Showing 51001 words to 54000 words out of 145917 words

Chapter 18 - TAFITA ZAKKA BOOK 2 COMPLETE.txt

04 Nov 2024

83965

yadda ya kwallafa rai akan cikin Sakina sannan yazo kuma ya tafi Ranar da Mallam ya kirasa ya fadamai da Zazzabi ya kwana,kwanansa biyu agida baya Fita Tana kula dashi,Ita kanta ta Damu sosai sai ta sakamai kuka ganin ya Daina Cin abinci sosai ballatana yawan mgana,da taimakon Mallam da Hajiya da Aliyu ya Dawo daidai da kuma Sarood itama tayi kokarin matuka wajen kula da shi Sosai take basa Tausayi tana da sanyin Hali kamarsa da kuma Hakuri shi kanshi yanzu ya Fara Tunanin mafitan da Aliyu yaso ya Nema tun farko yaki yarda da mganarsa ammh a yanzu yafi Sarood Damuwa Tsausayi take basa ita macece mai Rauni sannan kuma yaji yana Fatan in bai samu Haihuwa ta bangaran Sakina ba,me zai hana ya roki Allah ya basa ta bangaron Sarood Amina dai bai ma saka ta a Lissafinsa ba bai Taba kawo mata Daukan cikinsa nan kusa ba..!..abunda bai sani ba Daman Sau tari Allah yafi bamu abun da muke nema a inda bamu taba Zato ko Tsammani ba..!
Washegari yana cikin makaranta ya kira Aliyu da niyar ya Tuntubesa da mganar sai gashi shima ya fara mai mganar bayan sun gaisa Aliyu ke tambayansa matsalansa da Sarood ya ake ciki..? Yace mai har yanzu ba Sauki domin ko ya jaraba jiya iyau ne.


Aliyu ya kada baki yace"Shehi ni dai kaki jin Shawarata ne..Naso ka kira mallam ka sanar dashi matsalanka kila ya samo maka waraka Tunda yafimu sanin abubuwan da suka Shafi addini da irin wannan banace ka yarda wani yayi maka ba kasa aranka bamai yi sai Allah kuma wajensa kake neman waraka..!


