Showing 147001 words to 150000 words out of 194085 words

Chapter 50 - KUDI KUNBAR SUSA COMPLETE BOOK By Surayyams.txt

01 Sep 2025

1160

aiki tuni se ga horn din motar sa ya shigo gidan a gurguje

Kokowan ceton rai jud ta shigayi da su tana kauce ma dukan da ramat take kai mata wai ahaka din ma sotake in ta gama zane tan sai ta bada kawayen ta dama suma su hadu mata lilis

Gaba daya suka birkita dakin da ihu da masifa da zage zage da kyar jud ta kwace a hannun su ta koma can dungun tana tsaye tana kuka sosai

Baki ga komai ba,dan wallh gawar ki xaa futar agidan nan,waime kuke jira ne akamomin ita ban gama ba

Babu imani matayen suka haura zasu kamata jud ta sake tsala ihu tana kai masu hannu ta ko ina tana kiran aliyu kamar ranta zai fice

Arikice ya shigo gidan dan tun daga falon farko yakejin ihun ta da surutun su..

ma'aikatan gidan kowa ya futo yayi tsege tsege cikin damuwa,aliyu yana banke kofar ya same su sun kamo ta sun mata muguwar kamun ina za'a saka ga ramat da dorina a hannu tana huci,a firgice cikin tsawa yace what? subahanallah,mena ke gani anan,sunajin muryan sa suka sake ta,a firgice ta wawuso gudu cikin ihu ta fada jikin sa ta tsala masa ihun dayaji har tsakar kansa

A mugun fusace Yace get out..ku bace min agida na nace..marasa kunyar banza..yan iska,sum sum suka fara fita ji yake kamar zai yi amon wuta tsabar zafin da kirjin sa ta keyi

Tattaba jud yake a birkice yana tanbayarta tana ta rusa kuka duk jikin ta na kyarma

Ramat dake jin kanta kamar zata mutu tayi saurin tare kofa tace ina zakuce,ai bamu gama yau sai na kashe yar munafuka a gida na,a hatsale aliyu ya ture jud ajikin sa tun kafun ya waigo matayen suka ture ramat a tsorace sukayi waje,a mugun zafafe muryan sa har na rawa yace security,security,ganin ransa yayi mugun baci yasa bilkisu ma ta bi bayan su ta fice,security suna isowa ya hausu da dirin masifa yace in aka bar matayen nan suka kwana lapya bai yafe ba,cikin su yana rawa suka fuce sukayi arresting din su kaf aka fita da su

Ramat tasa mai ihu ta daka tsallen mahaukata tace macuci azallumi mayaudari, waima me xakayi?akan wannan karuwar zaka walakanta min kawaye na, tace tabbb bura uban can aliyu kawaye na zaka daure?.. aliyu,ko kulata baiyi ba,ya nufi inda jud take xai riko ta ya rarrashe ta a haukace ramat ta raruko aguje ta sha gaban sa,baka isa ba,ai abunda kanema kenan kuma yanzu ka soma gani maci amana mayaudari kawai,me zakaji ajikin wannan yar cikin kan in ba dan kaso ka wulakan ta ni ba


Se na kashe ta da azaba wallhy,sena kashe ki ta juya a haukace zata dungure jud shikann sa aliu baisan yadda akayi ya kifa mata wani zindikin mari ba,ta dago jajayen idanun ta zata yi masa magana ya sake daura mata wani kakkakrfan marin dayayi karar tassss saida waje ya dau wani shiru

Ramat ta dauke ji sakamakon toshewar da kunnen ta yayi kwakwalta ne ya dakata daga aikin sa na kai sako wani dishi dishi take kallon sa, ransa a matukar bace ya bankade ta ya dauko jud ya maidata kan gadon ya rungumota jikin sa sosai yanaji kamar ransa aka taba

Da wata kakkaurar tsaki ramat ta dauke kanta akan su Cikin wata iriyar slow motion me fallasa zafi da kunan rai ta ce Aliyu ka mare ni?

