Showing 105001 words to 108000 words out of 268365 words
Chapter 36 - Tana Tare da ni complete book document .txt
what Fannah batayi kalan wanda zata iya aikata abinda uncle nata yake fad’a ba. Ai inhar dagaske karuwan ce da bare so ya aura wa d’ansa ba k’azafi kawai suke mata, ayyah ashe shiyasa taketa kuka a office yau, shiyasa ko abinci ta kasa ci. “I will protect you Fannah no matter what.” Ya fad’a a fili.
*****
_9:23PM_
Fannah da family’nta ne zaune d’akin Baba yanzu tagama basu labarin abinda ya faru d’azu, abinda Mr. Fauzi yama su Ya Khaleel. Kowa wajen yasha mamaki matuk’a.
“Alhamdulillah! Alhamdulillah! Allah sak’a wa Anas da alhkairi, abinda yama Ya Khaleel daidai ne Allah saka masa da alkhai” “Ameen” kowa ya amsa wajen.
“Habibiti amman har duka Anas yama Farouq?” Mami ta tambaya cike da mamaki.
“Eh Mami, Mami tsoro nakeji wallahi Ya Farouq ze iya cewa ze rama dukan akaina.” Rungumota Mami tayi gam ajikinta tana shafa jelar gashinta da d’ankwalinta be samu ya rufe ba. “In shaa Allah ba abinda ze miki kina da Allah bayan haka kuma ga Anas na tabbata bare bari wannan shegen Farouq d’in ya miki wani abu ba.”
*****
_10:30PM_
“Wai ina wannan hegen yaron yajene?” Cewar Ya Khaleel da kansa for the 100th time yana duban k’ofar one room apartment da suka d’an kama da d’ansa. Chan ya hango shadow’n mutum, torchin hannun sa ya haska, ganin Farouq ke tahowa ya saki hamdala tare da nufan wajensa. “Kai Farouq ina kashiga tun d’azu? Kasan na rasa mahaifiyarka barin iya juran rasaka ba kaima. Kuma dan rashin hankali haka kata yawo a gari da fashasshen baki da hanci?” K’eyarsa ya tand’e “wuce ciki mu goge maka.”
_5 minutes later..._
Farouq ne mik’e kan ‘yar katifarsu a yayinda Ya Khaleel ke treating masa ciwon da Anas yaji masa a fuska da dettol. “Ina kaje ina tambayarka tun d’azu kamin shiru.”
“Kai de Baba Allah kaimu gobe se Mr. Fauzi ne ko Fauziyan nan ya raina wa kansa nan gaba ko kafad’an juna muka buga bare min koda kallon banza ba.”
“Wai me kake nufi Farouq? Kaga fa ka rufa mana asiri ni na fad’a maka kokuma in anzo tafiya damu in ce mai kai kad’ai ne banda ni, am warning you.” Lebb’an sa yacize irin mazan nan mana aikuwa yacize wajen ciwon.
★★★
_Washegari..._
K’arfe 8:10AM ya ma Fannah a office na Mr. Fauzi tun 8:00AM yake jiranta a zatonsa ma ko barata samu zuwa ba se kawai ya ganta, har cikin ransa yaji sanyi sede yau ma fuskarta ba walwala kamar jiya. As usual ta k’ariso gaban table nasa ta gaishe sa kanta a sunkuye. “Good morning Mr. Fauzi.”
“How are you feeling?” ya tanbayeta a hankali.
“Alhamdulillah, thank you for yestarday.”
“Ba komai” yace mata.
“Sir bansamu nayi making schedule naka jiya ba am sorry.”
“Is okay” yace mata ba tare da ya nuna damuwa ba. “Mesa baki fad’a min ba?” Ya tambayeta. A hankali ta d’ago kanta idanunsu na had’uwa ta sake sunkuyar da kanta, “I’m sorry” tace sincerely.
“Baki amsa min tambaya na ba, mesa baki fad’a min abinda wad’ancan biyun suke miki ba. Saisa kikazo jiya kika ta kuka kenan koh? Akansu ne?” Kai ta giad’a a hankali.
“Mesa baki sanar dani ba?”
“Sir I thought there will be no point in fad’a maka sesa kawai nayi shiru.”
“Next time call me up and tell me kinji?” Kai ta giad’a tare da godiya.
“Sun sake miki wani abu?”
“A’a.”
“Dagaske ne zaki auri wancan Farouq d’in?” Ya tambayeta kamar me jin kishin ta. Kai ta giad’a a hankali.
“Mesa? Kina son shi ne?” Nanma kai ta giad’a.
