Showing 57001 words to 60000 words out of 145917 words
Cikin wata irin Murya tace"Karya take yi madina..Uwani bata isa ba..In juranta Sammako mu mun Dade atafe..Bata isa ta zo ta lalatamana Aikin da mukayi wahala mukayi shekaru muna Wahala ba Haba Madina Hajiya Uwani muguwar matace bata da mutunci kuma bata da imani Tsakani ga Allah yadda Hajiya ta yarda da ita sai da ta Cutar da ita..?
Sannan ina laifin in ta Hana Amina Haihuwa ko zama da Umar daman haka muke so auran yadda yake gantale ya kare a gantale itama wannan Balarabiyar ai in ta Hanata Haihuwa mu taimakon mu tayi ammh Sai ta Hado da Sakina..?
Tasan shekara nawa kika kwashe kina Wahala kan Sakina ta Samu Ciki ta Haihuwa ta zama Mowar mata agidan Umar..?
Ko kuwa tasan Shekara nawa ni na bata ina Zaune da Fuskar balaraba Domun cikar Burina..?
Shekaru fin Talatin ina Kun san bakin Cikin Sa"idu da Matarsa YAYA shekaru talatin na kwaahe ina Bautama ya"yanta shekaru masu yawa na kwashe ina nuna ina son yarinyar nan Amina har saki sai da Tsinnanniyar tajamin sai acikin wannan shekarar ne na samu yadda nake so shima bayan kasa ta Shafe idon yaya..To bata isa ba ki Fadamata bata isa ba..Bazamu bari ta Rusa mana Shekarun da muka kwaashe muna Wahala na Samu Sa"idu Dakyar Madina saboda haka fa na Hada kai Dake domin cikar Burina ke kina komai Saboda Sakina ni kuma inayin komai saboda Sa"idu ne ko JAFAR daya so ya nuna taurin kansa nayi mganinsa yanzu..Duk da abaya ba AMINA NASO ta kangare ba..Ba ita naso ta zama mara kunya ba..Ba ita naso ta koma haka ba Jafar naso ya koma haka ammh duk da Haka ban Sare ba Madina lamarina ba ja da baya kuma ba Faduwa ballatana Na karaya kema bai kamata ki karaya ba Madina..!
Ta karishe Cikin Hargagin ta na Daukan ita kadai ce agidan idonta ya Rufe bataji bata gani.
Amina dake Tsaye Tsakiyar Falon Mamanmu sai da ta rike bango Sakamakon wani wawan jiri Daya kwasheta jin kalaman dake fitowa daga bakin mamammu wanda suke mata amsa kuwa acikin kunnuwanta tana Fatan yasa abunda taji ba gaskiya bane ba Mamanmu bace ke wannan mganar ba.
Tasowarta Daga barci kenan ta fito tayi alwala ta Duba Bayinsu na Daki ba Ruwa sai taji kanar mgana Daga Dakin mamamu sama sama yasa ta fasa yin wajen famfo ta shigo Dakin da niyar kiran sunan mamanmu sai dai mganar data ji ne yasa ta tsaya sanda Taji kalaman mamanmu da suka kusa saka Zuciyarta ta Buga.
Bata gama Dawowa daidai ba ta Sake jin muryan mamamu Cikin Fusata tana Fadin.
"Ita din banza Madina da zata Tsorataki. me akayi akayi HAJIYA UWA..? Muka kauda YAYA har Lahira ballatana ita..? Karki manta Saboda Cikar Burina kika taimakamin muka saka Malam ya Kara mata gudu zuwa Lahira.kamar yadda nake kokarin taimaka miki auran AMINA DA UMAR ya kare ahakan sannan bazata taba Zama wata mai Daraja awajensa ba Sakina ce kadai zata haifasama D'a jikan mallam da Hajiya..Saboda haka ki kwantar da Hankalinki Rai fa ba abakin komai yake ba wajen Biyan Bukata AMARYA..!
kai Amina ta Dafe saboda ya Fara juyamata Hannunta Duka Biyu ta saka ta Toshe kunnuuwanta Lokaci Daya tana girgiza kanta Hawayen da suka fito mata suka fara ambaliya saman Fuskarta kamar an Bude famfo..!