Bai amsa ba ta dada harzuka Xata sa masa ihu,dan har tayi tsallen bori da alaman zata hau fashe fashe da sauri ya sake jud ya damko hannun ta a walakance sukayi waje tare da ita,ihu takeyi tana zage zage sena kashe ki da azaba,na rantse da Allah gawarki za afutar agidan nan
Munafuka yar munafukai damgun karuwai makwadaita

Wani shiru gidan ya dauka tsaban tashin hankali

Aliyu Yana shiga site din ya ya wurga ta a floor a tsakiyar dakin ta yana me fetsar da numfashin sa ,da gudu ta taso a haukace ta shake gaban rigar sa,tasa ihun bala'u tana zage zage,inka isa kafita a dakin nan shegiya aka haifeni
Macuci marar adalci Allah ya isa tsakanina dakai aliyu,sai naci bura uban yar makwaidata se ta gwammaci mutuwar ta da zama dani,ransa yay koluluwar baci huci yake yana kallon ta da mahaukatan jajenyen idannun sa

Kamu daya yay ma hannun nata a wuyar sa ya watsar
Xata sake kamasa ya kifa mata mari

A matukar tsawace yace
"Keeee...ki nitsu

"Baki da hankali ne?are u mad..wani rawa takeyi karkar hawayen zafin kishi sun gama wanke idanun ta,ta kalle sa tace aliy..u yace dont u dare call my name,ashe ke mahauckaciyace ban sani,whats all these zaki tara mun mata yan iska kina mun zage xage a gida na, kashe ta zakuyi?yarki ce ko baiwa na kawo maki

Tace bansani ba,aikai zakayi bayanin wacce ka kawo min dan ni bansan ta,kuma wallhy da bakar azaba xata bar gidan ka.

Yace ohhh baki san ta bako?to jud abbakar ce yar gidan hamida aminiyarki,frm now on kisa cewa she is ma wife kishiyar ki...

Yanke kukan tayi cak,wani Dariyar mahaukata ta fashe masa da shi tace" Aliyu yar cikin hamida yanzu bakaji kunyar furta wannan kalaman ba?

aliyu ka cuce ni,se ta fashe da kuka me tsananin kara..Allah ya isa mun,dama tuntini nasan ka tsane ni ba zaman Allah kakeyi da ni ba baka daukeni komai ba In ba dan ka shirya kuntatamin ba ai baxaka saye kan hamida da kudi dan ta juya mun baya ba

Yace whaeva,naga zan iya ne..kudi ina dasu abanza,auren yarinyar ba haramun bane,koda dukan dukiyata nasa na siya kan uwarta da shi babu ruwanki, so nake in mallake ta kuma soyayya kadai ke kawo hakan..and dont push me to d wall

Ta rarumo aljihun rigar sa muryan ta ns rawa tace ehh lallai ma butulu,katon banza kawai..yoo nawa ka bada hamidar kafadamin mana inba tsoro ba,ni zan ruba mata a kunce auren nan dan wallahy bazan zauna da yar ciki na agidan nan
Ba xaka kwanta dani ka kwanta da yar ciki na,kai waye haka da zaka walakanta ni,wato dangin ka da suke kankartar dani bai isheka ba shine kaima xaka goya musu baya ko

To wallhy Dakai da hamida sekunyi dana sanin auren nan,baka dauremun kawaye na ba?sai ka shirya daureni nima,wallahy duka kam yanzu ta fara shan shi a hannu na...sena karya mata kafa da hannu sena makantar da ita

bata hankara ba taji an finciko ta an mata wani irin matsa wani wawan hadiyar yawu tayi,yace inkika sake dukan ta abakin auren ki ramla,tace what?a tsawace yace u heard me.. ko bakin gyalen ta kika taba ban yafe miki ba duk ranan da kika sake dukan ta wallhy sena sakeki,and u better relax now or park ur things and leave..

" cikin muguwar raxana da kaduwa Tace what?a daskare take kallon sa se taga kamar ba shi ba,he sound damn serious ransa a matukar bace yayi maganan

A...aaliyu..kace mene?ni ramla in barmaka gidan ka.
Aliyu walakanta ni zakayi,duk akan auren?..oh na manta ka hade kai da makirai munafukai wanda basa son ganin cigaba na,no wonder dan na zauna a estate dinka a saudia kasa aka kwace,Baka ga rashn adalcin da kake min ba ko?koni ba mutum bace,amanata kaci,ka siya kan kawata da kudi, ka raba ni da hamida,aliyu yar cikin ka auro min,auren ma baka sanar dani ba.wayannan duk ba zalunci bane aliyu

Yace eh in hakane zalunci awajen ki save it..
Ramla ni bansan me zan miki ba
Tun kan kibar gidan nan nake shan axaba wajen ki
Kin tafi harkan ki watannin ki fiye da biyar,... five gud months ramla,what do u xpect?na zauna maki...koni ba namiji bane,ce miki akayi babu jini ajiki na?

