Showing 111001 words to 114000 words out of 145917 words

Chapter 38 - TAFITA ZAKKA BOOK 2 COMPLETE.txt

04 Nov 2024

83962

faman mata fifita da Hijabinta Sakina na kallonsu tana jin kamar ta mutu saboda bakinciki.
Kan Mamanmu na kasa ta fara mgana.


"SOYAYYAR SA"IDU CE SILA..."


















*Janafty**TFZB2026*


*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*




Gabadaya Ilahirin Falon sai da kallo ya koma kan mamanmu cikin mamakin kalamanta,ita kuma kanta ta kara saddawa kasa hawayenta na diga saman cafet din Daya malale falon Hajiya ta cigaba da fadin'"Tabbas kamar yadda na fada da farko Hakane soyayyar Sa"idu ce ta kaini ga komar Nadama dana ke ciki..!


Na taso tun ina karamata ban taba ganin wani Namiji daya taba Burgeni kamar Shi ba,Tun tasowata shi kadai ne Namiji kwara Daya daya ke Burgeni Sannan na kamu da sonsa da kananun shekaruna batare dana sani ba,Sa"idu ya shiga raina yayi kane kanen da bazan iya rayuwa ba sai da shi Tun Lokacin suna Gusai kafin barowarsu chan su dawo nan Gumel da Zama saboda Sa"idu yasa ban taba Daga kai na kalli Samarin Dake kara kaina akaina ba ina ganin kamar zai so ni watarana sannan kuma Hankalina da duka Tunani ya karkata akansa shi kadai.
Sai dai me..?sai da girma ya fara kamani Sa"annina suna aure sannan na Fahimci bana gaban Sa"idu bai taba min wani duba ba sai na yan"uwanta duk da kaunar da nike ta Nuna mai a Fakaici in yazo garin yazo Gidanmu Tunda ni ina matsayin Diyar abokin wasan Marigayi Baba Aminu ne,yazo kaida Babani Lokacin Tana Raye bana iya sukuni na Dinga Bare baren jiki kenan a kansa bani da wani Sauran sukuni ammh bai Taba Daga ido ya kalleni ba ballatana yasan Halin da na Dade aciki alokacin har Babani sai da ta Fahimci ina son Sa"idu so kuma bana wasa ba.
Hankalina bai tashi ba sai da naji Zencen auransa ranar sai da nayi karamin Hauka Babani Allah ya jikanta ta Dinga Tausata ta bani Hakuri akan nayi hakuri na Cire Sa"idu a raina na bama wani Cikin Manema na Dama tunda dai Sa"idu bai Juyo gareni ba na Hakura dashi alokacin kamar in make Babani haka naji Sai dai ban nuna mata ba ammh a wannan gabar gaba nake kullawa ga Duk wanda yace na Rabu da Sa'idu ko waye shi kuwa..!
Auran Sa"idu da Hadiza kadan ne ya Rage bai kaini kushe wata ba Saboda Bakinciki da Zafin kishi har sai da na Fara Tunanin na kamu da ciwon zuciya ammh duk da haka ban makara ba sannan ban cire rai ba.
Ana cikin wannan Halin Babani ta amsa kiran Allah ta rasu dani a bakinta da Fatan na yi aurre kada na jirasa ammh ban jita ba Tunda ni kadai ce tare da ita bayan bakwai dinta sai kawu Salisu ya maidani babban gidanmu ina zaune a wajensa..!
Saboda Sa"idu da Soyayyarsa sai da Kaf sa"o"i na suka tafi gidan mazajensu har kannen baya na ma an fara aurar dasu a wanchan Lokacin ana auran wuri ammh ni nafi Shekara ashirin ko Tsayayyen mgana bata akaina Saboda bayan Sa"idu har Abada bana jin zan iya bama wani Namiji Dama.
Kwatsam Naji Labarin Haihuwar yaya da yadda Sa"idu ya dinga rawan jiki akanta da abunda ta Haifa sai Gyambo na ya Dawo sabo naji bazan iya Hakura ba,Da taimakon wata kawata Samira da mukayi Primary tare na Zayyane mata Damuwata tace ta kwana gidan Sauki ita ta Daukeni ta Fara kaini gidan wani malami ko Boka zan ce wanda ke mata aiki akan mijinta acikin garin Tsafe na ZAyyanemai Halin da nike Ciki ya Tambayeni me nake so nace Sa"idu nake so..Ya aureni ko ta Halin kaka ne yana so ko baya so ni ban Damu ba kawai Burina na ganni agidansa a matsayin matarsa..!
Yace an gama ammh zan zube kudi masu yawa na karin aiki ban Damu ba Daman ta Fadamin na Tanadi kudi alokacin wajen Biyan Bukatata komai zan iyayi Zoben Zinaren da na gada wajen Babani na Saida na yi amfani da kudin wajen jawo cikar Burina.
Kamar wasa sai ga karamar mgana ta Zama babba kawu Salisu ya Kira Sa'idu akan yazo yayi auran zumunci Dani alokacin ko gaddama bai yi ba ya Karbi mganar Daganan na Fahimci zama ba nawa bane samira ta Budemin ido da shiga malamai Domin Cimma Burina ban shiga Gidan Sa"idu ba sai da na saka aka kafani sannan aka Saka soyayyata da kaunata a zuciyar kowa banda ta Sa"idu domin bai kaunace ni Fiye da yadda nayi nazo ba,yafi kaunar yaya da Jafar d'anta data Haifa.
Wannan shine Bakinciki na Biyu dana taba Fuskata agidan Sa"idu bayan aurena dashi,Da Farko ina ganin Komai ya kare tunda na auresa ammh Daga baya sai na Fahimci zama bai ganni ba Duk da kuwa Daga Su mallan har ya"yansu suna so na da Girmamani Uwa uba kuma Yaya itama ta Sakarmin komai kamar yadda na nuna Dayan fuskata ta Salihai.
