da bata girma tace to anty safiya ace ina xuwa

Safiya tana barin wajen jud ta bude wardrobe ta dauko wata hadiyyar red three grt voile veil ta yafa shi akan daurin zara buhari datayi,da kyau da tsari ta saba jelar mayafin akafadarta bakaramin azaban kyau da kwarjini tayi ba,bata bata lokacin komai ba ta sauko abun ta,tun daga kan step tana takowa aliyu ya tsare ta da mayukan idanun sa yana matukar yaba kyaun halittar ta,yama mance da cewa magana yakeyi ma hajiy ya yanke,tana ta cewa eehem ehem,ina hankalin sa ya tafi yawo shaf bai wajen ta,abun ya dameta ta dan leka taga abunda yake kallo cahraf sai suka hade da jud tana karasasowa ciki.

Itama kallon ta bita da shi,ta shigo a nitse agaban hjiyar ta soma durkusawa ta gaida ta da harshen fullanci hjya tana ta murmushi cikin tsananin karajin son ta tana saka mata harda albarkan ta

Wani sassanyar rausaya jud takeyi cikin sanyin tafiyarta me daukar hankali tanayi tana bada control ma dukan langwasar dake jikin ta cikin kwarewa kamar tana nuna ma hajiya dirin halitar da Allah ya zuba mata ne

gaban aliyu ta koma ta rusuna gaban sa cikin nuna matukar girmamawa da darajawa ta gaida sa tana masa ina kwana,..wani marar kunyar murmushi yake sakar mata dan bakaramin faranta masa rai behaviours dinta na kimanta shi yake yi ba,"ta masa murmushi ya kwantar da muryan sa kamar ba shiba yace kin tashi lpya,taki ta amsa da dan sauti sabida ta bashi impression din kunyar hajiya datake ji,a hankli ta dago idanun ta suka hade ido aliyu kamar zai sume wajen kallon murmushin datayi masa,har ta tashi ta koma gefe ta xauna kasa kusa da hjya bai daina binta da kallo ba,hjya ta kau da kanta tanata murmushi.

Ta lura tun da jud ta shigo wajen aliyu ya rage magana hira kadan zakaga idanun sa akan matar sa,yana jin yadda suke hira cikin yare da hjyar sa kamar uwa da ya abun na masa dadi shidai kunya kunyar dake tsakanin su shiyafi komai burgesa.

Ga nan dai jud karamar yarinya amma babu yarinta a maganganun nata sabida sosai ta nitsu ta san iya abunda yake fita abakin ta..dan koda wasa ne bata yarda ta furta abu cikin rawan kai

Kallon ta kawai yakan sanyaya ma hjy binta bakincikin ramla dake ranta bare aliyu dayake matukar xumudin ta duk dama yasan ya mallaketa.

Ramat tana nan tana kan jan lokaci ta dauka kafin ta fito xata samu sunyi fushi ta gama bata musu rai but unfutnatly sai ta samu bahakan bane

Tun saukowarta da daga sama taga sunsa jud a tsakiyar su sunata hira harda dariya

Wani abu taji ya cakke ta ji tayi kamar zata haukace dan haushi

Mayafin dsta yafa kan nityn wanda bai gama rufe saman nonowrta ba ta ja sallamar ma ciki ciki tayi musu tana tafiya tana wani boucing tana dage kafada cikin shan qamshi

Ragwaf ta nemi waje a kujera ta xauna ta daura kafa daya akan daya babu wanda ya kulata bare su tanka wani faduwar gaba jud takeji...

a fizge ramat Tace ina kwana..

Wajen ya dau shiru,aka rasa ma waye ta jefo gaisuwar karshe hjya binta ce ta daure ta amsa da lpya batare da ta sake fuskn ta ba

Shiru ne ya ratsa wajen,bata ko kalle aliyu ba..