Azafafe Tace amma aiba yar hamida ce maganin matsalr ka ba...ai Ba yar cikin ka zaka auromin ba,in abbakar ne ya haife jud, ai kai sa'ar abbakr ne,mesa zaka tozarta ni haka aliyu meyasa..

Yace bcos ure not sorry for what u put me tru,tunda kina iko dakanki,nima ina da iko da kaina,kuma ita nagani nake so,in kece kika haifeta nagani ina so,in Allah bai haramta min ba sena aureta, am not a fool.. dont u dare take me as one..kibar haukan nan naki ku zauna lpya ko wallahy kiyi dana sanin sanina a rayuwaki,in har zan bada kudi in mallaketa to kisani babu abunda bazan iya yi in kika bata min raina ba..

Zatayi magana
Bai jira ba ya fizge jikin sa yayi waje

A guje ta biyo bayan sa,tana xage zage tana cewa seta rama,seta walakan ta shi,baxai taba samun kwanciyar hankali ba seta kashe jud,yaki ya kulata ta gama haukar ta ta fada kasa a falon gidan tana rusa kuka

Kukan takaicin kanta,tace kash kaico ai da ta san akan gindi ne kawai zesa aliyu ya kara mata aure wallahy da ta biye ma hamida tana dawowa time to time tana bashi

Duk a tunanin ta shege na nan,ai zaina taimaka mata akan asirin data mammasa

Little did she knw that,mu'amalar sa da inna yana daya daga cikun abunda ya sakwarkwata karfin sihirin ta ajikin sa,dan sosai ake sadaka da saukar qu'ani da al'qunut a sabun masallacin almajirn daya gina musu kafin ya aure jud, to shikan sa baima san ana wani abu makamancin haka domin sa ba.

Shidai kawai ya bari a auren jud ne ya sauya masa komai
Dakin sa ya nufa ya calming kansa dan yana da zuciya sosai Kafin ya fito yaga shol babu jud agidan yana kira layin ta ya tsinci wayar akasa shikadai yana kara

Wani sabon tashin hnkali da tsoro ne suka rufe sa nan da nan ya bude bathrum ya duba shiru yana bude wadrobe yaga kayanta cif cif,yace to ina take?atake kansa ya soma bugawa kirjin sa ta hau barin wuta tana masa wani irin zafi

Tuno da fatima yayi kawai yaji kamar kafafun sa baxasu dauke sa ba,a daddafe ya sulale kasa, sanda yay tsugunon minti talati sannan ya fice ya same ramat tana kan bori,yace mata ina jud take?ta masa shiru tana watsa masa harara ya daka mata tsawa a birkice itama a tsawace ta mike tace ban sani ba,ni banganta ba kuma kar ka sake tambayana ita,...kamar xai fashe ya kalle ta baice uffan ba ya shiga xaga gidan yana kiran sunan ta
Kowa yace bai ganta ba,kansa ya rike cikin tsananin fargaba yana furta innaliahi wa inna ilaihi rajiun,..

Ramat tana lura da hakan tayi sauri ta haura site din ta,tana ta zagaye ita days ta rasa waxata kira suyi murnan batan tan tare,duk dama bata san ina jud din take ba.

Ta sa key ta kulle kofarta bata fito ba sai can karfe uku na dare ta samu wai aliyu baya nan,tun daxun ya wuce neman jud acikin dare.

