Showing 99001 words to 102000 words out of 268365 words

Chapter 34 - Tana Tare da ni complete book document .txt

29 Aug 2024

54135

yadda blue eyes na Anas suke kallonta.


Da kallon ya isheta se kawai ta mik’e be ce da ita komai ba illa binta da kallo da yake, wajen coffee machine ta nufa ta had’a masa sannan ta kawo ta ajiye kusa dashi. “Sir it seems kamar yau wani abu na damunka take this, it might help.”,Ita Fannah acewarta tunda in ita batada lafiya yana nuna ya damu itama bari ta mayar masa da kulawan in return sede kamar yadda tace ba’a gane halin Anas.


“Banaso!” yace da zafi. “Jeki zubar banaso!” Ya fad’a a tsawace dayasa ta firgita. Me tayi ne da Mr. Fauzi baya san coffeen ta yanzu?
“Mik’o min bottle d’aya a fridge.”
Shaye shaye again! Ita abinda bata so kenan, mesa Mr. Fauzi zena shaye shaye. “Mr. Fauzi shan abunnan baida amfani please kadena”
“Bakida right na fad’a min abinda zanyi pass me a bottle.” Bata ko motsa ba “now!” Ya daka mata wani irin tsawa bata san lokacin da ta je ta d’auko masa ba. Hawaye take sosai, ganin ya bud’e bottle d’in kawai ta juya bayanta shima koda yakai baki seya kasa sha ya rasa dalili. “Damn it!” Ya fad’i a fusace tare da wurgi da kwalban tatas! Ya fashe a k’asa. A firgice Fannah ta juyo ganin kwalban ya fasa taji dad’i sosai a ranta.


“Sir take the coffee please” d’agawa tayi daga kan table d’in ta mik’a masa kallon cup d’in yake yana nazarin ya karb’a ko kar ya karb’a. “Ka karb’a please.” Hannu ya sa ya amsa tare da kaiwa bakinsa, kurb’i daya yayi kawai seyaji duk damuwansa sun gushe, abinda ko giyansa ma be tab’a masa ba. Atleast in giyan ne seya d’au kamar minti uku daga baya ma yazo seya kusan minti goma saboda yadda jikinsa ya saba dashi. He really missed her coffee like crazy be cire daga bakinsa ba sanda ya kurb’d duka.


“Should I make you another?” Ta tambayesa kai ya kad’a mata.
Amsar cup d’in tayi taje ta ajiye kan fridge sannan ta kama hanyan fita. “Miss Aleeyu ina zakije?” Ya tambayeta cikin sanyin murya kamar bashi ya masifeta yanzu ba.
“Zanje in d’auko mop ne daga janitor’s closet (inda ake ajiye tsintsiya, mop da sauran kayan share dotti) in yi mopping wajen chan.”
“Leave it cleaners zasu yi taking care of wajen just don’t go.”
Wai meke damun Mr. Fauzi ne yau? Mafarki yayi ne yake tsoron a barsa shi kad’ai ko meh? Dawowa tayi ta zauna kan kujera duk lokacin data d’aga ido se suyi ido hud’u da Mr. Fauzi kallonta yake ko kyafta ido baiyi. Bata kuma d’aga ido ba se chan, tana d’agawa kuwa taga har yayi bacci kan table d’in. Through out jiya beyi bacci ba as se tunanin abinda Shettima ya fad’a masa kan Fannah yake ga kuma a gida ya kwana bareyi yayi shaye shayensa ba.


A hankali ta mik’e ta nufa wajen nasa biron dake hannunsa ta karb’e a hankali yadda barata ta dashi ba tare da arranging kan table nasan tasa komai in place kamar ranan yau ma taga littafin data soma karantawan. “Mr. Fauzi” ta kira sunansa. Bacci yake me k’arfi ko jinta beyi ba. “Mr. Fauzi da ka tashi kaje d’aki ka kwanta, kwanciya anan ze iya haddisa maka ciwon baya.” Nanma shiru be amsa taba. Hannu ta gwada waving a fuskarsa taga ko motsawa idanunsa basuyi ba alaman bacci yake me k’arfi kenan. Littafin ranan ta kuma cirowa takai kan page data tsaya ranan se b’ari take amman kaman aikin dole takasa ajiyewa karantawa ta soma dukda tasan yin hakan haramun ne.


