Showing 75001 words to 78000 words out of 145917 words

Chapter 26 - TAFITA ZAKKA BOOK 2 COMPLETE.txt

04 Nov 2024

83941

Rayuwarsu ba.
Ya jafar ya fara fada yana Fadin"Hala iskancinta ta maka..? Ai Amina sai Allah..Wlh ya Danmallan ka daina Sake mata ne. !
Cikin haushinsa yace"Tambayata zaka bani amsa ko zaka Tsaya kana gayamin abunda zan yi da matata ne..?
Saj jafar ya rike baki yana yar Dariya kafin yace"Amina bata da Halin karya..Bata da kumbiya kumbiya ita Free take abunta bata da Tsoro sannan tana da kafiya da Taurin kai yadda kasan zuciyan kafuran farko bantaba ganin wanda duka baya Sata tayi Laushi ba sai Amina..Ko zaka kasheta sai tayi mgana sannan abunda yake gaskiya take fada
Bansanta da karya ba gaskiya..Sai dai Rashin kunya da tsiwa da Tonen fada da Yawon tsiya..!
Danmallam ya jinjina kai alamun gamsuwa kafin ya Datse kiransa ya jafar afili yace"Ko son Amina ya Danmallam ya fara ne..?
Dariya yayi kafin yace"Tab..bai Fada hannu na gari ba..Amina ai jidali ce..!
Danmallam kuwa suna gama mgana ya saki Huci Amina tana da gaskiya wani abu na Faruwa sannan ya Fara ZArgin Hajiya tasan wani abu shiyasa ta hana Amina ta zauna a gumel sannan kuma ta hana kowa yasan da Cikin jikinta tabbas ya hasaso wani abu..
Sai dai koma menene ya kamata yaje Negaria yaga Amina su yi mgana sosai sannan yaga ta ina zai Bullo ma al"amarin da ke faruwa agidansu karkashin Tarbiyan mallam..?
Lalle ana Zaton wuta a makera sai aka sameta a masaka..Zuciyarsa ne taji ta Bude da duka mganar Amina da Tsausayinta da bai taba jiba ba..Dole ya tafi gida cikin watanan mai Shiga abubuwa Dadama suna Bukatar yaje ya gabatar dasu tukunnah..!
















*Janafty**TFZB2018*


*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*


Tun daga ranar Danmallam bai taba kwana batare daya Kira Amina ya lallasheta ba ganin da gaske fa abun na cinta aranta Fatansa Allah yasa kada Damuwar ta haifarma da abunda ke cikin wata matsala sannan bayaso ta fadama kowa abunda ta Fadamai mganar tana Bukatar Bincike da Lura sannan ba kowa bane zai iya Daukan mgar har ya Fahimceta sannan yayi tunanin mafita Shiyasa yake kokarin kiran Aminar yana amfani da Hikimarsa wajen kara Lallashinta da bata Baki.
Wani Lokacin yafi Kiranta in yaje Wajen aiki ko in ya bar gida Zashi masallacin Madina ammh in yana Gida baya Kiranta Daga ita har Sakinar saboda Gudun matsala Ga Sarood kamar ta goyasa haka take ji Dashi bazai so yayi abunda zai ci mata Fuska ba shiyasa yake kiyaye wasu abubuwan sannan nauyi ne akansa ya kwatanta adalci Tsakanin mtansa.
Abunda Amina ta Fadamai na nan aransa kamar ya Tuntubi Hajiya da mganar sai kuma ya fasa yana Tunanin ta ina Zai fara duk da fa yana da Zargin Hajiya tasan wani abu Shiyasa ta Boye Amina da Cikin Dake jikinta,Mallam ma kamar Zai mai mgana sai kuma yaga ai bai da wata Sheda itama Aminar ji tayi bata Nadi murya ba Tunkarar wani da wannan mganar ma a yanzu bai taso ba,Sannan abu ne na Kashe rai duk da daman kowa yasan Mutuwa ta Allah ce sai dai mutum ya Zama Sanadinta.
Bangaran Sakina kuma ai ya Dade da Fahimtar mganar Amina Hakane kodaga yadda bata taba mai mganar Amina ba Ranar Dayake so ji ta Bakinta suna waya sai Rigima take mai kan yaushe zai zo ya Dauketa..?
Ita ta gaji da Zama agarin nan baya nan sannan ta yi bari tana son maida Cikinta,Mirmishi kawai yayi kenan mganar Amina ta fito su Burinsu kawai Sakina ta Samu Ciki ta Haihu..?
Saboda ya jarabata yasa yace mata Bata taba Tambaynsa ina Amina ba..?
Sai Sakina tayi Tsaki kafin tace"To ni ina Ruwana..Tunda ta bar min gidan mijina ban damu ba..Ba"an ce hajiya takai ta wani waje ba..?
Yana jinta ammh Daganan bai kara mata mganar Amina ba Itama Sakinan bata Damu ba,ita kamar ma Dadi Take ji tunda ta bar mata gidanta ai taje koma ina ne bata Damu ba Allah ya raka taki gona..!
Allah duk ya shafe musu Tunanin Mezai sa rana Tsaka a Dauke Amina Daga Gumel..?
Duk basu yi wannan Tunanin ba Idonsu ya Rufe da nasu Cikar Burin dukkansu.