*Janafty**TFZB2014*
*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488*
To mu kawar da ita nace madina tunda zata kawo mana matsala mana..Nafa fada miki tun abaya wajen biyan bukata rai ba abakin komai yake ba ke kika kara tunatar dani hakan madina Lokacin da kikace mu Kawar da YAYA naki baki Dama ina ganin kamar a lokacin bai kamata ta mutu ba naso ne sai na kunsa mata kwatan kwacin bakincikin da ta kunsamin amamh da kika nuna min mutuwarta itace masalaha bagashi tatafi ta barmin Sa"idun ba kuma sai da ta kauce na samu abunda nake so to kamar hakane in dai Hajiya uwani zata zame miki matsala wajen cikar naki Burin Madina mu kawar da ita kawai..!
Amina Tsabar Rudin data ke ciki yasa kafafunta suka kasa Daukanta bata san sanda ta sulale ta zube saman Cafet din dakin mamanmu Lokaci daya tana Saka Hannuwanta duka biyu ta toshe Bakinta saboda kuka ne ke son kwace mata ba taredata sani ba.
Mamammu fa..?mamanmu Innalillahi wa"inna ilaihirraju"un ita ke fadi da bakinta ta kashe Yaya ta kashe yaya wannan mganar amsa kuwwa take mata sannan mganganun sun Haifar mata da juyawar kan data kasa gane wani yanayi take ciki abu daya ta sani Taji abunda Tunda take bata taba jin makancin sa ba taji abunda Hasashe ko zato ko Tsammani bata ba Zato zata jisa Daga Bakin data aminta dashi ba.
Rarrafawa tayi kamar mai koyon Zama saboda ta kasa tashi ta Dage labulen Dakin mamammu na ciki ta gefe kadan so take ta Tabbatar da abunda taji domin gani take yi kamar ba Mamanmu din bace mai irin Muryanta ne sai gashi taga Fuskar mamanmu cikin yanayin da bata taba ganinta ba Tana Tsaye tana waya ta cigaba da mgana cikin Zaro ido tana Fadin"to maza ki kira mallam..Ayi mana mganinta mu koma gefe muna Cin Duniyarmu da tsinke a Matsayin Dayyaba da Madina chan gefe kuma muna Cigaba da yaudaran mutane da Salihan Fuskokin mu na Balaraba da Marliya..!
Bata tsaya ma ta gama ji ba ta juya Cikin Rarrafen har ta fice Daga Falon batare da tayi wani motsi ba Hawaye kuwa kamar an bude Famfo haka wasu ke fita wasu na kara Bulbulowa Idanuwan mamanmu ya rufe shiyasa kwata kwata bata ji wata alaman akwai wani acikin gidan ba.
Amina na fitowa Tsakar gida tayi tayi tatashi sai ta kasa Domin gabadaya jikinta ya Saki Lokaci Daya ta kasa gasgasta abunda taji kuma ta gani Mamanmu kadai kanta ke iya fadi da sunan yaya Anty Amarya bata wani bata mamaki ba jin sunanta Daman ita Tuni Tasan Halinta ammh acikin wannan yanayin ace Mamanmu ce ke da Alhakin Duka abubuwan da suke Faruwa ta yaya zuciya zata iya Daukan wannan Gaskiyan..?
Dakyar ta iya mikewa sai da ta rike Karfen barandan su sannan gabadaya kanta juyamata yake Bata gani Dakyau wani irin Biji Biji take gani Allah ya taimaketa taga Hijabin Haddar Hamida kan igiya data wanke ta Taka Sannu sannu tana Nunfashi Sama sama ta Daukosa ta sakasa ko Takalmi babu a kafarta haka ta Fice Daga gidan Cikin wani yanayi duk Takun da Zatayi sai kalaman mamanmu sun mata amsa kuwwa acikin kunnuwanta Daki Daki Dayasa Cikinta ya Cure waje Daya Dakyar take iya taka kafarta a Haraban gidan taga Jawaad yana kwallo yana ganinta ya nufeta yana Kiran sunanta sai kawai Amina ta kallesa ta kara kallonsa Tabbas sai Allah ya Tsine ma balaraba ko da Hakkin Jawaad aka barta sai Rayuwarta ta D'aida'ice Rumgumesa kawai tana so ta Fashe da kuka ammh ta kasa acikin Kirjinta take jin wani zafi kamar zata mutu batare da tamai mgana ba taja Hannunsa suka fice domin gabadaya gidan ne yayi mata wani zafin Datake jinsa har acikin jikinta suna tafe yana Fadin"Ya Amina ina Takalmin ki. ?
A islamiya an ce mana ba kyau tafiya ba Takalmi..!