_From the day Ummimi left us, my family was turn apart. You made me your son a drunker. Why do you have to leave? Why must you choose another guy over your family? Why will you have to bring back Angel (Amal) 8 months after leaving? Exactly a day after birth. Why are women cruel? Ummimi I’ve loved you but not now again, I’ve cared for you but not now again. I will never set my eyes on you again, God bless Ummi for caring for us just as her own kids. I hate you! Don’t ever come back. I promise to avenge for my family and I for what you did to us on all women of your kind. I promise to cause heart break and attack to 100-200 women so they will feel exactly how it feels to be abondoned. Only these three women I promise not to hurt, Ummie, Amal and the girl from the other night._


Mamaki ne da tausayi ne yacika Fannah. Allah sarki Mr. Fauzi ashe ba laifinsa bane duk abinda yakeyi yau, laifin mahaifiyar sa ce, mesa to zata barsu? Ashe saisa yake san Amal kamar ya mutu saboda bata sha d’umin mahaifiya ba. Allah sarki, gaskia duk sun bata tausayi, su nasu ba tafiya Baba yayi ba rashin lafiya ne amman seji suke duk ba dad’i time da jikinsa yayi worse bale nasu suna ji suna gani mahaifiyarsu ta tafi ta barsu. So wannan ne dalilin dayasa bayan ko wani kwana uku-hudu yana breaking up da ‘yan mata ashe ramawa yake. Shine dalilin da yasa baya mutunta mata kona misqala zarratun, amma dukda haka da besa shaye shaye aciki ba, ba abinda shaye shayen ze masa in banda sake b’atar dashi da yayi hak’uri ya rungumi k’addara.


Next page ta juya zata karanta a yayinda Anas yaja wani dogon numfashi hannunta na b’ari ta mayar ta ajiye se bugu zuciyarta yake. Dudum! dudum! Sede Anas ya ganta lokacin da take mayarwan amma be gane me take ajiye wa ba ko files ne ko littafi be sani ba dan daga bacci ya tashi.
“Me kikeyi anan?” Ya tambayeta.
“I... I.. I” tama kasa magana. “I’m sorry” tace daga k’arshe.
Idanunsa ya sake mayarwa inda yaga tana ajiye abu seyaga diary’n sa wajen, take mood d’insa ya canza danko Shettima da Amal bai barinsu su karanta.

“Diary na kika maranta?” Ya tambayeta daga jin muryarsa a san he is angry. Shiru tayi se b’ari take. “I’m talking to you!” Ya fad’a a tsawace.
Bata san lokacin data fara hawaye ba. “Sir I’m sorry.”
“How dare you! Ke bakisan ba kyau karantawa mutum sirrinsa bane?” Kuka harda me sauti take dan yadda yake magana a fusace a kuma tsawace.
“Am talking to you! Mesa zaki karanta min diary?”
“Sir I’m s.. So..” Bakin ta b’ari yake tama kasa magana. Ita kanta tasan itace da laifi batasan wani gulman yasata karanta masa diary ba, kodan halan ta damu dashi ne tadamu da shaye shayen da yakeyi, tana san ta gyara masa gurb’arcacciyar rayuwar dayake living zuwa daidaicacciyar hanya. Batasan taga Mr. Fauzi na shaye shaye musamman ma data karanto kad’an daga cikin sirrinsa.


Kuka take sosai wanda har ya soma damun Anas. Sekace ba shi ba, in akoi me san ganin Fannah na kuka be wuce Anas ba amman banda yanzu, bayasan jin kukanta. Sekuma yaji ba dad’i mesa ya sata kuka? “Me aciki dan ta karanta diary na, maybe tausayi na fara bata and she wanted to help, the problem is banasan help nata banaso.” Handkerchief yaciro daga aljihunsa tare da mik’a mata. Kukan take bar yanzu ba makawa, “wipe off your tears” yace ba tare da ya kalleta ba. Amsa tayi a hankali tayi kamar yadda ya buk’ace ta sede har yanzu bata bar raira kukan ba.


“For goodness sake kukan ya isa. You passed the line banasan ana min shisshigi kema kin sani.”
“I’m sorry” tace a hankali.
“Ya isa you can go.” Hak’uri ta sake basa sannan ta fice. “Huh!” Numfashi yasaki “God what is wrong with me? Koda Amal ce ta karanta min diary nasan zan mata worse than this, firing Fannah ya kamata inyi amman nakasa, koda banyi firing nata ba yakamata in bata punishment na intruding min datayi amman nakasa, se wai ma taban tausayi naji banasan kukanta. Naji wai ma nine da laifi dan sata kukan danayi. Oh God no! I’m not in love I’m not.”