Bakinciki ya dame hajy aranta amma hakan ta danne dan yau bata so arabu ba a cimma manufa ba..tayi gyaran murya tace to alhamdull Tunda Allah ya tara mu anan,bawani abun boye wa tsakanin mu kunsan ku ba yara kanana bane,nan ta fara da aliyu ta masa nasiha sosai tace aliyu kaine babba dole ne zakayi hkri ka kasance me adalci da kyautata ma matayen ka,haka dai ta dan kwakkwso waazi ta masa ta sanya masa albarka tukunna ta dawo kan ramat da jud atare take musu nasihan tare da jan kunnen su akan abunda ya faru jiyan,tace jud kece karama saiki bita sau da kafa yi bari na bari,ki tuna itama tamkar uwace agareki in bakiyi me kyau ba tana da dama ta gyara miki so kar ki bari shedan ya na shiga tsakanin ku
Jud ta amsa a nitse

Hjy Tace shi aure kamar qaddarace ramla ki amshi jud matsayin abokiyar zaman ki,yarki kuma yar aminiyarki kuyi zaman amana ko Allah zai bamu ladan zamunci muna fatan Allah ya sanya albarka

Kowa yace ameen ramat ta doka wata kakkauaran tsaki

Atake aliyu yace ke lpyarki kuwa?ta mike tsaye cikin hararar su ranta abace

"Aikin banza ni za'a aje ana gayamin maganan banxa bayan ancuceni?

Hjya dake danne zuciyarta dan yau kwata kwata bada niyyan masifa ta zo ba,tace meye haka kuma ramla ashe duk abunda nagama gaya muku yanzu ke bai shiga kunnen ki ba..

Wani gatsine tayi tace yo me za'ace min?hjy tsakaninki da Allah kiji fa me kike cewa wai ramla ga amanan yarki yar aminiyirki,kuma kishiyarki,ke in aka miki wannan walakancin zaki amsa ne,koni ne dakika tsana zakice inyi zaman kishiya da yar cikina auren cin amana duk an hade min baki,koda shike ba a ganin laifin kowa sai nawa dama da ya auroni ai ba sona kuke ba in dai adalci za'ayi ai aliyu bai kyautamin ba,amana ta yaci..nidai wallhy zan dau mataki yarinya ta shiga tsabgata sai na hallakata agidan nan

A zafafe aliyu ya yunkuro zai tashi yayo kanta hjy ta daga masa hannu

Jud tayi shiru bata koyi yunkurin dago
Kai ba .

Ba yabo ba fallssa hjya tace habawa ramla,da girmanki zaki na firta irin wayannan kalaman abunda ya faru ai ya riga ya faru,in fa Allah yace jud matar aliyu ne ba boka ba malami sannan babu wani masifar da zai hana auren nan zama

Wani garasssss ramat taji saukar maganan,kamar da biyu aka cakka mata wani kazamin fushi taji tana neman rufe mata idanu..

A zafafe tayi maganan ta gatsau cike da raini tace

"Eh za'a gaya min haka mana, sabida ansan banda uwa banda uba,ai da ke akayi wa haka bazakice hakan ba,hjy kyace mun kezaki iya zama da yar wannan yarinyar ce kina shiga dakin miji itama tana shiga?

a tsawace aliyu yace enough..sai tayi shiru hjya bata kula ba ta kalle jud, dan ta dada kular da ramat seta mata magana cikin yare," tace yata tashi ki shiga ciki zamu tattauna da yar uwanki,sai akara hakri sannan duk abunda ya sameki karki bata lokaci ki kirani kifadamin,jud tace taji,sai ta mike tsaye tace Allah ya kaiki gida lpya mamah hjy tayi karamin murmushi tace Allah maki albarka jeki ki huta kici abinci sosai akunyace ta gyada kai tasa kai ta bar wajen abunta

Hakan da sukayi agaban ramat bakaramin kona mata rai yayi ba,kuncewa ne kawai ya rage mata dan sosai kanta yake hayaki.