Wajen maman sa ya nufa da tashin hankalin,gashi dare ne yayi ta kirar hamida bata dauka ba,ganin yadda ya firgice ya damu hajiya binta ta saka masa kuka,yau kam tasan in har abunda ya faru da fatima ya maimata kansa akan jud ba shakka dan ta zai shiga gararin rayuwa

Da kyar asubahi tayi musu,ya kira wannan ya kira wannan gashi ko masu gadin gidan ma cewa sukayi basu gan ta ba

Fannin jud kuwa jin aliyu bai dawo bane yasa ta dau mayafin ta ta sabule jiki ta isa can bakin titi ta hau napep ta arce gida,Allah ya so abbban ta bai gari ta shigo shiru kamar munafuka
..lpya lau ta yi sallama a babban falon su suna hade ido da hamida ta fashe da kuka sosai

A tsorace hamida tayo kanta da mamakin ganin ta cikin dare tace meye,kukan me kikeyi waya taba ki,ina aliuun
Jud bata amsa ba ta fada jikin maman ta ta cigaba da rusa kuka,hankli tashe hamida ta shiga dudduba jikin ta tana kwala kira hamdiya,hamdiya da sauri anty hamdiya ta sauko jin sautin kukan jud a tsakar gidan ya sa ta kara sauri tayo kansu a raxane.
Tace subhanallah jud Jud..innalillhi hamida me aka mata take kuka,rai abace hamida tace oho gata nan tamin shiru yanzu ta shigo tana kuka,taki tamin magana

..fincuko ta anty hamdiya tyi tace waye ne ya taba ki. ina aliyun?

Cikin kuka mai tafe da shesheka jud tace yana gida

"To kukan me kikeyi
Me aka miki,ramat ta taba ki ko?me tace miki,ko ita ta koraki?

Tace ummma... umma.. wasu mata ta debo dayawa suka zo suka bugeni

Cikin gwalo idanu Anty hamdiya tace duka?

"Dauke numfashi chak hamida tyi tace mene,suka bugeki,nine zan haifa ma ramla jaka?

A mugun xuciye ta fixge xata fita anty hamdiya ta rikota

Tace hamidiya li sakeni yau Sena ci uban ramla bata san da wa take yi ba yata zata buga?
Anty hamdiya tace relax hamida tsaya muji kan labarin

Tace Ke jud,shi aliyun shi yana ina suka zo din?.

Ba gargada jud ta shiga basu labarin komai daya afku,hamida se huci takeyi tana tsuma da kyar da karfin bala'i anty hamdiya ta danne ta.

Duka suka taru suka rarrashi jud sanda tayi bacci suka dawo falo suna tattaunawa


Da asubahin fari jud ko wanka batayi ba taga anty hamidya akan ta,tace muje inkaiki gida mijin ki ya damu sosai

Jud batayi musu ba ta dau mayafin ta sanda suka fito tace
Ina umman ta,anty hamdiya tace ta riga mu isa,muje xaki same ta acan

Gidan aliyu straight
Suka shigo jud tana fitowa maza aka kira shi aka gaya masa ta dawo,har yar zaxxabin daya rufe san tas yaji ta sake shi baijira hajya ta idda salla ba ya hau motar sa ya nufi gida

Jud tana ta kallon anty hamidya da mamaki dan sam batayi tsammanin hamshakan bulalu bane ne ajakar ta sanda suka shigo tace inane site din wanda ta bige ki?

Dake iri daya da nata ne sai bai bata wahalan ganewa ba,

Ramat tun da ta fito cikin dare taga aliyu bainan tayi kwanciyar ta hankli kwance koba komai ai ta watsaar da su,dan ba damuwar ta bane ma tasan ina jud take

Dede 6.54am lokacin bata farka ba ta hangame baki tana ta shakar sanyin AC dama bata sallan safiya bare ya dame ta

A dakile anty hamdiya ta bude kofar jud tana biye da ita,tace wannan kafurar ce ko,jud ta gyada kai,anty hamdiya ta kamo fuskan ramat cikin baccin ta daura mata wani hargutsatsen mari nan danan ramat ta bude ido a gigice tunkan ta shiga hayyacin ta anty ta nemi dede mala malan cinyar ramat da suka kwaye ta sake iya karfin ta ta xabga mata dorina,ihun firgita ramat ta tsala wayyo Allah na waye xai kasheni,ba kakkautawa anty ta rinka zuba mata xana tana tambayar jud duka nawa ta miki,ba kunya jud tana amsawa.. wani hamshakin kokawa suka kaure da shi,