*© miemiebee*


beeenovels.mywapblog.com
[12:51, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •°
°•°
*TANA TARE DANI...*👫


❣🎀❣🎀❣


*_written by miemiebee👄_*

In dedication to *Aunty Sis💕*
4⃣1⃣








Haka har da aka tashi Anas be sake neman Fannah ba. So yake ya nisantar da kansa daga gareta as possible enough as he can, saboda ya soma ji kamar maganganun Shettima gaskia ne. Saboda when it comes to Fannah he is weak abubuwa dayawa take masa wanda yaci ace ya koreta koya hukunta ta amman seyaji bare iya mata komai ba. Yasoma yarda eh he is feeling something for Fannah amman ba love bane tausayi ne kawai, yana tausayawa mata sede ko daya tambayi kansa tausayin me take basa yakasa answering. Fannah is his weakness.


Fannah kuwa dad’i taji da be sake nemanta ba dan da wannan kayan kunyan da tama kanta na masa shisshigi harda karance diary’nsa bata san da wani idan zata sake kallonsa ba. Ita abinda yafi bata mamaki ma shine yadda Anas yabata hanky wai ta goge hawayenta bayan abinda ta masa, shin meke damunsa yau? Ta d’au atake zeyi firing nata kokuma ya mata wani abu makamancin haka amman seyayi sab’anin abinda take expecting. He is acting wierd yau, bata tab’a ganinsa haka ba shida yake fad’in kukanta bai damunsa segashi yau bayasan ji.


Hanky’n ta ninke tasa cikin jakarta sannan ta mik’e tare da rufo k’ofar ta dan ganin lokacin tashi yayi. Ta rufe k’ofar office nata ta juya kenan sega Anas shima yafito suna had’a ido tayi saurin kawar da kanta. Public elevator tabi a yayinda Anas ke binta da kallo so yake yace mata ta zo su shiga elevator’nsa amman kuma girman kansa bare bar sa ba, wai mesa ma yakesan su shiga elevator’n sa bayan abinda ta masa d’azu? Sanda ta b’ace sannan ya nufa nasa ya shiga shima, kafin ya sauk’o kuwa tuni Fannah ta k’ara mai. A d’an wani shago ta tsaya tare da yima family’nta d’an siyayyan kayan k’walama. Isarta gida keda wuya.


Mutane biyun data gani tsaye cikin gidansu ne suka mugun razana ta. Ido wuru wuru ta zaro tare da dafe k’irjinta tana me salati a zuci. “Baffah Khaleel?! Ya Farouq?!” Kai tasoma kad’awa danko bata yarda da abinda idanunta suke gane mata ba. Mami dasu Afrah dake tsaye gefe guda suma fuskarsu d’auke yake da damuwa.
“Mami dan Allah kice min basu bane, tell me idanu na wasa suke min.”


“Fannah manyan gari wato har gidan TV ake nuna ki, ‘yan matan nawa fa duk sun girma sosai tunba Fannah surikata ba.” Cewar Ya Khaleel yana wani murmushin mugunta.
“Kai Farouq baka ga matarka bane da baraka mata magana ba? Jeku gaisa mana.” Wani tantirin dariya ne a fuskar Farouq a yayinda ya soma takowa gaban Fannah. Baya tayi take ganin haka “Fannah mata ta ya haka kuma? Mijinki ne fa ni, bekamata kina min haka ba, matso mana mu gaisa.” Sosai Farouq ya sake girma yazama cikakken na miji yanzu kyansa ya sake fitowa, sede iskancin nan nasa daya saba har yanzu yana yi be bari ba.


“No don’t touch me.” Kamar kyaftawan ido Mami tashigo tsakaninsu, “Ya Khaleel meh amfanin haka dan Allah? Nasan kai da d’anka kunfi k’arfin mu dan Allah kuyi hak’uri ku koma inda kuka fito. Fannah bata san Farouq Ya Khaleel kayi wa Allah ka hak’ura da kai da d’anka dan Allah.”
“Maman Aiman kenan, in kinga mun koma Bama toh wallahi da Fannah ne. Wace karuwar ‘yarkun ma wacce ko martaba battada, dan ni da Farouq zamu rufa mata asiri zaku wani tsaya kuna mana tsiya yau shekarunta nawa takasa yin aure, ba d’a na mijin da ze amince ya auri Fannah inba Farouq ba.”


“Baffah Khaleel dan Allah kayi hak’uri ka rufa min asiri banasan sake komawa Bama, banasan Ya Farouq ni na rungumi k’addara zan gama rayuwata duka ba aure dan Allah kar ka aura min Ya Farouq.” Fannah ta fad’i hawaye na gangarowa kan kumatun ta abin tausayi. Tajima bataji tashin hankali kamar na yau ba. Ta riga da ta ajiye past nata a gefe mesa su Baffah Khaleel zasu dawo su hargitsa mata komai??