“Miss Aleeyu” ya kira sunanta “na’am” ta amsa kan ta a sunkuye. “Look at me.” A hankali ta d’ago kanta tana kallonsa kamar yadda shima yake kallon nata. Ba komi ne tattare da idanunta ba inbanda tsoro. “Do you really love him?” Ya sake tambayar ta cikin sanyin murya.
Hawaye tajiyo na ciko mata, “no Mr. Fauzi banasan sa, ban tab’a san sa ba, mugu ne, azzalimin da besan daraja ta ba.”
“Shhh is okay kar kiyi kuka, bakiya sansa baraki aure sa ba kinji?” Har hawayen nata sun soma sauk’owa ya ciro hanky ya mik’a mata amsa tayi ta share hawayen. “Sir how? Baffah Khaleel is powerful ni nasan dole zan auri Ya Farouq.”
“No baraki aure sa ba I promise, jeki huta Kacallah ze kula da aiki ki yau.”
“Sir don’t worry zan iya yin aik-” bata k’are maganar ba ya katse ta “banasan musu idanunki sun riga sun nuna baki samu bacci ba jiya so just go before I change my mind.” A hankali ta juya sanda takai bakin k’ofa sannan ta juyo tana kallonsa taga yana tattara files na gabansa “Mr. Fauzi” ta kira sunansa chak ya bar abinda yakeyi tare da d’ago blue eyes nasa yana kallonta. “Yes?” Ya bata amsa.
“Thank you” tace dashi. D’an murmushi ya saki wanda ya sake bayyano da kyan sa. Giad’a mata kai yayi as an answer sannan ya cigaba da abinda yake a yayinda tafice zuwa office nata ita kuwa.
Batasan me ba amman kwana biyun nan in *_TANA TARE DA_* Mr. Fauzi setaji she is safe kuma setaji ta ba damuwa. Kan cushion nata ta baje a hankali bacci me uban nauyin gaske ya isketa wanda takasa yi jiya da daddare dan yadda damuwa suka mata yawa.
_30 minutes later..._
A nitse kuma a hankali Anas ya bud’e office na Fannah. Taku d’ai d’ai yake a hankali har yashigo cikin office d’in zube ya sameta kan 3 seater tana bacci peacefully. Har gabanta ya tako tare da tsugunawa d’an hijabin daya tare mata fuska yasa hannu ya gyara dogayen eyelashes nata yatsaya yana kallo sannan yakoma kan girarta dayake nan kamar na Kajol na india yadda ya had’e me kyan bala’i. Sekuma d’an siririn hancinta dayake nan madaidaici dakuma d’an bakinta dakenan ba k’aramin chanba bakuma babba ba tsakatsakiya.
Besan dalili ba amman kawai ya tsinci kansa cikin jin dad’i, killer murmushi ne kwance kan kyakkyawar fuskarsa wanda ya lotsar da dimple nasa na gefe d’aya. Jakanta dake saqale a kafad’arta ya zira hannu ya cire a hankali yadda bare tada ita ba, tare da ajiye wa a gefe guda, k’afafunta ya daidaita kan kujerar tare da kunna AC’n a medium ta yadda beyi yawa ba bekuma yi kad’an ba. Ficewa yayi zuwa d’akinsa ya d’au wani arabian bargonsa me uban laushi da pillow yazo ya rufeta dashi tare da aza kanta kan pillow’n ya juya ze fita kenan Fannah ta kama bakin suit nasa ta baya chak ya tsaya tare da juyowa hannun nata ya raba da kayansa a hankali sannan ya rufo mata k’ofar ya fice zuwa office nasa. Yau yagama had’a model nasa sauran asalin gini yanzu. Already filinsa na nan kawai abinda yarage shine asa drawing d’in into action.
*© miemiebee*
beeenovels.mywapblog.com
[12:53, 12/18/2016] +234 903 612 6826:
•° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •°
°•°
*TANA TARE DANI...*👫
❣🎀❣🎀❣
*_written by miemiebee👄_*
In dedication to *Aunty Sis💕*
4⃣4⃣
“Miss Aleeyu barin je ba kema leave I can take care of myself” hannu ya mik’a ze amsa pillow’n se kawai ya saki k’ara dan zafin dayaji a cikinsa saboda blows da Farouq ya riga kai masa. A rikice tace, “meneh Mr. Fauzi?” Kafin ya amsata ya mata k’arya ta kwaye bedsheet d’in daya ruhu dashin, hannu ta aza kan bakinta cike da mamaki “Subhanallahi Mr. Fauzi dan Allah meya sameka? Ina kasamu wannan ciwuka? Kalli cikin ka? Ya Salam!!!” Ta fad’i tana hawaye tana kallon cikin Anas da yayi har wani purple brownish colour dan azaba.
“Mr. Fauzi meya same ka please?” Ta sake tambaya hankali tashe.