Na Dade ina Fama da kuncin zuciya da Bakimciki kauna da wannan Tsausayin da bana ganinsa akan kowa sai akan yaya ni kuma sai dai Zaman Tsausayi da yan"uwanta ka ban taba ganin wannan kaunar da nake son gani atare dashi ba Sannan sai na Fahimci Duk wani Buri na Sa"idu yana kan Jafar ne bashi da sukuni in yana gida yana Tare dashi ko da Ranar ni ke da girki sannan duk kokarinsa na yaboye wannan kaunar bata Boyu awajena ba Dalilin Dayasa Idona ya Rufe da Kishi kenan da Bakincikin yaya da ya shiga raina na har Abada.
Hankalina ya kwanta dana Samu Cikina na Farko ina Tunanin Namiji zan Haifa nima Sa"idu yayi rawan jiki akaina da abunda na Haifa sai dai kuma ina hakan bata Faru ba haihuwar ZULFA sai ya koremin wannan Burin nawa sannan kuma sai na Fahimci kamar Sa"idu bai yi murna da wannan Haihuwar ba Duk da yadda ya dinga min Hidima yaya da Hajiya na Tsaye kaina ban taba Gani ba Saboda gani nake yi Itace ta Hanani Samun abunda nake so tun Farko Sannan tasha gabana a zuciyar Sa"idu.
Na yi ta neman Samira domim mu koma wajen mallan sai na samu Labarin mijinta ya tafi da ita Lagos inda yake Neman kudinsa sai hakan ya katsemin hanzarina ban koma wajen maallam da wuri ba har Tafiya ta Cigaba da tafiya alokacin Yaya ta Haifi Jadwa da Jaleela ni kuma ina Goyon zahra kaf alokacin ni nake rainan duka ya"yan da yaya ta Haifa Saboda na kara jawo Hankalin kowa da Tunanin kirkina akansu kuma naci Nasara na zama ban damu da komai ba a Bayanne a boye kuma ba wanda ya kaini Bakinciki.
Hankalina bai kara tashi ba sai da naga na kara Haihuwar Zulaihat ban samu Namiji ba sannan ga Jafar ya girma sai nake ganin yaya ita ke da gida ni kuma ta barni bani da Tsuntsu ballatana ta tarko sai nayi Shirin komawa wajen mallam sai dai nayi Rashin Sa"a an ce ya tashi Daga nan kuma ba wanda yasan inda ya koma Hankalina ya tashi Saboda alokacin na kasa Hakuri so nake ko ta Halin yaya ne na sami mafita na gaji da Kunsan Bakim cikin Sa"idu da yaya.
Hakanan na Dawo gida tunda bansan wani Malamim ba sai dai kafin na Samu mafita zuciyata ta riga ta gama kekyashewa Tsanar yaya da ya"yanta ya gama Cikamin zuciya wannan Bakincikin Tun aurena da Sa"idu yake Cikin Raina bai Taba gushewa ba Sai Ranar da YAYA ta bar gidan Duniya..!
Mamannu ta karishe Fada tana gunjin kuka Mallam ya girgiza kai Cikin Wani yanayi yana Fadin"Innalillahi wa"inna ilaihirraju"un..!
Kafin ya karisa ya samu Daya Daga Cikin kujerun falon Hajiya ya Zauna Rawaninsa duk ya jike da zufa Aba kuma yana Durkushe inda ya Sulale kansa na kasa ba wanda yasan Halin Dayake ciki su Nasir da su Nazir kuma duk kasa suka sulale suka zauna jin wannan labarin mai kama da al"amara.
Su ya Jadwa da su Jaleela suma kafafunsu ne ya kasa Daukansu suka zube nan saman cafet suna Faman kuka kada su Zulfa su ji Labari gabadaya kowa da abunda yake sakawa acikin ransa Amina kuma na Rumgume jikin Danmallam Tana kuka yana faman share mata Hawaye yana Shafa bayanta Jafar kuma kansa ya Dukar kasa Hannunsa Daya Dafe da kan nasa ya kasa yarda da abunda yake ji kuma yake gani
Gabadaya kowa acikin Falon ka kallah sai ka Hango tashin Hankali da al"ajabin wannan abunda dake Faruwa.
Mamanmu ta Dago Jajayen idanuwanta ta Sauke kan Anty Amarya da jikinta ya fara rawa sai alokacin ta Fahimci Komai fa ya kare sai dai babu wani tsumi ballatana Dubara.
Cikin Muryan kuka da Nadama Mamanmu ta Cigaba da Fadin"Ban taba Sanin bayan ni agidan Baba mallam akwai mai irin Halina ba Sai daga baya..Har ga Allah da Farko bansan Haka marliya take ba sai da watarana na jita tana waya da malamin Dake mana aiki kan Hajiya da mallam alokacin nasan itama irina ce..muna neman abu Daya agida Daya sannan alokaci Daya..!
Ban nuna mata na jita ba Sai daga baya,Na koma na nuna mata fuskata na bayyana mata Duka Burina da Fatan zata bani Hadin kai mu cure waje Daya wajen Cikan nmu burin..!
Tafada tana kallon Anty Amarya da kallo ya koma kanta komawa tayi ta Zauna Dabas saman Cafet sai kuka Cikin wani yanayi ta cigaba da fadin"Alokacin da Balaraba ta zo min da wannan bayanin na tsorata Saboda ko ni ban taba Tunanin haka take ba..Ammh data zauna ta warwaremin komai sai na Fahimci Rauninta nima ina Cikin irin haka..Sannan in muka Hada Hannu zamu cika namu Burin atare..!