Fixgewa tayi zata bar wajen a zafafe aliyu ya ruko hannun ta wani faucewa tayi ta tsala masa ihun data saba,ya tare ta da tsawa"wai me haka?hauka kike ne,ta fashe da kuka tace namiye zaka rikeni ai kun gama magana kaidin baka da laifi ne,nice me lefi,da ka auro yar aminiyata bacin amana na kayi ba mesa baxa a baka lefi ba nice marainar wayo za adake ni a hana ni kuka,bazan rike ta amana bazan saurari kowa ba tunda rashin adalcin ku akaina zai sauka wallah yanzu xaka soma gani

..hjy ta mike tsaye bata rike ta ba tace ramla can u please calm down,ya kike abu kamar karamar yarinya ko sai ta rainaki ne xakishiga hanklin ki,cikin kukan tace eh din eh din ta raina ni mana ai hakan kike so,banda walakanci agabana xakuna zagina da yare?kodan anga bana ji ai dole,dama can an gaya mata an tsaneni dan ta rainani da kyau mekuma za'ace me min tsakani da Allah

banda wulskanci da cin zarafi me aliyu yamin tunda ya dawo?ai yasan yamin lefi wato shi yafi karfin yaban hakuri ko,harda mari na fa yayi hajya,agabanki hamida ta sa shi ya kaini caji offis dan kawai a walakantani yanzu se in zauna ana zagi na da yare walla baxan dau raini ba

..hjya tace o o dama damuwarki kenan?to aini ba zaginki nayi ba,infact mutunci nake so naja miki shiyssa na sallame jud ta bamu waje,ko ke atunanin ki zata ji tsoron ki ne bayan taga yadda kika raina mijin ki,nima uwar sa kike neman ki raina ni,inda kin saurareni..Hakurin nima nazo na baki
Abunda kikayi jiya sam ba mutuncinki bane, Ai sede neman raini kuma,narasa wani irin girma kikayi ramla ke gashi kina tunkaho kina buga kirjin cewa ke babbace baxaki zauna da karaman yarinya ba amma tunda yarinyar nan ta shigo gidan nan kike aikata aikin yaranta,ai nasan bakijin dadi aranki
Its normal ai Ni na fahimce ki nasan auren nan bazai miki sauki ba sabida nima mace ce,amma saiki duba aure al'amarin Allah ne jud ba itace mace na tara da aliyu ya aura ba?ai in ba matar sa bace duk xaki gani Allah dakansa xai dedeta.
But i dnt get this ur madness me kike so ki nuna mata?

Ramla ashe baxaki nitsu ki tarbi qaddararki kuyi zaman lpya da juna ba?

Wani kukan makirci
Ramat ta fashe da shi mai karfi
,tace Nide an cuceni,xubar da mutunci na nawa aliuu ya riga ya zubda mun mutunci tunda ya auro yar cikin sa..

.Hjya ta kalle sa tayi masa alaman ya rarrashe ta duk dama ba har ranta ba,aliyu ya miko hannu zai riko hannun ta ta fauce yace kiyi hakuri ki xauna,ta cigaba da kuka hjya ta riko kafadun ta da kyar ta amince ta zauna tsakiyar su aliyu ya rufe idanun sa ya shiga lallabata a gaban hjya yana bata hakuri tana bankadewa,gashi ba daman cakkar su da bakar magana sun riga sun sauke mata kai sunki suyi xuciya.. rasa abunyi tayi dan dolen ta ta saurare abubuwan da suke furtawa

Yace mata xaiyi iya bakin kokarin sa dan yaga bai sake kuntata mata ba
Kuma baxai bari raini ko tashin hankli ya shiga tsakanin su ba

Tace sam..sede ya mata alkawrin bazai dinga sako hamida cikin hidamar su ba
Acewar ta baxaiyu hamida taxo tana mata mulki akan aurenta ba ai dashi kawai take surukan taka ita babu ruwan ta,so in yana son ta hakura dole ne ya dakatar da ita wjen shiga hidaman su

Anan hjya binta seta goya mata baya,for the first time in her life tace ma aliyu yayi hakan.
Ta kuma ce masa hakan ne kawai zai kauda fitina tsakanin su.

Ramat taji sauki sauki aranta hjya ta dada ja mata kunne akan ta rike girman ta na babba anan kam batayi musu ba

Bayan tafiyar hajya suka dawo suka xauna a falo yana ta lalallshin abisa umarnin mhaifiyar san sai wani yauki take,tana jan jan aji ta tace dashi ai yakamata ayi magana yau yau din nan dan kowa yasan matsayin sa a gidan nan sabida bana son abunda zai zo ya bata min raina

Yace ok kamar me kenan?tace kamar yadda xa'a gudanar da xama a gidan nan ko ahaka zamuci gaba da zama?bazaka fa min wayo ba ai tun sati biyu daya wuce kaci angoncin ka
Kawai araba magana kowa yasan iyakar sa.