******


Usman mijin Aisha ya Dawo washegari suka kai Amina asibiti shi da Aisha speacialist Hop suka kaita Inda Aisha ke zuwa in Bukatar Hakan tataso,anyi mata Scan cikin Amina Har ya shiga wata na Biyar sannan jininta yana sama kadan Saboda Tana saka Damuwa sannan kuma Sugar masu Ciki na son kamata ammh ita da Abunda ke Cikinta suna Cikin koshin Lafiyan an bata mganin karin jini su Vitamin c da sauransu sai kuma na cin abinci tunda Aisha Tayi Korafin batacin abinci Likitan yace Normal ne indai tana cin abunda Cikin yake so ba wata Damuwa...!
Ya sanar dasu zata fara zuwa awo Duk bayan Sati Hudu sannan in yayi shiga wata shidda za"a sake mata wani Scan din
Basu Dade a asibitin ba suka Dawo Gida suka ijiye Amina suka kara Fita kasuwa suka shiga Aisha ta Zabo ma Amina Dogayen Riguna guda Biyar da Wanduna plazo sai ruguna masu yalwar wadanda zasu mata Saboda ta kara kiba kaya wanda tazo dasu sun mata kadan sannan nata bazasu wadaceta ba.
Data kawo ma Amina taji Dadi sosai kamar ta goya ya Aisha tana Daga rigunan adakin Yakaka take fadin"Yakaka kalli Rigar nan bata miki kyau ba .?
Tana zaune saman Cafet tana Gogan goranta tace"Sosai ma ai sai ma kin sakata Ajikin ki takwarata ai mu duk kayan da muka saka sai ya karbemu..!
Ya Aisha na Dariya ta Fice tana Fadin"Ki fito kiyi ma Darling godiya yana Falo..!
Amina in Aisha ta Kira mijinta Da Darling mamaki take bata,agida shuru shuru kamar bazata aikata ba kamar ma batasan komai ba.
Kwashe kayan tayi ta maida a leda ta Saka Hijabinta ta fita falo ta Durkusa tama Usman godiya ya amsa mata yana Fadin"Bakomai Matar yayanmu..Kin dai ji abunda Likita yace ko..?
Ta gyada mai kai kanta na kasa tana jin kunya ya cigaba da Fadin"To sai ki yaye in kina Bukatar wani abu ga Sweety nan ga kuma Yakaka Dukkansu They are Their for u..!
Kanta na kasa ta amsamai Lokaci Daya damai godiya kafin tatashi ta koma Dakin yakaka tana Santin kayanta ta gwada wannan ta gwada wannan tana nuna ma yakaka ita kuma tana yabonta Amina ta gwada wata Riga Mai yalwa ta juya ta Sake juyawa kafin tace"Sai yanzu najini Daidai...Ammh wacce ya Aisha ta bani jan nan tamin kadan fa yakaka..!
Yakaka tace"To Daman ai irin wannan ne Daidai dake..Daga gani ba wani Girman Ciki Zaki yi duk a kiba Zai tsaya .!
Amina ta bata rai kafin tace"Wai sai nama kara Kiba yanxu..?
Yakaka na cin soyayyan gyadan da su Aisha suka siyomata a kasuwa tace"Af ai sai kin ninka kibanki na yanzu..
Ai sai Amina ta Zauna akasa ta Fashe da kuka Yakaka ta saki baki tana kallonta Kafin ta tabe baki tana Fadin"Yarinyar nan kin samu waje..Ki bari Balaraban Madina yazo sai ki mai wannan shagwabar..!
Amina Ta tura baki Batayi mgana ba Yakaka tayi Dariya kafin tace"Tsoro kike ji kada su kwace shi..?
Amina tace"Tab..Allah ya Tsareni ni bana tsoron su har ita gajeran ma..!
Yakaka tayi Dariya kafin tace"yauwa haka nake son naji Tsoro ai ba namu bane..kada ki Damu kina Haihuwa Zaki Dawo silandiyan dinki..!
Amina ta washe baki Tana Fadin"Da Gaske kike yakaka..?
Yakaka tace"sosai ma ai mu ko da kiban mu muka je mune agaba bazamu taba komawa baya ba. !
Amina ta amsa da wlh kuwa Daganan ta warware suka Cigaba hirarsu Daman kukan Aminar na Tabara ne da jidalinta.