“Nace miki babu in kinsan kuka zaki tayi anan kuma go, leave, I can take care of myself.”
Innalillahi! what do I do now ta tambayi kanta barata iya barin Anas haka ba he is badly wounded ga fuska ga ciki meya samesa ko b’arayi ne suka shigo suka masa duka? Amman kuma ai gidan tsaf yake ba abinda aka b’arnata. Toh meneh?
“Mr. Fauzi please kayi hak’uri mu kaika asibiti kaji? Yi hak’uri.” Ta fad’a still tana hawaye dan tsantsan tausayi. Danko ba wanda zega ta’addancin da aka ma Anas be tausayawa masa ko be zubda hawaye ba.
“Nace miki barinje ba kitafi please.” Wayarta ta ciro zata soma dialing number’n Amal dan sanar da ita halin da ake ciki.
“Me zakiyi?” ya tambayeta.
“Zan kira Amal ne in sanar da family’nka I’ve found you tun jiya suke neman ka.”
“No karki kira su hang up.”
“But Sir-” katse ta yayi ta hanyan daka mata tsawan da seda shi kansa ya masa ciwo “I said hang up!” Kansa ya dafe yana muntsika fuska cike da azaba. Nan ta katse ta matso kusa dashi “Sir kanka ke ciwo?” Niyan shareta yayi da farko sekuma ya giad’a mata kai a k’arshe. Jakarta ta ajiye kan side drawer ta nufa toilet tare da fitowa da bowl cike da warm water data d’iga dettol ciki dakuma towels guda biyu, jakarta ta ture gefe tare da ajiye bowl d’in akai. Kallonta yake “me zakiyi?”
“Sir your face is a mess, zan goge maka ne.”
“Banaso just leave.”
“No Sir I’m not leaving mesa kai zaka taimaka min amman ni bakasan na taimaka maka? Saboda bankai inyi offering maka help bane? Saboda ka raina ni banida standard? Saboda ni talaka ce? Is that it Sir?”
“No Miss Aleeyu that is not my point...” sekuma yayi shiru.
“Toh kabari in biyaka taimakon dakake min koda na yau ne.” Shiru yayi chan ya giad’a mata kai.
A ranta tace, Ya Allah kar ka kamani da laifi saboda zan tab’a na mijin da ba muharrami na ba, baida lafiya ne taimako zan masa, astaghfirullah.
Nan ta tsoma d’ayan towel d’in cikin ruwan d’umin tare da matsewa a hankali ta d’an tab’a gefen bakinsa daya fashe. Towel d’in na tab’a wajen yajiyo zafi sosai hannunta ya kama “Sir nasan zeyi zafi hak’uri zakayi kaji? Sorry” a hankali ya sake hannun nata. Tana sake tab’a wani waje ya saki k’ara “arghhh! Ya isa kibari ze warke da kansa, go home”
“Mr. Fauzi please mana kabari koda germs d’inne a kashe tunda baraka je asibiti ba. Please”
Haka a nitse cike da tausayi ta riga bin duk ciwon da ke kan fuskarsa tana gogewa a hankali, sosai Anas ya riga sakin k’aran azaba in towel d’in ya tab’a masa kan ciwon ita kuwa duk lokacin daya yi d’an ihu seta basa hak’uri. Tagama da fuskarsa sauran cikin. D’ayan tsumman ta d’aga ta sa cikin ruwan kamar yadda tayi d’azu bedsheet daya rufe jikinsa dashi tasa hannu ta kwaye zuwa cibiyar sa.
“Me kuma zakimin?” Ya tambaya yana k’ok’arin jan bedsheet din gam ta rik’e tana me hanasa yin hakan. “Ba abinda zan maka Sir zan d’an matse maka wajen ciwon ne.”
“Don’t worry ze warke da kansa. Wai ke bakia jin tsoron zama da namiji kad’ai ne under thesame roof?” ya gwada tsorata ta ko zatace ta hak’ura zata tafi.
“Ina ji amman in da kaine bana ji, I trust you Mr. Fauzi nasan ba abinda zaka min shiyasa. Yi hak’uri in d’an matse maka cikin kaji?” sanda ya k’are mata kallo sannan ya giad’a kai.
A hankali ta aza hannunta kan cikinsa ta matse towel d’in kai. K’ara ya saki sosai dan azaba tare da rik’o hannunta. “Awwchh! Kibari ya isa ze warke da kansa, arghhh!”