Yace ok in kirata kenan?ta watsa masa hararan kasar ido tace a'a abari se da yamma in anzo dinner,ita me ta sani game da gidan nan sai na gama tsara komai za'ayi magana

Baice mata uffan ba ta mike ta barshi zaune awajen baisa tunanin komai aransa ba daukar remote yayi ya kunna tv abunsa yana canza channel bai bar wajen ba sanda aka kira xuhr tunda ya fice sai bai sake dawowa ba sai bayan ishai
[7/31, 2:29 PM] SURAYYAHMS: *59*
Motoci biyu ne suka rako su aciki har da na hajya binta bulama wacce ta nace sai itace zata kai jud har cikin dakin mijin ta..

Saukan dirin motocin su a harabar gidan shi ya birkita ramat yasa ta kasa zama dan tunda akace mata su aliyun ne suka dawo taji gaban ta yayi mummanan fadi zuciyarta na harbawa wani ziriyar bakin ciki ta shigayi tana kaikawo ita daya..
Tashin hankali ne ya tasa ta a Gaba gaba daya ta rasa me xatayi.
Cijewa tayi ta danne haukar ta ta haura sama site dinta da sauri ta dauko car keys da waya tana saukowa a birkice tana lalubar number bilkisu,dede zata shawo kan step kenan taga wulgawar masu aiki anata kaikawo da kayayyakin su zuwa sashen jud, labewa tayi tayi tsam dan ta gane ma idanun ta,aliyu ne ya soma shigowa da sallamar sa yayi matukar kyau kamar yau ne ranar auren,abayan sa hjy binta ne ta riko hannun jud inda ta dakatar da ita tun daga kofa ta mata aduoi sannan ta umarce ta akan ta shigo da kafar dama sannan tayi bismillah,a idanun ramat akayi duk wayannan tana kallon su har suka lume suka bar wajen,cikin sauri ta sauko a haukace a fixga ta fincike bakar pradon ta tayi gaba.

Gadon jud irin manyan royal bed din nan ne black nd purple colour wanda yaji tsaddaden off white bedings,Har kan gadon hajiya ta aje ta ta sake mata nasiha musamman akan zaman hakuri sannan tayi mata seda safe ta fito aliyu yana biye da ita abaya

Hirar su sukeyi har suka iso tsaka da babban falon gidan tace Aliyu wai ina ramla ne?..baka gaya mata yau zaku dawo da yar uwanta bane,in bazata gaishe ni ba ai tazo ta karbemu,tun kan aliyu ya amsa se ga safiya ta sauko da tray,har kasa ta rusuna ta gaishe su a girmame nan ya mata tanbayar da maman shin tayi,tace masa ai yanzun nan ramat ta fice

Hjy binta da dama ba har ranta tayi tanbayar ba tace toh agaya mata gobe zanzo kowa ya kasance yana nan...

Daga aliyun har safiyan suka amsa mata da to,babu yadda batayi da shi ya koma ya same jud ba amma haka yaki fir yace ai bai gaji da ganin ta ba dole ne ya sake rakata har gida,ranta baiso ba amma hakan ta barsa suna tafiya suna hira tun hirar biki,har cikin ranta yau taji dadin ganin aliyu dan ko ba ace komai ba annuri da kwanciyar hanklin daya dade da juya musu baya yau ya soma fallasa akan fuskan sa,cike da godewa Allah take amsa dukanin hirar sa,a dan hutun sati biyu kawai dayayi amma sai taji kamar ba aliyun ta ba..