Mallam Dake zaune yana jin abun al"ajabi ya Bude Bakinsa Cikin wani yanayi yace"Ke menene naki Burin..?
Burin daya sa kika fifita Duniyarki Fiye da Lahirarki marliya. ?


Anty Amarya bata iya kallon mallam ba Saboda yadda taji muryansa ba wannan amon ballatana karkashi Abunda ke Faruwa ya Dakushe komai Tana sharan Hawaye ta Cigaba da Fadin"Ni burina shine na Zama Tauraruwa a wajenka..Na zama ni ce agabanka kafin kowa..Sannan Burina na zama na Dara duka matanka a wajenka..Sai dai ina burina bazai taba Cika ba indai Hajiya na Duniyarka na yi barnar kudi akan ka mallam da Hajiya Saboda kawai na Zama Tauraruwa a wajenka sai dai hakan bai Samu ba kowani aiki baya Tasiri akan ku saboda kun rike Allah sannan ko acikin Wani Hali baku daina ambatonsa ba. !
Sannan tun zuwana gidan nan na Fahimci Hajiya ta yi mana Fintikau,Komai naka itace,Daga ita Sai SA"IDU sune kadai suke gabanka da su kake shawara sannan uwa uba Sa"idu ne ke jan Ragamar Duka Dukiyarka nayi iya Bakin kokarina na Raba hakan sai dai ban cimma gashi ba..Sai na Sauya shawara da taku..Na Fahimci in ni bazan zama Tauraruwa ba ta Sanadin Sakina zan iya Cika Burina Har fiye da yadda nake Tunani..!


