Showing 81001 words to 84000 words out of 145917 words
ne ba"ayi ba kada aji kunya su Hajiya an yi Zani an yi Riga. !
Sakina tace"Zai iya yuyu wlh Anty..!
Allah ma yasa hakan ne..!.
Ta amsa mata da Ameen suna Dariya Ranar dai suna gidan har Dare wannan karon Sarood Shashen Hajiya ta Zauna tare da su Hanne tunda suna gida basu da Jarabawa wannan karon Sakina taji Haushin zuwa da ita da akayi yasa bata jata ajiki kamar baya ba
Sai Dare suka koma gida,Washegari shi kadai yazo su suna gida Shashen Hajiya ya yada Zango aka Bude kaya ya bama Hajiya Tsarabanta na Turaren da Hijabin larabawa na mata sai Dogayen riguna guda Biyu masu kyau da Tsada da takalmi haka ma Anty Amarya da Haj.Nasara da Haj.Uwa dogayen riguna da Turare,Wannan karon har Hanne da Hamida yama Tsaraba domin bazai manta da kaunar da Amina ke musu ba, waya goma sai ta ambace su shiyasa daya siyo mata suma ya siyo musu Ya kuma nuna mata tsaraban Amina da Siyayyan kayan Jariran Da yayi,Hajiya Taji dadi sosai ta dinga yabawa sai dai Bata ga Tsaraban Mamanmu ba Tunda Har Aba ya yoma Tsaraba Sai alokacin ya tuna ma da ita Har ga Allah bai yi niyyar bata bane kawai Saboda tundaga Labarin da Amina ta basa yaji matar bata kwanta masa ba sai bai nuna ma Hajiya ba yace ya manta ne sai Hajiya tace bari ta bata Cikin nata.
Sai ta hada mata da Ruwan Zam zam da Dabino.
Hajiya ta aika ma su Haj.Nasara da Tsaraban Danmallan suna ta godiya haka su Hanne suka yi ta Tsallen murna,Ganin har dasu a Tsaraban Hamida da Hannen ma suka kai ma Mamanmu nata ta karba tana ta godiya da Santi tana auna kanta in tayi ma Aba kwaliya da ita..
Mallam dai Turarensa ne na Arab sai Zam zam da Dabino.
Tsaraban sakina gida yakai mata nata Sai jin Dadi take yi ganin har da takalma ga kayan masu kyau da Tsada
Na Amina kuma wajen Hajiya ya barsu su hanne kuwa tunda suka ga basu ga Amina ba kwana uku da Dawowar ya Danmallam ba labarin Dawowar Amina sai suka cire rai da Mganar Hajiya da kullum take sanar dasu Amina zata dawo nan kusa sai suka Sare..
Gashi har sun yi nisa a jarabarwarsu suna gabda gamawa gabadaya sai basa jin Dadin zama,ba Amina suma sun yi ahuru kamar basu agidan da ko da Amina ke nan wlh sai su shiga gidan mallam sau goma gidan Aba ma haka Rashin jinsu kawai yasa Dole ma asan dasu ammh yanzu sai a kwana awuni ba ba"aji ko motsinsu ba.
Islamiya da Boko ma an gaji da Cigiyar Amina Daga baya ma su Hanne cewa kawai sukayi an cireta Daga mkaranta bata agarin harta mariya abokiyar fadanta da malaman makarantarsu Mallam Datti da kansa ya Kira mallam ya tambayesa Amina Mallam yace mai Amina bata gari ne shiyasa..!
Kwana hudu da dawowarsa Ranar yazo Gidan da Safe Ya shiga shashen Hajiya suka gaisa da sauran matan Sannan ya koma wajen mallam to basu Dade da Mallam ba aka kirasa agidan mai anguwa Idi ya tafi kaisa Aba kuma baya nan sai ya tafi Dakin Nazeem ya dan kwanta ya Huta Sarood Tun abunda Sakina ta Fadamata take shamai kamshi sai bai Biye mata ba Sakina kuma kamar rana Daya zai mata Ciki takuranta ne ya Ishesa,yake barin mata gidan ita da Sarood din su ci kansu.
Amina kuma tun washegarin ranar daya sauka daya Kirata bayan ya saka Layinsa na nan ya fadamata ya Dawo suka gaisa har take fadamai sun je asibiti ta fara awo sannan an mata Scan,basu wani jima suna mgana ba yace zai sake kiranta,kuma bai Samu Lokaci ba,Basu zauna sun yi mgana da Hajiya bane yana so yaje ya ganta kafin ya koma tunda ba wani Dadewa zai yi ba Sati Biyu ne zasu yi,zasu koma.