Umar yayi shuru kamar bazai yi mgana ba Jin haka yasa Aliyu yace"Tunda Sakina ga matsalan da ake Samu Shehi me zai hana ka Jaraba Sarood din itama mu gani..!
Nasan fa kana son ya"ya bama kai da abun nan yake Faruwa Dakai ba ni kaina abokinka i feel ur pain Umar ina Fatan kai ma ka ka ijiye masu yi maka addu"a watarana..!
Danmallam ya gyada,kai kamar Aliyu na ganinsa kafin yace"Shikenan Aliyu zan jaraba shawarka..bari na Kira mallam muyi mgana..!
Aliyu yaji Dadi suka rabu bayan ya Bisa da addu"an Allah yasa adace a samu waraka kamar yadda suke fata..
Nan take ya kira mallam sai dai baya gida yace mai yana Jigawa sun zo Taro ne nasu na Da"awa ammh bazai Dade ba zai koma gida in ya koma zai kirasa.
Dayake abun na ransa kuma ya Kudiri niyar fadama mallam komai yasa bayan awanni kadan ya Sake kiran mallam din Lokacin har ya koma gida Misalin goma na Dare anan madina Nageria kuma suna fitowa sallar mangariba.
Mallam Shashensa ya koma abunda ba Dabi"arsa ba sai sun gama Sallar Isha"a yake shiga gida ammh ganinsa da waya yasa aka san uziri ne ya taso ma mallam din.Tabbas Uzuri ne domin yadda yaga Umaru ya Damu yasa yasan ba lafiya ba wani abu na Faruwa.
Bayan ya Dauka sun gaisa da Tambayan gida da iyalai kamar kullum mallam yace"Umaru meke Faruwa ne.?
Wannan kiran naka bana Lafiya bane ko..?
Danmallam ya kaskastan da kansa Waje ma ya fito saboda ba ya so Sarood taji mganarsu cikin Ladabi yace"Eh ba Lafiyan ba mallam matsala ne dani tuntuni nayi iya bakin kokarina ta bangarena ammh abu ya ci Tura shiyasa na yanke Shawaran kiran ka na Sanar Dakai..!
Mallam ya koma ya zauna gefen gadonsa domin kurya ya shige kada ma wani abu ya katsesa a yadda yaji Umarun yasan da wani abu.
Cikin Dattakonsa yace"Ina jinka..Allah yasa Zan iya maka mganin matsalan ka Umaru..!
Cikin Kunya kamar yana ganinsa ya farama mallam bayanin Tundaga Farkon matsalan har karshe da Mganin Shafan Aljanun da siya mata Tayi amfani dashi ammh matsalan kuma bata kare ba har alokacin..!
Mallam yayi shuru yana jinsa har ya gama kansa ya Daure na wani Lokaci,daya sa ya kasa mgana Har sai da Umar ya Kira sunansa sannan ya amsa Cikin Alhininsa yace"Ta bangaranka da ita Sakinar lafiya kalau ko..?
Duk da yasanni ammh so yake ya Tabbatar in da lafiya ai in ba lafiya ba ta Dinga samun ciki hartana barinsa ba.
Danmallam ya amsa da Eh cikin kunya aransa yana addu"an Allah yasa kada mallan ya sako Amina Har ga Allah bai shirya fadamai ya haikema wannan yarinyar ba duk da ba Haramci yayi ba matarsace ta sunna.
Sai Addu"arsa ta karbu mallam bai Tsawaita tambayarsa ba illah kai da ya Jinjina kafin yace"Umaru kana jina ko..?
Ka bani nan da zuwa gobe zan yi Bincike na acikin littafan malaman musulunci sosai sunyi bayanai game da ira iran wadanan matsalolin naka..Insha Allahu zuwa gobe zan kiraka da kaina nayi maka bayanin komai..!
Danmallam yace"Shikenan mallam..Allah ya kara girma Allah ya kara nisan kwana..!
Mallam ya amsa da Ameen Ameen ya Cike da fadin"Kada ka damu da Yardan Allah zamu samu mafita..Domin Qur"ani waraka ne gamu bayin sa kaji ko..?
Ya amsa cikin yakinin kamar ma ya Samu mafitan daganan sukayi sallama Mallam ya koma yayi jugum yana nazarin matsalan Umar..
Tabbas yana da zurfin ciki sannan yaga Hakurin ita Saratun,bazai ce ga matsalan ba kai Tsaye tunda Basir ko Sanyi na Haifar da haka ammh nasu sai dai Raunin gaban namiji ba ta ki yin amfani ba gabadaya sannan shi da Sakina lafiya lau ita Saratun ne matsalan.
Lalle akwai wata mgana a kasa shi ba Malamin Duba bane ko na Shirka shi malamin sunna ne da Qur"ani in an kawo matsala ba kansa Tsaye yake yi ba yana Duba Littafan addini na malamai da kuma Qur"ani Domin neman mafita sannan akwai Irin irin matsalolin nan na Sihiri da malamai Dabam dabam sukayi littafai da Dadama Domin warware ma Mutane kai dasamun Mafita shima haka zai yi bazai yi zargin wani abu kai Tsaye ba sai ya bincika.
Ana Idar da sallar isha"i ya Sake dawowa cikin gida yau ko Aba basu Tsawaita Hira ba sukayi sallama ya wuce Shashensa Ranar hajiya ke da Turaka ko da tazo ta iske malama nata Nazarin wasu littafai sama sama ma suka gaisa abinci ma sai da ta matsamai yaci kadan
Abun bai bata mamaki ba taga ko barci bai kwanta ba tasan sa da son nazari wani Lokacin ammh bai hanasa kwanciya ammh sai gashi ya kasa barci data tambayasa yace yana wani Nazari mai muhimmaci ne,tayi kwanciyarta in ya gama zai zo ya sameta Dole ta shiga ta kwanta ta kyalesa.
Shi kuma sai wajen biyu na Dare ya gama Bincikensa sannan bai kwanta ba ya Dauro alwala yayi nafilfilu da addu"o'i sannan ya kwanta wajen uku da Rabi Biyar na cika ya Farka ya Tada Hajiya ya fice zuwa masallaci.
Sai Chan Safe ya Dawo Shashensa ya Tsaya masallaci sun yi meeting da Dattajan anguwannin kusa dasu.
Wanka kawai yayi ya karya Lokacin Hajiya ta koma bangaranta ya Kira Umar bai Dauka ba sai da ta katse sannan ya Kirasa yana aji ne yana karatu yana ganin kiran maallam ya nemi lamini ya fita waje ya kirasa.
Bayan gaisa kamar yadda suka saba Mallam ya fara mgana cikin Dattakonsa kamar haka.