Har waje suka sauko ramat tana sose sose tana zagin ta dan bakaramin zanuwa tayi ba,motar aliyu yana shigowa sega hamida da female inspector,zuwa tayi ta hada nata makircin ta daga ma polisawa jarfan bala'i,nan ma tayi waya da comissioner of police agaban DPO tace ga ramat tace xata kashe mata yarta babu gaira babu dalili

Ai Babu tantama suka yarda da furucin ta musamman da akabi kan case din su bilkisu da kawayen ta dake daure a bayan kanta

Hanklin aliyu ba karamin tashi yayi ba yana gaishe da hamida ta share shi ta daure fuska,ga wani axababben sautin ihun dake fitowa daga cikin gida,tun daga kan matakale suke kokawa ramat tana iya bakin kokari taga ta dan kwace bulalar ta rama anty amma hamdiya bata sake mata ba sanda taga kowa ya shigo ana kallon su

Da sauri tabar mata bulalan a hannu taja baya ta boye jud tana masifa kamar su aka neman doka,wallahy baki isa ki kashe ta ba,"

Ramat da babu wayo bata ma gane me aka shirya mata ba a mugun zuciye tace sena ga bayan ta,sena kashe ta.

Tayi wuf xata xana musu bulalan inspecta ta hauro da gudu ya cafke ta ta kwace bulalar ta yar a mugun xuciye,tace let go off me.. jud tana ganin aliyu ta fashe da kukan munafurci anty hamdiya ta kamo hannun ta suka sauko...

Aliyu ya rasa me ke masa dadi se kallon kowanenn su yake,

Ran ramat ya matikar baci ga radadin zanan da taci yana mata rairayi duk jikin ta na mata wani irin xugi,idanun tane sukayi jaxir har suka sauko falon

Inspectar tana jan ta itama tana janta,tace Allah ya tsine miki hamida tirrr da rayuwarki na kwadayi,Allah ya tsine uwar da xata siyar da gindin yarta dan abun duniya,shikenan burin ki ya cika kin wargaxa mun gida na,kin juya ma miji na kwakwlawa..to wallah yanzu muka fara,shareta hamida tayi kamar bataji me tace babu mutunci tace inspecta kinji da kunnenki wallahy yata ta mutu ku zan kama

Aliyu ya tattara sauran karfin ikon sa yace wai meke faruwa,ya dan dube jud yace jud ina kika je?hawaye kawai ta sauke bata dago kanta ba.
KKS is not free its 300 access via 0152983148 surayyah muhammad sule gtb or 08060712446
[7/31, 2:29 PM] SURAYYAHMS: *60*.....ya sake memeta tambayar Jud xata amsa shi hamida ta katse su dacewa hamdiya shiga ki tattaro min kayan ta bazata zauna anan akashe ta ba,a tsarge aliyu yace hamida?hamida pls dont do this,ta bata ranta sosai tace wallhy aliyu in kaga yata bata bar gidan nan ba to an kulle wannann shegiyar ce dan duk wanda yace zai kashe min yata bana wasa da shi,dariya ramat ta fashe da shi irin na mahaukata hamida bata kulata ba..ko kabari aje station a bincike uwargidan ka akan kalamanta na kisa akan yata ko yanzun nan na tafi da yata gida

"ramat tace toooooo aliyu uwarka tayi magana sai ka amsata,kasa a wakalan ta matar ka sabida ka auro yar gidan makwadaita wuuu anji kunya,aliyu yace enough ramla tace bazan yi shiru ba,akan wannan yar zakatsaya ana walakantani shikansa comisonern saiya gamu dani dan babu wanda ya isa ya hanani kashe ta wallhy

..yace baxaki dena furtawa ba,ta sake furta wa abun ta,ido ya ma inspecta ta damko hannun ramat xatayi waje da ita a hargitse ta kai mata duka wani fixgar bala'i takeyi

hamdiya tana rike da jud,ramat se zagin hamidar takeyi, anty hamdiya dataga abun ba mutunci nan ta ja jud suka haura sama taje tana rarrashinta

Da kyar aliyu ya samo yar abaya aka sama ramat akayi masa waje da ita kafin nan gidan ya samu sarari,ya matso xaiyi magana hamida ta daga mai hannu,cikin bacin rai tace aliyu ba haka mukayi da kai ba,akan me xata bugar mun ya,kashe ta xasuyi,in har

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login