Bata ma Sauraransa ita dai kawai Jefa kafa take yi Allah ne ya kaita Falon Hajiya ba Domin tana ganin Hanya Dakyau ba suna shigowa Hamida da Hanne suka Dago suna kallonta gabansu ya fadi ganin Hawaye Kaca kaca a Fuskarta Hannun Jawaad ta Saki ko barayin bata kallah ba Ta nufi Dakin su Hanne tana jin ita da Hamida na Faman kiran sunanta suna tambayanta me ya faru take kuka ko Waigowa batayi ba a yanayin Datake Ciki ba kowa zai iya Fahintarta ta ba Tunda bata da Uwa a raye a Duniya to ta samu kadaicin da zata Zauna Tayi Tunanin makomar ta a wannan Duniyan da Rayuwar data ke cike da Tarin azzalumai maciya amana..!
Tana shiga Dakin ta Ture kofar bata ma iya karisawa Kan gadon ba ta Sulale nan saman Cafet a kofar Dakin Tana Dafe Saitin zuciyarta Daya Dunkule waje daya ga cikinta Daya Cure waje Daya yana murdamata Sosai da sosai Hawaye da majina Har da Miyau haka suke kara kaina akan Fuskar Amina batare data Damu Data Share su ba.
Achan Falo kuwa Hamida ta kalli Jawaad tana fadin"Wai me ya faru ne Amina ta shigo tana kuka..?
Shima ya girgizamata kai kafin yace"Bansani ba nima ina kwallo na ne tazo tana kuka taja Hannuna muka zo nan..!.
Hanne ta mike tana Fadin"Hamida muje mu gani..;
Tare suka Dumguma suka Nufi Dakin suna Tura kofa suka kusa cin karo da Amina atare suka saki Salati Hanne ta Duka gaban Amina tana Fadin"Amina meke Faruwa ne..?
Amina ta runtse ido sai wasu Hawayen ta Dafe saitin zuciyarta Dake mata Zafi bakinta yayi Nauyin da bazata iya mgana ba.
Hamida ta kalli Hanne Cikin wani yanayi kafin tace"Ko zaki je ki kira Hajiya a shashen Baba mallam ne..?
Hanne ta mike tana mai yarda da mganar Hamida da Sauri Amina ta Rike kasan Sikat dinta bata so ta Kira Hajiya domin in tazo bata san me Zata Fada mata ba, ta tabbata ita kanta ba Domin taji ta gani ba ko Duniya Zasu Taru su fadamata Bakaken Halayyar mamanmu bazata taba yarda ba shiyasa ta Dago Jajayen idanuwanta Dakyar tace"Kada ki kirata..!
Hanne tace"To kuma kina ta kuka..!
Amina ta Runtse ido kafin tace"Ba..bani da lafiya ne..!
Hamida tace"Kan ki ke ciwo..?
Daman tasan Amina da Raki ciwo kadan sai ta Fara kuka da Sauri Ta gyada kanta Hanne tace"To ki tashi kici abinci ki sha mgani sai ki kwanta..!.
Saboda su kyaleta yasa tace musu tasha mgani agida Muryanta a Dakushe Hamida ne tace Hanne ta Taya ta su taimaka ma Amina ta koma kan gado tunda bata da Lafiya haka suka taimaka mata ta hau kan gado ta Dunkule ta Runte ido kamar mai barci har Hamida ta Lallube kafarta da Bargo suka fice bayan sun turo mata Kofar sai da suka fita ta Bude idanuwanta Allah Sarki Hamida mai kyakyawan zuciya tunda Take da Hamida bata taba ganin wani sharrinta ba sai Alheri ya zata ji in ta ji Halin Mahaifiyarta..?
Kai Innalillahi Yaya ashe ashe kasheta sukayi Shiyasa ta kwanta Lafiya lau sai gawanta aka gani shin me yaya ta Tsare ma Mamanmu..?
Ta bar mata ragamar gidanta ta bar mata Ragamar duka ya"yan data Haifa ace ko don haka mamanmu bazata Raga mata ba..?
Tunda take bata taba ganin Aba yayi bambamci tsakanin Mamanmu da Yaya ba har tana Kwatantashi Cikin masu adalci Tsakanin matansa.
Ashe ashe alheri yana komawa Sharri ashe ashe haka Duniya ta gada..!
Sai yanzu ta Fahimci Bakin Zaren Ta Dade tana Tunanin da wa Anty Amarya take waya kwanaki tana ambaton sunanta da kokarin Hanata Tarewa a gidan ya Danmalam sai yau Sirrin Boye ya fito Filo ashe mamanmu da Anty Amarya Bakin su Daya..?