“Sir hak’uri zakayi sauran kad’an sorry.” Haka tata lalashinsa kamar d’an yaro. Towel tasake canzowa tare da k’aro ruwan zafi kan ruwan dan ya riga ya huce. Bayan ta zauna ta sake tsoma towel d’in ciki, cikin siririyar muryarta tace, “Sir did you get drunk yestarday” Shiru yayi kamar be jita ba. “Sir?” Ta kirasa. “No” ya mata k’arya danko besan taga kwalban a bakin k’ofa ba.
“Toh wancan fa kwalban meh?” Ta tambayesa a nitse. Kai ya d’aga yaga kwalban sekuma yaji kunya. “Toh me ruwanki dan nasha? You are not my mother ko ita mahaifiyar tawa bata isa ta hana niba, stay out of my personal li-” be k’arisa fad’in ‘life’ ba yasaki ihu “arghh!” Sanadiyar tab’a masa kan inda ke masa zafi sosai da Fannah tayi. “I’m sorry” tace “sauran kad’an.” Chan ta nisanta, “Mr. Fauzi will you listen to me in na fad’a maka wani abu?” Kamar wanda bare ce komai ba seyace “meh abun?” Sanda ta sake matse towel d’in ta mayar kan cikinsa tana daddanewa kan ciwon a hankali tace, “if I were you, in za’a maidani kai abani kyanka da kud’inka da ilimi da komai da kake dashi I will thank God barin na wasting rayuwa na akan shaye shaye ba. Masu shaye shaye sune wanda basuda aikin yi, wanda basuda ilimi basuda komai se shaye shayen da sukeyin. Amman kaga kai komai Allah ya baka Mr. Fauzi, you are handsome, rich and very intelligent, me kake nema? Don’t you think bakayi adalci wa Allah ba ta hanyar masa godiya da shaye shayen da kakeyi?” A hankali ta d’ago idanunta tana kallonsa shima kallon nata yake da blue eyes nasa sannan ya kawar da kallonsa daga gareta.
“Kayi shiru Mr. Fauzi, do you think you are fair to Allah? Bayan ya gama baka komai seka gode masa ta hanyar bijire wa dokokinsa na hana kowane muslimi shaye shaye”
“No I’m not” ya fad’a ransa b’ace, muryarsa cike da weakness. “Ke bakisan mesa na mayar da drinking abinyi ba kidena intruding min cikin personal life. Get up and leave” yace a lokacin daya d’aga hannunta daga kan cikinsa.
“Yafi ace ka rasa mahaifiyar ka ko mahaifinka kokuma d’aya daga cikinsu ya gudu ya barku? Is that the reason kake shaye shaye?” Kallonta yake totally speechless chan kuma ya tuna ashe ranan ta karanta masa diary, cikin chan tagani. Hannunta ta raba da nasa ta mayar kan cikin nasa.
Hannun nata ya kuma d’aga daga kan cikinsa “ya isa you can go banasan maganan nan, saboda kin karanta min diary hakan be baki daman fad’a min whats right or wrong ba. I’m still your Boss”
“I know Mr. Fauzi, you are my Boss. Ammana in saboda mahaifiyar ka kake misleading precious rayuwarka ta hanyar shaye shaye you are destroying your bright future. Hakan na nuna you are weak yana nufin ka barta taci nasara kanka kenan. Show her you are strong ko ba ita you can live your life, ka mance da ita and move on if possible forgive her if not ka mance da ita. You have a very bright future kadena b’atawa ta hanyan shaye shaye kaji Mr. Fauzi?” Shiru yayi bece komai ba as ya wula cikin duniyar tunani yana nazarin duk abinda Fannah ta fad’a masa. Tabbas ba k’arya ko d’aya cikin abinda ta fad’a masa dan kuwa haka Shettima ma kullum ke fad’i masa sede koda Shettima ya masa magana bai san sauraro amman yau da Fannah tamasa maganar seyaji yanasan yayi moving on ya manta da abinda Ummimi ta masa sede bawai ze yarda ko ya aminta da mace bane a rayuwarsa ever again he is already broken.
“Can you do that Mr. Fauzi for Amal’s sake?” Kai ya kad’a mata da nufin “a’a.” “For mahaifinka?” Nanma ya girgiza kai. “Ummie?” girgiza kai still yayi. “For Shettima?” Nan ma haka. Cike da kunya tace, “for me?” Jiran masifar sa take setaji yace, “yes” a hankali sounding defeated.
Idanunta ne suka sake bud’uwa cike da jin dad’i da murna. “Dagaske Sir? Zaka dena shaye shaye and move on?”
“Yes” ya sake fad’i. Dad’i taji sosai wanda ta kasa b’oyewa. “You promise Sir?” ta tambaya dan sake tabbatawa.
“I promise” yace. Sede duk maganan nan da suke baya kallonta. “Look at me please Sir” tace cikin murya me dad’in sauraro. Yi yayi kamar be jita