"Umaru ka yarda da Allah shine mai yi kuma mai hanawa..Sannan ka yarda da duk abunda ya samu bawa Daga garesa ne sannan kowata Lalura daga garesa ne sannan Waraka ma yana wajensa ko..?
Danmallam ya amsa da eh Mallam ya Cigaba da nuna mai Duk abunda zai Faru da bawa koma ya faru kada ya Zargin kowa ya Dauka Daga Allah ne kuma garesa zai nemi waraka bai Fito ya mai bayanin Sihiri bane ammh Cikin Dattakonsa yace"Ka san Acikin Qur"ani akwai ayoyin da Allah ya Fadamana suna karya sihiri ko asiri ko .?
Ai kasan su..?
Cikin Sanyinsa yace"Eh mallam..!
Maalllam yace"karantomin su naji..!
Umar ya gyara Tsayuwa ya fara fadin"SURORIN AL'QUR'ANI GUDA SHIDA DAKE KARYA SIHIR KO ASIRI.


1. SURATUL TAUBA: AYATA 14.
2.SURATUL YUNUS :AYATA 57.
3.SURATUL NAHIL: AYATA 69.
4.SURATUL ISRA"I :AYATA 82.
5.SURATUL SHU'ARA :AYATA 78_82
6.SURATUL FUSILAT: AYATA 44.


mallam ya jinjina kai kafin yace"Dakyau..To kamar yadda ka lissafasu ka samu ruwan zamzam ka karantasu duka ka tofe aciki ka rika Shafe al"auranka duk dare in zaka kwanta da jikinka gabadaya sannan ka rike addu"a da azkar domin koma menene Yana jikin ka ne ba jikin ita Saratun ba..!
Danmallam ya jinjina kai yana Fadin"zanyi haka insha Allahu nagode mallam Allah ya kara girma..!
Mallam ya amsa da Ameen yana fadin"Allah ya warware mana..Allah yasa adace Allah yasa asamu waraka..!
Daga haka sukayi sallama Danmallam Ya Dade tsaye kafin ya koma cikin ajin sa ya cigaba da koyarwa karkashin Ransa kuma yana gasgasta mganar Aliyu koda mallam bai fito yace sihiri bane ammh Yanayin addu"o"in da ya basa na karya duk wani Sihiri ne ko asiri.
Yana fitowa da ga ajin ya koma Office ya Kira Aliyu ya fadamai yadda sukayi da maallam Aliyu ya rike baki kafin yace"Kaji mganata ko..?
To ka gaggauta fara abunda yace maka Fatan nasara Allah y bamu waraka..!
Daga haka suka rabu Daga cikin makaranta gida ya wuce daman yanaa da Ruwan zamzam din Sarood bata nan tana makaranta sannan in ta Dawo Zata biya gida Mami Sara na Fama da Zazzabi.
Alokacin ya samu Lokaci yayi Duk abunda mallam ya Umarcesa ya Tofesu acikin Ruwan zamzam din a kuma wannan Daran ya Fara amfani Dashi da yakinin Ciwonsa Daga Allah ne kuma waraka na wajensa..!
Sannu sannu dai..Bata hana zuwa sai dai a Dade ba"a je ba..!
Daga yanzu aikin nasu ya fara Lalacewa Alalan geronsu ya riga yayi Ruwan da bazasu taba iya Dauresa ba koda kuwa sun mai Cikon Gari acikinsa..!


*****


Sati dayan da Malam ya Dibar ma Anty Amarya na cika ya Kirata a waya Daman kiransa take jira tana Lissafe da Ranakun.
Sai dai yana fara bayanin Idanuwanta suka Rufe Daga sanda yace Wace ke Lalata Cikin Sakina tana cikin matan mallam sannan tafi kusa da Hajiya da kowa acikinsu sannan bama Take lalalata Cikin ba ko yau sakina ta kara Samun ciki bazai taba zama a mahaifanta ba akwai abunda aka bata Tacin ma cikinta wanda yake hana Cikin zama acikin maranta. !
Anty Amarya na Tsaye ne acikin Dakin su Sa"adatu in da su Sakina suke bata gama Sauraran mganar mallam ba ta yi wurigi da wayar sakina ta Tsorata tabi ta kallo ganin yadda ta fita a fusace.
Haj.Uwani na gaban madubin bedromm dinta tana Saka dan kunne a kunnenta Kamar Daga sama taji an bango kofar lokaci Daya da shigowa Cikin mamaki ta juyo tana kallon ikon Allah..
Idonta fes a na Anty Amarya wacce ke kallonta Cikin Jajayen idanuwanta da suka rine da bacin rai da wani Bakinciki.
Haj.Uwani Cikin mamaki tace"A"a Amarya Lafiya kika shigomin har Cikin kuryan Daki ba sallama..?
Kawai sai Anty Amarya ta Nufeta ta Shako wuyanta idanuwanta sun firfoto waje cikin Karaji take fadin"Ke baki chanchanci sallaama ba..Baka mai bakar aniya muguwa azzaluma mai fuska Biyu da izinin Lahi Uwani sai kin ga sakamokon ki Tun aduniya muguwa macuciya azzaluma kaawai..!
Haj.Uwani ta Fincike Wuyanta Cikin Wata irin kallo take bin Anty Amarya da shi kafin ta kece da wata irin Dariya tace"Azzalumai bakake masu bakar Aniya zaki ce Marliya sannan ki rika saka min jaye..Bazamu gama da Duniya Lafiya ba DA NI DA KE..tunda duk jirgi Daya ya kwasomu..!