Ramat bata tsaya ba, tuki take tana huci tana hura hanci karar wayarta ya katse mata tunani,ta dauka azafafe tace wai kuna inane?sukace sun ganta ma ta tsaya a inda take xasu karaso,parking tayi ta gyara ko minti uku batayi ba saiga wani katon jeep yana mata signal cike da manya manyan mata lukuta lukuta su biyar kowacce cikin shigar marasa mutunci dan kwalin su kaf daurin ture kaga tsiya suna wani taunar cingam kamar kilallun karuwai,sun manyanta amma babu me mayafin arxiki a kafadarta

ganin su kawai ya sa tsumin ramat ya dada harbawa
Daga drivers seat bilkisu tayi sliding glass tace muje

wani wawan taka mota sukayi ajere kamar wanda zasu tashi sama har suka iso gate din bulama mansion

Pim pimmmm pimmm a mugun rude mai gadi ya taho ya bude muusu suka shigo kamar sun iso filin yaki,rikif suka diddiro booth aka bude kowacce cikin su ta dau dorinan ta mai kauri mai baki biyu,kowa anan sanda gaban sa ya fadi dan tsoro,..haka duka matayen nan suka taso daya bayan daya su biyar ramat da bilkisu suka cika su bakwai basu tsaya ko ina ba dai shashen jud
.
Jud kuwa dama tun fitar su aliu ta yaye mayafin ta ta diro kasa,tana kare ma sabon dakin nata kallo dan komai da aka saka ya matukar burgeta

Kirar su anty zakiya ne ya maidata kan gadon,hira sukayi sosai kowa yana nata sannu da dawowa katse wayar ke da wuya taji an wani banko kofar dakin ta da karfi wasu mayukan kan bulalu ne suka soma mata welcome

A razane ta sake wayar ya fada kan gado,tana dagowa ta soma ganin kattan mata marasa mutunci suna layi bisa sawun juna suna shigowa mata daki,rassss gaban ta ya fadi tsabar tsoro bata san sadda ta haura tsakiyar gadon ba

Bilkisu ta kare ma dakin kallon yatsine da walakanci ta buga wani wawan ihu da shewa,ehehe hehe ayyururi banci dala ta dadi ba inji yar gidan makwaidata

wannan ce tsinanniyar amaryan taki?

Azafafe ramat tace itace fa...

Wasu zafafan harara suka watsa ma jud ayayin da sauran matayen suke faman zagaye ta da mayunwatan idanun su kowacce ta rike bulalar ta,ramat se fixge numfashin ta take cikin bunkassa
Da tsananin jin kishii,"jud ta bata rai tana matsawa da baya baya,

Tace"keeeee,ramat ta daka mata wata muguwar tsawa tana nuna ta da yar yatsa sosai jud ta tsorata ta kara dunkulewa tace dan ubanki da uwarki baki da kunya kika aure min mijina?a rude jud tace nidai kufita min dan Allah
Buga ma gadon dorina daya daga cikin matan tayi wanda ya sa jud kara rudewa ta kai hannu a rude zata dau wayarta bilkis ta kwace wayar ta yar

ramat tace ina magana kina magana?.
,dan uwarki waye xaki kira yazo ya cece ki,ai kin sayar ma kanka jaraba dan ubanki tunda kince dani xakiyi zaman kishi,ashe baki da kunya dan ubanki da uwarki mijina zaki aura?ni saar kine...wani Kuka jud ta fashe da shi muryan ta na rawa tace nide kufice min wallahy
Bana so...

Azafafe ramat ta daka mata ihu akan ta,tace ai sena kashe ki..ta cigaba tana azaxxalan ruwan masifa wasu xagin ma jud bata taba jin su ba,tace ai tunda baki da wayon cema uwarki a'a, to ni zan koya miki ba mai fitar dake a gidana se mutuwar ki kuma ni nan zan kashe ki ...

ku babbankare mun ita inci uban ta Bakince miji na zaki auraba to ga welcome party,aikuwa rututu mata suka fara jawo kafafun jud ta tsala ihu ta shiga fingicekwa tana tututtura su suna jan ta tana zansu,wani wawan zana ramat ta kai mata zut a jikin ta

Jud tace wayyo na shiga uku wayyo Allah na

"Sena kashe ki da bakar azaba a gidan nan,mayya karuwar yarinya nafi karfin ki nafi kafin uwarki ta sake kai mata zana ihun balai jud takeyi tana kiran aliyu Aliyu,gaba daya gidan ya dauka da ribibin ihun su

Onlyy god knws waya kira aliyu cikin masu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login