Tunda ta ambaci Sakina Danmallam ya zura mata ido yana kallonta sakina kuma jin an zo wannan gabar kawai sai ta kara Volume din kukanta ta soka kanta Tsakanin Cinyoyinta tana gunjin kuka ko Aliya Dake gefenta bata da karfim gwiwan lallashinta.
Anty Amarya na jan Hanci da majina ta Cigaba da Fadin"Har ga Allah Lokacin da na Dauko Sakina ta zauna awajena da zuciya Daya ne sai daga baya..Data fara girma na Fahimci Tana matukar Kaunar Umar in ta gansa ta Dinga mai rawan jiki kenan shi kuma alokacin bata gabansa ita da su Jidda da su Nazifa duk Daya ya Daukesu..Ban tabbatar ba sai da na Samu Sakina mukayi mgana ta Nuna min in ba Umar ba bazata iya auran kowa ba Daga Lokacin na hango Cin ma nasarata ta bangaran Sakina..!
Ni na shiga na fita na Karkato da Hankalin Danmallan akan sakina..Duk da alokacin akwai ya"yan malamai manya wadanda suka fita komai da suka so su hada zuru"a da Maallam kwatsam yace Sakina yake so..Nasam ko Hajiya alokacin tayi mamaki Sanin ba wata alamar Soyayya a Tsakaninsu sai dai sanin ita bamai yawan maida kai kan sha"anin Umar bane yasa bata nuna komai ba ko a Fuskarta ba..!
Hajiya ta jinjina kai tabbas ai Biri yaso yayi kama da mutum Rana Tsaka Danmallam yace Sakina yake so ashe Ba yin kansa bane lalle Allah shine Sarki.
Anty Amarya tacigaba da Fadin"Mallam kuma bai nuna komai ba sai ma farinciki zai yi tuwona maina..Tunda yarcda ya rikeni Sakina Tsakani ga Allah haka yake rike da ya"yansa Daya Haifa,ammh duk ban gani ba Zuciyata ta kekashe da cikar Burina..!
Ban yi salama ba sai da aure ya Kullu Tsakanin Umar da Sakina sannan naji Hankalina ya kwanta sannan na sanya aka doramai shakkar Sakina da Duk abunda zatamai bazai taba gani ba ballatana ya Dauki mataki akanta Shiyasa sai tayi ta yin abubuwa bai Taba Daga ,kai ya Dubeta ba Sannan wannan aikin mai girma ne Tunda shima yana da Tsari ajikinsa Dakyar aka samu nasara akansa..!
A wannan gabar ne muka Hada hannu da Balaraba wacce ainihin sunanta ne Dayyaba..Ni kuma marliya nake ammh ana Kirana da Madina sai muka juya sunayemmu Domin kada Bacin rana a fahimci in da muka Dosa..!
Ni na kai Balaraba wajen malamin Dake min aiki anan Dutse Bukatarta ta Farko shine ayima Jafar mugun asirin da zai Fandare ya zama gagararree ya bi Duniya ya lalace kada yaji mganar yaya ballatana ta Sa"idu ya Zama YA FITA ZAKKA Acikin Dangi wanda Daga karshe Sa"idu zai gaji ya tsine mai kada dai ya amfana da Haihuwarsa har Abada..!
Sai akaji goggo Husai ta saka Salati Tana kuka tana Fadin"Innalillahi..Ammh wlh Balaraba kin cika bakar muguwa azzaluma..!
Sai kawai ta koma ta zauna tana Fadin"Allah yayi gaskiya..Zai Tsare bawansa a duk inda yake..!
Jafar kuwa ko Dagowa bai yi ta kasan Inda yake zaune Hawaye ne ke Digar masa Danmallan kuma Hannayensa Jimke Cikin na Amina tun labarin Anty Amarya na Sanadin Auransu da Sakina yake ta Hailala acikin ransa..!
Mamanmu kuka take yi kamar ranta zai fita ita da Anty Amarya da suka san yau komai yazo karshe..!
Ba wanda yace musu kala su kansu ya"yansu zuwa Lokacin sun Fahimci komai ban da tashin kukan au bakajin komai afalon..!
Mamanmu na Toshe kukanta ta Cigaba da fadin"Sai dai an samu matsala..Aikin sai ya kuskure maimakon Jafar sai ya Sauka kan AMINA tun Yaya nada Tsohon Cikinta alokacin..!.
Sai kallo ya koma kan Amina wacce ta kifa fuskarta kan hannun ya Danmaallan tana ta kuka,mamanmu na kallon Amina ta gyada kai tana fadin"Tabbas abun bai sauka kan kowa ba sai kan Amina..Mallam din da kansa ya fadamana haka ni da Madina da muka koma da Korafin aiki bai ci ba..Ya sanar damu aiki yaci Sai dai ba akan Jafar ba,akan Abunda ke Cikin Yaya..!