Tafada tana dariya lokaci Daya tana mata kallon Nasan ki, ni tuntuni ke kuma sai yanzu kika sanni..?












*Janafty**TFZB2013*


*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488*




Anty Amarya ta dago tana kallonta cikin rawar baki dana jiki tace"Ban..ga ne ba..?
Me kike nufi Uwani..?
Haj.Uwani ta saki wani kayattacen Mirmishi mai hade da cin nasara tana kallon cikin Idanuwan Anty Amarya wacce ta fara tsorata da Lamarin Uwanin tace"Kina sane da abunda nake nufi marliya ko na kira ki da Madina ne..?
Tafada cikin tsaida kallonta kan Anty Amarya wacce ta zaro ido jin Sunan da Uwani ta Kirata dashi Sunan da mutanen da suka santa dashi ba su da yawa suna ne da ta saka ma kanta Tun tuni domin cikar wani Buri nata.
Haj.Uwani ta fara taku acikin Dakinta tana Zagaye Anty Amarya tana Sakin Dariya kasa kasa kafin ta nufi kofar Bedroom dinta ta kulle ta harda Murza key ta juyo tana Fadin"Komai na Bukatar sirri madina duk da bansan da wacce kike zo ba..?
Anty Amarya da tagama Tsorata da mganganun Dake bakin Hj.Uwani baisa ta yi saurin karaya ba yasa cikin Gyara Tsayuwarta tace"Kina sane da duk abunda nazo dashi Uwani..Tunda ke kike aikata shi..Kashe rai fa kike yi fa Uwani..?
Kina lalata duk cikin da Sakina take samu yanzu in wannan mganar ta fita kina Zaton zaki kara Minti Daya acikin gidan nan ne..?
Tafada tana kallon Haj Uwani wacce ba karaya ko nadama ko kaadan a Tare da ita sai ma Zama da tayi gefen gadonta ta Dora kafa Daya kan Daya tabi Anty Amarya da kallo kafin tace"Ranar Biyan Bukata rai ba abakin komai yake ba Marliya a wajen ki na koyi wannan Tsarin sannan Da kike mganar in Labarin nan ya fita bazan kara ko minti Daya agidan nan ba..?
To wayace miki zai fita yanzu..?.
Ai ko zai fita sai na gama cika Burina Likacin na zama giwar mata ko mallam babu yadda ya iya dani marliya ballatana Hajiya da ban Dauketa wata Tsiya ba..Atafin Hannuna take kinsani..!
Bama ita ba gabadayanku a nan dina kuke ba wacce bansan duka motsinta ba..!
Ta karishe Fada tana Nunatafin hannunta cikin gadara Anty Amarya tayi wani mirmishin takaici kafin tace"Aiko kunyi kuskure Uwani..Wlh yadda kika yi sanadiyar Salwartar da Cikin Sakina sai nayi Sanadiyar da asirunki ya Tonu yau a idon Duniya..Yanzu ba sai anjuma ba, zan je na Sanar ma Hajiya komai domin ta gano Muguwar bakar Fusarki..!
Tafada a fusace kafin ta juya zata fita ta tsinkayi muryan Haj.Uwani Cikin Gadara.


"Bani kadai zaki tona ma asiri ba marliya Har da ke karan kanki..da wacce ta hada hannu Dake kuka KASHE YAYA..sannan kuma baya zatayi Zani marliya harta Danmallan zai gano cewa ba da Ra"ayinsa ya auri Sakina ba ke kika shiga kika fita hakan ta kasance..!