Yana kwance har ya fara barci yaji sallama kamar daga sama yana Bude idanuwansa ya ci karo da Hanne da Hamida suna rabe raben shigowa Hanne na Tura hamida itama tana Turata mikewa Zaune yayi Daga kan gadon yana fadin"Ku shigo mana..!
Jin haka yasa suka shigo Dakin kansu na kasa kamar wasu marayu duk suna Sanye da manya Hijabi har kasa mamakin ganinsu yayi gabansa suka Duka kamar masu neman gafara gaishesa sukayi ya amsa yana Dan Nazarinsa dazu a falon Hajiya yaga Hanne sun gaisa hamidan ne dai bai gani ba. !
Hamida kuma hanne ce taje ta jawota kan suzo su tambayi Ya Danmallam Tunda Hajiya taki fadamusu inda Amina take kila shi zai fadamusu shine suka zo a bakin Hajiya sukaji yana Dakin ya Nazeem Shine suka zo sun kuma kasa mgana saboda ba Sakewa Tsakaninsu sannan yana musu kwarjini.
Shine yaga suna Sunkuye sunkuye kai da taba juna yayi mirmishi kafin yace"Lafiya..?
Baku je makaranta bane yau..?
Hanne tace"ai jarabawa muke yi yau bamu dashi sai monday..!
Ya gyada kai sai yanzu ya tuna da Tsarin Tun farko,tunda Hajiya ta sanar dashi yadai manta ne,Cikin Sanyinsa yace"Kuyi mgana ina Fatan dai lafiya ko..?
Hamida ta sanda kanta kasa tana Fadin"Dama..Dama..Muna so mu tambayeka ne ya Danmaallan..!
Zama ya gyara yana Fadin"Allah yasa na sani..!
Hanne ta zungura ita kuma sai ta kara kasa da Murya tana Fadin"Dama kan mganar Amina ne yaya..
Kai Tsaye yace"Amina..?
Me ya faru da Aminar.?
Hanne tace"Bakomai tunda Hajiya ta tafi da ita har yanzu bata Dawo ba..Muna ta tambayanta ina take taki gayamana gashi har mun fara jarabawa ba Amina muna kewarta ne Hajiya sai tayi ta ce mana zata Dawo Zata Dawo ammh shuru..Shine mukace bari muzo mu tambayeka muji ko kasan inda take..?
Wlh kuma bamajin Dadin Zama ba Amina..!
Hanne ta karbe da cewa"Kawayen mu sai tambayan mu ita suke yi..Kowa sai yace ina Amina.?
Mu kan mu muna son sanin inda take..!
Sai da suka gama Mgana yana kallonsu kafin ya saki Mirmishi ya tuna sanda ya kira Amina yace ya Dawo abunda ta fara tambayansa yaga Hamida da Hanne..?
Don Allah ya gaishesu yace tana missing dinsu.ai shi shaida ne Saboda Rabin wayarsu mganar Hanne da Hamida ne ya Dade yana jinjina wannan kaunar Dake Tsakaninsu Amina tana matukar ji da Hanne da Hamida in tana Hiransu haka Zakaji Farinciki da Murna acikin muryanta Shi bai wani zauna dasu ba ammh yasan dai tare suke su uku ammh baisan Rayuwarsu ba gaskiya.
Gyaran Murya yayi kafin yace"Kada ku Damu Amina na Cikin koshin Lafiya..Itama tace na gaisheku sosai tana kewarku..!
Suka kallesa kafin su koma su kalli juna sai Hawaye duk ya Cicciko Idanuwansu Hanne tace"Muma muna kewarta don Allah tana ina..?
Kuma yaushe zata Dawo..?
Kai Tsaye yace"kuyi hakuri bazan iya Fada muku inda take ba..Ammh tana Cikin Koshin lafiya..Sannan zata Dawi kowani Lokaci itama bata manta daku ba koda yaushe Cikin Zencen ku take yi..!
Kawai sai suka fara mai sharan kwallah ya kallesu baki bude bai yi mamaki ba in ya Tuna yadda suka rika uban kuka Ranar da zai tafi da Amina gidansa.
Gyara zama yayi kallesu yana Fadin"ku share hawayenku..Ku Zauna Dakyau yau labarin Amina zaku bani Tundaga Farko har karshe..!