“In baki son shi to shi yana sanki sakariya kawai, aure tsakaninki dashi kuma farillah ne nan da ‘yan watanni, gomma tun wuri ku fara shiri, karatu ne Farouq yayi. Yanada diploma’nsa dakuma aiki me albashin da ze iya rik’eki. Kinga ko wannan karan ke zakiyi kayan d’akinki tunda kema kinada aiki. Abinda ya kawo mu dama kenan, bayan biki zaki bi mijinki Bama ku fara zama acan, in qaninan ya tashi ku gaishesa. Farouq mu tafi.”


“A’a Baba ni ba yanzu ba semun gaisa da matar tawa tukuna.”
“Karka damu akoi gobe ai, gobe zaka dawo har girki seta maka tunda matar kace, mu tafi.” Nan suka fice. Kuka me k’arfi Fannah ta rushe da. Mami na bata hak’uri haka Afrah da Aiman ma. “Mami ni shikenan Ya Farouq zan aura? Duk inda mukaje se sun tsakuro mu. Mami dan Allah do something wallahi banasan Ya Farouq mugu ne, azzalimi banasan sa Mami.” Ta k’ara shigewa jikin Mami tana kuka me tsuma zuciya.
“Yi shiru Habibti in shaa Allah baraki auri Farouq ba kamar yadda Allah ya k’wato ki kwanakin baya haka ma ze miki yanzu mu dage da addu’a kawai.”


“Ya Fannah kiyi hak’uri zamu tayaki da addu’a” cewar Afrah cike da tausayi. Kuka sosai Fannah takeyi haka yadda taga rana taga dare ta kasa bacci. A ranan kowa hankalinsa tashe yake basu san kuma ina zasu sake zuwa ba, basu san ko in sun bar Maiduguri akoi inda zasuje Fannah tasamu aiki me kyau kamar na nan ba. Baba ya tausaya wa ‘yarsa sosai ba kuma abinda yafi bak’anta masa rai kamar in ya tuna ba abinda ze iyayi ya cheto ‘yarsa daga halaka. Dan auren Farouq halaka ne yaron da besan darajar mace ba ko kad’an, d’an giya d’an iska.
Daga Fannah ta rufe ido seta soma mafarke mafarke ganin ba mahilicci se Allah ta tashi tayi alwala tariga nafilfilu har seda k’arfinta ya k’are sannan tayi zaman istighfaar. Da safe ta tashi tana shirin office sanyi sanyi kamar wacce k’wai ya fashe ma aciki duk Afrah na kallonta takasa koda ce mata uffan dan tausayi. Mami ce tashigo ta tarar da ita tana sa kaya bayan gaisuwa Mami ta tambayeta cike da tausayi “Fannah ba se kinje office ba yau ki huta”

“Mami gomma inje saboda zama anan ba abinda ze haifar min inbanda bak’in ciki jiya Baffah Khaleel yace Ya Farouq ze dawo yau, bana san ganinsa Mami na gwammaci naje office.”
“Toh shikenan Fannah Allah kare kicire damuwa daga ranki kinji? Muna nan muna kan miki addu’a.”
“Nogode Mami ni na tafi.” “Allah kare” both Mami da Afrah suka mata sannan ta fice.


8:01AM daidai ya mata a office na Mr. Fauzi kanta sauk’e a k’asa ta gaishesa, sama sama ya amsa. Jakarta ta bud’o tare da ciro hand kerchief daya bata jiya ta ajiye kan table nasa. “Gashi, nagode.” D’gawa yayi ya sake mik’a mata “na baki keep it.”
“But Sir-” katse ta yayi “I said keep it” yace a hankali. Amsa tayi tare da masa godiya ta mayar cikin jakar ta.
Har yanzu basu had’a ido ba dan kanta a sunkuye yake.


“Ina schedule d’ina na yau?” Ya tambayeta yana danne danne a laptop nasa.
“I’m sorry bansamu na had’a ba excuse me yanzu zanje in had’a maka.”
“Mesa? Me kikeyi tun jiya da baki had’a ba?” Ya tambayeta cike da tsiwa.
“I’m sorry” tace nan ma bata d’aga kai ba sede daga yadda take maganar Anas ya gano wani abu na daminta ya tambayeta meneh kuma girman kansa bare barsa ba. Kallonta ya tsaya yi kusan na minti biyu amman sam bata gwada yunk’urin d’ago kai ba bale ya kalli cikin idanunta ma. “Miss Aleeyu” ya kira sunanta a


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login