Ita tanayin komai Saboda Aba ne ita kuma Anty Amarya saboda Sakina ne..? Ita fa Haj.uwa dataji suna ambatkn sunanta ita me ta ke aikatawa..?! Sannan domin wa take yin abunda take yi har suke Tunanin in zata basu matsala su kawar da ita..?
Lalle Duniya ba abun yarda bace abunda ko a mafarki ko Finfinan India dana Hausa bata jiba ai ko a karance karancen datake yi bata taba Haduwa da makirci da mugunta irin wannan ba Shekaru Goma sha Shidda Mamanmu ta kwashe tana kassara Rayuwarta ko da da rana Daya bata taba bari ta rabu da Yaya tasan Dadi da Martaban uwa ba shekaru sha Shidda ta kwashe tana Gurgunta Rayuwarta sai alokacin abubuwa suka Dawo mata Daki Daki Tun Farko kovsau Daya mamanmu bata taba Zaunar da ita tayi mata Fada kan wani abu ba sai dai ta rika Fadin yarintace in ta girma Zata Daina Ammh ai Hamida bata mata Haka bama ita ba kaf ya"yanta tana Dorasu kan Hanyar mai kyau tun daga bangaran Tarbiya har bangaran Ayyukan gida da Sauraran abubuwa ashe da gangan ta Sangartata ta Shagwabata Duk cikin Lalata Rayuwarta ne bata sani ba Kaiconta ashe ashe duk wasu abubuwan datake yi ba yin kanta bane tasan wasu abubuwan na tadda Hali ammh wannan Rashin Tsoron da Zafin Zuciyar duk ba nata bane Mamanmu ne taso ta kassara Rayuwar ya Jafar sai abun ya Tsaya akanta ta Godema Allah da abun ya Tsaya kanta Domin daman karamin alhakin daka raina Watarana shi zai tsole maka ido.
Tafara Tunanin yadda ta rika turata sai taje ta ce ma Hajiya ko mallam bazata tare ba batasan Dannallam sai yanzu ta Fahimci komai wato tana Taya Anty Amarya ne kamar yadda ta Taimaka mata ta kashe musu uwa anya Balaraba zata ga Annabi kuwa..?
Idan ta Mutu kila kasa bazata taba karbanta ba ashe ashe bata son tarewarta da ya Danmallan ta Tabbata Auran ma Allah ne yaso da bazasu taba bari ba ta Tuna sanda take tusa mata ra"ayin tace ya saketa Tsoho ne bai dace da ita ba ta tuna yadda take Zaunar da ita tana Dukan ruwan cikinta in taje gidan Danmallan tayi Weekend ta Dawo tasha Turketa ta Tambayeta ko suna waya sai tace mata A"a data ga kuma kamar abun yayi musu yadda suke so ne ta fita Sabgarta ashe Duniyar ce ta Fara Samuwa ba shakka Taga Aba ya Rage damuwa da wasu al"muran sannan ko Jawad sai ya kwana wajen su a ashashen Hajiya Aba bai Damu ba abaya kuwa yana Dawowa sai ya nemi Jawaad inda ya Saka kafa nan yake sakawa shima sai da Mamanmu ta rabasu taji Dadi ashe ashe Sihiri ne ajikinta shiyasa take Fama da Zafin zuciya bata sani ba..!
Sai ta Tuna Aminu sanda yake Fadamata watarana ga Mamanmu din ammh har Abada bazata Shafe mata matsayin UWA BA..ta yarda kuma ta amince a wannan Ranar kewar Uwa ne ya Taso mata da tana Raye da a kan kafadarta zata kwanta tayi wannan kukan ammh ina Duk da Lokacinta ne yayi domin mamanmu bata isa ta yi Ajalin yaya ba tunda ita ba Allah bace ta sani Daman chan kwanakin da suka Rage mata a Duniya kenan
Mamanmu da izinin Lahi sai tayi mutuwar wulakanci sai tayi mutuwar kaskanci wannan Duniyar datake Fatan ta samu bazata taba cinta ba Har Abada tunda har tayi sakacin Datasan sirrinsu tayi alkawarin sai ta Daidaita Rayuwarsu daga ita har Anty Amarya kuma da yardan Allah zama da ya Danmallan yanzu ta fara Zama Daram Kuma Haihuwa da izinin Lahi indai Allah ke badawa sai ta Rokesa ya bata Ta Haifar masa dozin yan Bakinciki da mahasada sai dai su Fadi su mutu Allah Sarki bawan Allah yana chan yana aikinsa a nan an saka sa agaba Allah Sarki Hajiya da mallam kuna Zagaye da makirai da mugaye baku sani ba.