Da wani irin mamaki da al"ajabi da Faduwar gaba Anty Amarya taci Burki ta kasa juyowa ta Fuskanci Hj.Uwani Domin tana faman kokuwa da Faduwar gabanta na yadda Uwani ta san wannan Boyayiyun sirrukan da ga ita sai balaraba sai Malaminsu suka san anyi haka sai gashi a bakin Uwani to garin ya akayi ta san duka sirrukan su haka su basu taba sani ba..?
Tana wannan Tunanin taji Muryan Uwani a saitin kunnenta tana fadin"Kin yi mamakin ya akayi nasan Duka wadanan sirrukan naki ko nace naki keda Balaraba ko..?
Anty Amarya ta kasa gaba ballatana baya ba inda jikinta baya rawa Haj.Uwani ta saki Dariyan nasara kafin ta fara Tafiya zuwa gaban madubin Dake Dakinta tana Fadin"Nayi mamakin da sai a yanzu malaminki ya gano miki ni marliya ai na Dade ina shirina kusan ma nace na Rigaki shirya komai..Ni tuni Mama ta Bincikomin komai naki da ke da wacce ke tayaki dukkan ku wani motsinku ko sirrinku yana Cikin Tafin Hanuna Marliya abunda baku sani ba Kuna aikin ne ni ina warware muku..Kamar yadda Sakina ke barin Cikinta haka in wannan balarabiyar ta samu ciki ita ma haka zatayi ta barinsa hakama Amina ita kanta ban kyaleta ba na shigo da ita cikin Tsarina..Tsarin da zai kai ni nan da Lokaci kadan na cika Burina..!
Sai alokacin Anty Amarya ta Juyo tana kallon bayan Haj.Uwani Cikin Rawan baki tace"Wani irin Buri ne wannan da kika Zabi ni ki hanani Cikar nawa burin.
A bar batun Rufa Rufa Uwani Tunda kinsan komai ba amfani na cigaba da Boye miki manufata ni in kinyi Hakuri ba mallam nake so na mallaka ba..Kawai Sakina nake so ta Zama Mowar mata wajen umar da Danginsa..Sannan ita kadai ce nayi ma alkawarin zata haifa ma Umar magaji ta kuma Haifa ma Hajiya da mallam jika mafi soyuwa bayan ita ban yarda wata tazo Daga baya ta fita ba..Sannan in hakan ta faru nasan nima zam zama Shalele a wajen mallam da Umaru tunda nice silar duk abubuwan da suka faru..!
Ki fadamin meye naki burin da yasa ni kika ki bari nawa burin ya cika..?
Ina so naji irin naki Burin akan mallam da zur"arsa..?
Haj. Uwani ta juyo tana kallon Anty Amarya ido na cikin Ido kafin tace"Ko baki tambayeni ba zan fada miki..Boye boye ai ya kare. tunda malamin ki ya gano miki ni Marliya..Karkade kunnuwanki Ki sha Labari yanzu zan sanar Dake yadda naki Cikar Burin ke neman yayi min Cikas kan nawa Burin da nayi shekaru ina Wahala akansa..!
Komawa tayi ta zauna ta kara Dora kafa Daya kan daya kafin ta fara Fadama Anty Amarya duka shirinta da nata tsarin da Burin datake dashi akan mallam da ahalinsa ta karishe da Fadin"In har na bar Sakina ta Haihu Da Umar kin batamin Tsarina marliya..shiyasa na hana faruwar haka sannan bama ita ba indai ina Raye Umar bazai ga kwansa a Duniya ba..Tunda na gano Mallam yana matukar son yaga jikokinsa ta bangaran sa na mike tsaye na shiga na Fita na hana faruwar hakan..Ya"yana kadai ne zasu haifama mallam jikoki kuma ya sosu ni kadai ce zan zama Tauraruwa ba Hajiya ba..In ta samu mallam a baya awannan gabar Lokacinta ya kusa karewa..!
Nasan zaki ce ina Nazir da Nasir da na bari suka haihu.?
Ai suma din ba gazawata bane Marliya Tsarin aikina ne..Daga ya"yan Nazir din har Nasir din wa kika gani mallam ya Damu dasu?
Ai nasa mama ta Dakushe wannan Tasirin har Abada kuma bazasu yi shi a idanuwansa ba Nazeem ne kadai da Uzairu zasu haifa masa jikoki su zama Sanyin Idanuwan mallam bayan su kuma nayi alkawarin har Abada ba wanda zai haihafama mallam Jika Tun balle ma Danmallam da mallam ya fi so cikin ya'yansa shiyasa kika ga inayin Duk abunda nake so..!
Niso nake nan gaba ya"yana su zama sune Hop din mallam gabadaya Sune komai nasa bashi da yarda zai yi sannan kuma alokacin ni zama giwar a cikin matansa ko yana so ko baya so..Ya'ya ne kan gaba a dukiyarsa sannan wajen haifa masa jikoki ma sune kan gaba Dole kauna da soyayya ta koma kaina da Ahalina gabadaya..Mganar Sa"idu bai gabana domin ke da Balaraba kun Rage min wannan aikin..Lokaci kadan nake jira na Aiwatar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login