Yau ina so naji nima..!
Hama kurum yake son jin Labarin Amina,batare da yasan Dalili ba.
Jin haka yasa suka gyara zama suka Fara bashi Labarin Amina da yarintarsu Hanne tayi in ta gaji Hamida ta karbe in suka fadamai wani abu baya sanin ma yana Dariya jin jina Jidalin Amina kawai yake yi aransa ashe haka tayi nisa bai sani ba ?
Kirarinta ke basa Dariya in ya Tuna wai Aminene ikon Allah badai ta Mutum ba sai ta Allah lalle yarinyar nan sai Allah taci kuma kirarinta..
Hanne ta Karbe da Fadin"Wlh ya Danmallam Amina tana da kirki sai wanda ya Zauna da ita ya sani...Tana da son yan"uwanta sai dai akwai abu Daya Amina tana da riko in ta Tsaneka sai Alllah sannan tana da Fada da Tsiwa kuma bata Laushi ko bata da gaskiya sannan ga son jin gulma,Amina fada ko ba nata bane siyanta take yi a makarantar boko da Islamiya ba malami ko Dalibin da baisan Jidalin Amina ba,ba wanda ta Kyale tana da Fara"a sai dai bata Daukan Reni bata kuma son arainata kan Hamida da hanne Amina Zata iya yin komai tasha Fada saboda mu kuma duk wani abu da ake yi Amina ce gand leader din mu.
Ya Danmallam ga ni Amina wata Hudu ta bani Hamida kuma wata uku ta bata ammh nuna wa take kamar ta Girmemu Amina bata san Faduwa ba bata nuna gazawarta Wlh ko su ya Abida ban shaku dasu yadda na shaku da Amina ba tunda muka taso bamu taba Rabuwa ko na kwana Daya ba,Shiyasa Rashinta ya ke sakamu cikin Wani hali komai baya mana Dadi..!
Hamida ta karbe da Mirmishi tace"kuma ba"a zaman minti goma da ita ba"ayi fada da ita ba..tafi Fada dani Fiye da Hanne saboda ni bana gani na kyale Hanne kuma bata da yawan mgana,Mu yi fada mu Shirya hakanan muke zaune duk duniya ba wanda yakaimu sanin Amina sannan mun san Halinta sai muka ci Mganin zama da ita, jidalin Amina ni da Hanne kadai muke iya Daukan ta, ko Ciwo tayi kowa sai yaji wani iri saboda Amina mai Fara"a ce sannan tana da Dadin zama ga wanda ya santa sai dai kawai Fada da Zafin rai sannan bata Daukan Reni Haka Aminene take bata da tsoro bata Shakka Kirarinta badai ta mutum ba sai Allah..!
Ko abunda ya faru na Aminu Tsausayi ne wlh ba Halin Amina bane nan ta shiga bashi labarin soyayyar ta da Aminu tundaga farko Har karshe da abun da ya Faru Hamida ta kareshe da Rantsuwan wlh tallahi ya Danmallam Tsautsayi ne ammh wannan ba Halin Amina bane barta da Jidalanta ammh Namiji baya gabanta soyayyarta da Aminu kaddara ne ta Ubangiji..!
Da Dukkan Hankalinsa yake sauraranasu duka labaransu suna shiga kansa wasu labaran na Amina abun Dariya ne wasu kuma ya Dauki wasu abubuwa da mganar Data Fadamai akwai kamshin gaskiya ko wani yaro akawai irin yarintarsa ammh na Amina yayi yawa wannan Rashin Tsoro da rashin jinta yayi yawa ba nata bane ita kadai da gaske an kara mata ne duk da abun ya Tarda Halinta ne ya gasgasta mganar ta Dalilai da dama sannan ga abunda ya Lura dashi a wajenta lokacin da ya kusanceta din nan ya Fahimci akwai matsala sannan ga mgangan su Hamida sosai yaji tsausayin Amina da wani Kaunarta na shiga ransa bai sani ba..
Mganar Aminu kuma mallam yadan Fadamai kadan Daga Cikin abun da ya faru Lokacin bai wani mai da kai ba kan mganar tunda alokacin yana ganin Aaminar kamar ta riga ta gagarane aransa kuma sai yaji ya baci da jin Labarin yadda su Jafar suka Dinga Dukan mai mata gaskiya ransa ya baci da Yana Kasar sai ya hanasu ai wannan abun yayi yawa kamar sun sanu jaka su bazasu Fahimci wani abu kan Amina ba..?