Ita ne nan zata zama sillar Tonuwar asirinsu.
An riga anyi walkiya ta gansu.
Sannan an Dade ana ruwa kasa tana Shanyewa..
Ita nan Amina Aminene ikon Allah badai ta mutum ba sai ta Allah kainuwan Dashen Allah indan Rana ta fito Tafin Hannu bai isa ya kareta ba..Daya bayan Daya sai sun tsinci abunda suka shuka wannan alkwarinta ne..!
Kukan da Amina bata samu tayi ba sai yanzu ya kwace mata sai da Filon Datake kwance akai ya jike da Hawaye kanta ciwo yake yi Idanuwanta sun mata nauyi ga Cikinta na murdamata Har da yunwa tana jin Hajiya ta shigo Dakin bayan ta Dawo daga Falon mallam sukace bata jin Dadi ta shigo ta Dubata ita kuma ta Tusa kanta cikin Hijabi tayi Luf kamar mai barci har ta fita tana fadin Ta samu barci.
Duk tana kwance taji Su Hamida sun shigo sun yi sallar mangariba sai alokacin Hajiya ta leko tana Fadin"Hamida ku tada Mamah mangariba tayi..!
Hamida ta mike ta isa wajen Amina tana tashinta kafarta tataba Taji Jikinta kamar wuta ta Dago tana Fadin"Zazzabi ya kamata jikinta Zafi..!
Hajiya ta kariso Dakin tana Fadin"Asshsha..Mamah Daure ki tashi kiyi sallah sai kici wani abu ki sha mgani..!
Dole Amina ta mike Hajiya sai da ta Tsorata da ta ga yadda idanuwanta suka koma Cikin wani yanayi tace"Amina meya faru kike kuka kinga idanuwanki yadda suka kumbura kuwa..?
Amina ta mike Zaune tana fadin"Hajiya Yaya na tuna..Sai na fara kuka sai kirjina ya fara ciwo da kaina sai Zazzabi ya kamani..!
Daganan kawai ta saki kuka Hajiya ta Dafa kanta Cikin Tsausaya tace"Addu"a zaki mata in kin Tuna ta kin ji ko mamah ba kuka ba..?
Kai ta gyada tana kara sharan Hawayen wasu na ambaliya ita ta mike ta kama Aminar da Jikinta ke Rawa ta kaita Tiolet ta barota ta Fito tana kallon su Hanne da Jikinsu yayi sanyi tace"Zo ki kar ban mata magani ke kuma Hamida shiga kitchen ki zubo mata abinci ga Jawaad ma chan afalo ki zubamai yaci kafin yayi barci.!
Da toh suka amsa mata ta fice suka bi bayanta Hamida tayi yarda Hajiya tace ta Zubama Jawad Jallop din Taliya da Miyar kifi ne ta Zubama Aminata kaimata ta iske tana Sallah a Zaune Hanne ma ta kawo mata mganin da Ruwa suka koma Falo suka barta kada su Dameta.
Tana Idar da sallah ta zauna sai kuka take yi ta rasa addu"an ma da zatayi kawai sai ta Daga Hannu tana rokar ma Mamanmu tabewa da bala"in Duniya kala kala tanayi tana kuka Kafin ta kife kanta ta cigaba Tana wajen aka kira isha"i daga Zaunen ta yi sallar ko abincin bata kallah ba sai da taji kamar Hajiya zata shigo sannan ta Jawo Filet din ta fara ci Turawa kawai take yi ko Rabi bata ci ba Cikinta ya Cuse zuciyarta ta fara tashi ta Nufi Bayi a guje sai amai sai da ta Amayar dashi Duka sannan ta koma gefe tana maida numfashi koiya Fitowa batayi ba sai da Hamida tazo ta fito da ita ta iske Hajiya da Hanne afalon abincin tace a Dauke a Hado mata Tea mai kauri to shi ta dan samu ta sha ya Zauna ta hada da panadol Hajiya ta fice zuwa shashen mallam ta Sanar dashi cikin wani yanayi yace Allah ya Sauwake in ba sauki gobe sai Hajiya ta kaita asibiti tun abunda ya Faru