Alokacin gani muke kamar wasa sai da Yaya ta Haifi Amina sannan muka gasgasta kowa yasan tun Haihuwan Amina ta fita zakka cikin ya"yan gidan da kowa ma,sai kuma nayi amfani da kissa na,na rika jan Amina ajiki ina nuna nafi kowa sonta tunda kowa baya kaunarta Saboda Rashin kunyarta da Kuma Yadda ta addabi kowa ban so Amina ta tsaya haka ba naso ne ta Lalace tabi Duniya ta Zama Karuwa sai dai ina burina bai Cika ba Allah ya Tsare Amina duk Rashin kunyarta bata mu"amala da maza ba Sannan Tarbiyan gidan su data gidam Baba Mallam ta Zauna mata Daram Sannan Allah ya Tsareta da Fadawa wannan Halakar..!
Duk soyayyar da nike nuna ma Amina na karya ne bayan Sihirin Dake tare da ita nima na bada tawa gudummuwar wajen kara Lalata Rayuwarta,Ban taba mata Fadan tayi ba Daidai ba,Duk da alokacin in na Fadamata zataji Domin na Fahimci Duk Duniywa bayan ni da su Hajiya Amina bata yarda da kowa ba sannan tana kaunata Fiye da yaya data kawota Duniya da hakan nayi amfani na Gurbata rayuwar Amina ban taba bari ta ma kanta wani abu ba bana so watarana hakam ya amfaneta sai na Zabi na Sangartata kada ta iya komai ta tashi ahaka ta kuma rayu ahakan na Tabbata watan watarana sai haksn ya Zama illah agareta.
Saboda irin Kaunar da nike nuna mata ba wanda ya taba Fahimta ta Komai sai dai in saka Hamida Amina kuma na Dauketa wata Shashasha ce da bazata iya moran rayuwarta ba Sannan na kara nesantata da Mahaifiyarta yar da har Yaya ta koma ga Allah Amina ko da na Minti Daya bata taba rabarta ba. !
Amina ta Dago jajayen idanuwanta tana kallon Mamanmu kallon Tsana da wani Bakimciki haka Hamida itama da su Zulfa suke kallonta Cikin kyama da wani Takaici Aba dai bai Dago kansa ba har alokacin..!
Mamanmu bata Damu da kallon da suke Binta dashi ba ta cigaba da Fadin"Duk abunda kuka ga Amina nayi ba yin kanta bane..Tana da Sihiri ajikinta sannan da Shafar aljanu su suke sakata ya wan tsorata da kuma Mugayen mafarkai sannan duk abunda ya Faru da Amina kan Aminu na sani ammh ban taba Hanata ba..Ban kuma nuna mata na sani ba da Gangan nake ijiye wayata in da Zata gani saboda ta Dauka alokacin Naso ne Aminu ya lalata Amina Ya yi mata Cikin da zai yi Sanadiyar tsarwata zuciyar Sa"idu da yaya Tunda na Fahimci har ahakan Kaunar da suke ma Amina na Dabam ce ta fita zakka ko acikin ya"yansu ita din mafi
soyuwarsu ce..!
Wannan Karon har Hajiya sai da ta Saki Salati Amina taji kamar dan Ciikinta ya juya ta fara Kokarin tashi Daga jikin Dannallam kawai sai ya kamata ya Rumgumetw zuciyarsa na Bugawa Fat Fat ammh bai Daina kiran sunan Allah ba kada ya rasa natsuwarsa Amina ta nitse Cikin kirjinsa ta wani Fashe da wani marayan kuka Mamammu ta Cutar da ita Cutarwa da bazata taba iya yafe mata ba..!
Mamanmu kanta na kasa tacigaba da Fadin"Sai dai Burina bai cika ba..Allah ya tsare Amina Daga tarkona..Acikin wannan tsukin mallam ya Shammacemu ya Daura mata aure da Danmallam auran daya sa na Harzuka Madina ta harzuka itama,Auran da shine Silar Sanadin mutuwar YaYA..!


"KARYA KIKE YI..Hadiza bata mutu ba..Ke kika KASHETA Balarabaa..!


kawai sai jin kakkusan muryan Aba sukaji ta karade Falom Cikin wani amo mai karfi da ba"a taba jinsa yayi irinsa ba..!
Sai kallo ya koma kansa ayadda Idanuwansa suka kada suka yi Jajir kamar gauta sai ya baka Tsoro ya mike jikinsa na

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login