Yayi mamakin da ko mallam bai Taba kaawo wani abu acikin Ransa ba sai dai kila wani abu Allah bai Cika bayyanasa da wuri ba sai Tafiya tayi tafiya mganar Aminu kuma bai Damu ba yasan ba son shi Amima ke yi ba yarinta ne da kuma kaddaran auransa da Amina shi kamar ma taimakonsa yayi sannan da kuma karfin rabon dake Tsakaninsa da ita
Mirmishi yayi har Hakoransa suka bayyana kafin yace"Wato Aminene dai ikon Allah ce badai ta mutum ba sai ta Allah..!
Hamida da Hanne sukayi Dariya suka Dukar dakai shima Dariya yayi yana tuna wai tace ma malamar corper dinsu tana warin maza kawai sai yaji wani abu mai gardi da Zumudi kan Amina na kara mamaye ransa
To ai a jidalin nata zata zama uwa..!
Lalle akwai kallo sannan Jidalin akwaishi kam
Nan ya samu ya lallaba su hanne yace zai hadasu suyi mgana da Amina ammh bai sanar dasu inda take ba sun ji Dadi da sanyi tunda Amina dai tana Lafiya sannan tunda yace zai hadasu susan bazai musu karya ba sannan yace kada su fadama ko Hajiya mganar da sukayi.
Adaran yayi ma Hajiya mganar zuwa Abuja Hajiya tace ko da yaushe ya shirya yaje mana ya ganta..
Kansa na kasa yace zai sanar da Mallam jibi sai ya tafi gobe zai je Dutse shi da su Sarood su gaida Aliya matar Aliyu tana asibiti Ciki na bata Wahala...
Hajiya ta jajanta kai Tsaye tace ma Danmallam ya Dauki Aliyu ya rakasa Abujan mana.
Cikin mamaki yace"Hajiya kin manta kin ce ko shi kada yasan komai..?
Hajiya tace"Ka sanar dashi nasan shima bazai sanar da kowa ba..Bai kyautu kaje kai kadai bane..!
Ko Jiya sai da nayi ma Sa"idu Tsiya kawaicinsa yayi yawa bai Taba Tambayana ina Amina ba ko ina na kaita ba.?
Anya akwai Uba irin Sa'idu kuwa..?
Cemin yake yarda da nayi Dake Hajiya yarda kika rikeni Tsakani ga Allah na Tabbata duk inda Zaki kai Amina Za"a kula da ita kuma bazaki kaita inda Za"a Cutar da ita ba .!
Danmallam mirmishi kawai yayi bai ce komai ba Tsakanin Baba Sa"idu da Hajiya ko mallam baisan Tsakaninsu ba ballatana shi da ba mazauni ba sun Dade suna Hira da Hajiya kafin ya mata sallama Shashen falon ya koma sukayi mganar Tafiyarsu Dutse gobe da zuwansu Abuja shi da Aliyu mallam yace yana da kyau hakan Aliyu ai Aminini sosai sannan ya bada Sakon gaisuwarsa ga Mamarsa Amina.
Daya fito daga wajen Mallam shi da Nazeem suka yi hira sai after 10 ya koma gida Sarood ta kwanta Sakina dai na Zaman jiransa ya riga yaci abinci shashen mallam shiyasa bai ci wanda suka shiryamai ba yasan Daman abunda take mawa shi har mamaki take basa zafin nema na kawo samu ne..!
Tunda ya Dawo bata barsa ya Huta ba koda yaushe abu Daya ce mata akayi haka ake samun Ciki..?
Koda yake duba da Cikar Burinsu ai yasa tama Fita daga hankalinta Kada ya Danne mata Hakkinta yasa ya Biye mata kuma duk Shawaran Anty Amarya ne Ta Dake ta maida Cikinta Datayi barinsa.
Washegari karfe tara na Safe suka Dauki Hanyar Dutse shi ke Driving din Sakina na gidan gaba Sarood na baya sun isa da wuri Ajiyan aka Sallami Aliyan tana gidan chan suka wuce Direct bayan sun ci abinci sun huta sai mazan suka shiga Cikin gari suka bar matan agida
Sakina da Aliya suna mgana da Hausa suna Yamutsan fuska suna zunden Sarood, ita kuma tana kallon su tana washe baki batajin me suke Fadi Daga baya ma tashi sukayi suka shige Ciki suka barta ita kadai afalo kamar mayya su kuma sai bayan La"asar suka Dawo abokansu suka ziyarta da sukayi makaranta tare da aiki ya kawosu Dutse da zasu dawo suna Hanya Danmallan yace gobe da Safe ya zo zai rakasa Abuja Aliyu bai kawo komai ba Tunaninsa wani abun zai kai Umar din Abuja.
Yasa bai matsamai da Tambaya ba ya amsa masa da toh Allah ya kaimu.
Bayan La"asar suka Dauki Hanya bayan su Aliyu sun rakosu da Fatan isa Lafiya da suka Dawo gidan mallam suka Sauka sai aranar suka shiga gidan Baba Sa"idu suka gaisa da mamanmu shima adaran ya shiga shida Aba suka gaisa da ita sai kallonta yake yi yana Nazarinta haka kurum daman shi tun Farko kirkirta bai mai ba sai kuma ta kara Dora kanta azargi da Aba ya shiga Shashensa ta fara tambayansa Amina harda sharan kwallarta na karya wai Hajiya taki sanar ma kowa inda takai Amina..
Mirmishin yayi kafin yace mata shima bata Fadamai ba sai ta fara sallallanmi tana Fadin Allah yasa to dai lafiya.
Har ya mata sallama ya fita yana Auna mganganunta Biri dai yaso yayi kama da mutum a kaunar datake ma Amina in har na gaskiya ne Amina Bazata kai wannan wattanin bata nan ba bata wani damu ba gaskiya bai yarda da ita ba daman mutum ya cika Kirki wani Lokacin mugu ne.
Sai dare ya kwashi matansa suka koma gida adaran ya Fada musu gobe zai je Abuja wani aiki zai kaisa ba su Damu ba ita kanta Sakina bata kawo komai aranta ba ta Dauka dai aikin zai kaisa kamar yadda yace.
Washegari kuwa agidan mallam suka Hadu da Aliyu bayan ya gaida su Hajiya suka Dauki Hanya,Hajiya ta bata Goriba da su Rama da zogale da kulu su gauta da yalo da Daffafiyar gurjiya akaima Amina sun yi mgana da Aisha ta fada mata abincin zamani Amina bataci sai na gargajiya.
Danmallan ya taho da Tsaraban Amina tare da Ruwan zam zam din daya riga ya karanta mata duka ayoyin dake karya sihiri aciki sannan da Sauran addu"o"in Tsari Domin ya yardan ma kansa Amina ba ita kadai bace.
A motar Aliyu sukayi tafiyar dayake sun tafi da wuri sha Biyu suka shigo Abuja Usman mijin Aisha Danmallam ya Kira yayi musu kwatance cikin Lokaci sai gasu a anguwan maitama Dayake gidajen akawai lamba sai gasu agidan Usman ya Fito ya tarbesu daman yana gida ya samu dan break yana Hutawa kuma shima sai da Safen nan Ya Dannallam ya kirasa ya fadamai suna tafe kuma yace kada ya Fada su Aisha..!
Sai da suka iso gidan ne Aliyu yaga Usman sanna ya kalli Umar yana Fadin"Daman gidan Aisha zamu zo..?
Ko wannan ba mijinta bane..?
Lokacin Usman din yayi gaba suna Binsa abaya zuwa Cikin gidan.
Danmallam yace"Eh ammh ba wajenta nazo ba..!
Aliyu Cikin mamaki yace"To wajen wa kazo..?
Ai naga har sako Hajiya ta baka ka kawo mata. !
Kamar bazai yi mgana ba sai kuma yace"Zaka ganta ita wacce nazo Dominta..!
daidai suna shiga kayattacen Falon na gidan Aisha.
*Janafty**TFZB2020*
*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*
Har cikin babban falon gidan Usman ya kawosu yana musu maraba suka samu Daya daga cikin kujerun falon mai zaman mutum biyu suka zauna suna kallon falon ko'ina tsab sai tashin kamshi yake yi sai talabijin dayake ta babatunsa shi kadai cikin Tashar Arewa24.
Usman kitchen ya wuce Direct saboda gida ba wanda ya tashi sai Saude mai aiki shima kiran Danmallam ne ya tashesa bayan ta gaisheshi yace ta kawo Ruwa da lemo akwai baki a falo ta amsamai da toh Cikin girmamawa.
Yana fitowa ya zauna saman kujera mai zamam mutum daya suka kara gaisawa da Danmallam da Aliyu.
Sannan Usman ya mike yana fadin"Bari na