Hajiya suna waya da Amina ta wayar Amina Tunda Aisha ta Tura mata lambar Aminar koda yaushe sukayi mgana sai Amina tace ina su hanne abasu su gaisa sai Hajiya tace ba yanzu ba ko Aba bata yarda ta Kira ba sai Mallam kawai ta Turo mata Lambarsa ta Kirasa suka gaaisa ya Dinga mata nasiha da Saka albarka yaji Dadin jin tana Lafiya kalau..
Amina tana jin kewar su Hanne sosai Kamar yadda suma suke kewarta Tunda suka ga sun fara Jarabawar Fita Amina bata Dawo ba suka Sare Hanne tace da sun san ba tare da Amina zasu zana Jarabawar Fita da Mallam ya bar su sun gama SS3 Kamar kowa sai dai ina bakin alkalami ai ya Riga ya bushe.
Duk damuwarsu basu kai Sa"adatu ba wanda hakan da mallam yayi yanuna cewa bazasu Dade agida ba suma zai aurar dasu Shine tashin hankalinta su kuma su Hanne Amina ce Damuwarsu Saboda rayuwar ba Dadi ba ta abaya ashe ba Rashi sukayi ba Tunda Amina na kusa dasu yanzu kuma da basu da tabbas din ina take sai Damuwar tafi ta baya,Sun gaji da Tambayar Hajiya sun kare har Mallam sun tambaya yace su tambayi Hajiya Hamida data tambayi Aba shima yace Hajiya bata Fadamai ba.
Ganin Hamida ta Damu ne yasa Mamanmu ta Kikkira su Jaleela ta tambayesu ko wajen su Hajiya ta kawo Amina ammh har Jordan ta Kira amsar Daya ne A"a sai ta fara Dawowa Hankalinta ta fara Tunanin ina Hajiya takai Amina..?
Har su Zulaihat ta Kira suma suka ce mata bata wajensu kuma kowacce ta Kira sai ta nemi karin bayanin ina Aminar ba"a ganta bane..?
Sai Mamanmu tace wayasani Hajiya dai tace Zata kaita Gidanjenku gashi Wajen Wata Daya da wani abu ba Labari sannan Hajiyar taki Fadan inda take in sukaji basa Damuwa cewa suke ai Hajiya bazata kai Amina inda Za"a Cutar da ita kada ma mamanmu ta Damu Hajiya Zata Dawo da Amina kamar yadda ta tafi da ita.
Mamanmu ta fara Tunanin kodai da wani abu ne..?
Sai kuma ta Tuna ance Dubaran Zaman aure za"a koyamata tuna haka yasa ta watsar da mganar Amina aranta tana ma Hajiya Dariya Tana Wahalar da kanta ne saboda auran Amina da Danmallan ai haka zai kare agantale.
Da sukayi waya da Anty Amarya ma sai da ta mata batun Anty Amarya ta Saki Tsaki Tana Fadin"Nace miki ki daina mana wannan mganar mun gama da wannan shafin..Ba inda Zata kaita Daya wuce maiduguri garinsu tana da inda yafi chan ne..?
Mamanmu tayi Dariya kafin tace"Ai Tunanina bai kawo nan ba..To Allah ya raka Taki gona ya mganar Sakinan..?
Madina ina son kema naga Burinki ya Cika kamar yadda nawa Burin ya Cika .!
Anty Amarya tace"kada ki Damu Saura kadan..Cikin watan nan Danmallan zai zo ya tafi da Sakina kinga in ya tafi da ita shikenan sai naji da Hajiya uwani kuma..!
Mamanmu tace"Ai Hajiya Uwani matsiyaciyace..!
Anty Amarya tace"Babba ma kuwa sai kin ga yadda take shigema Hajiya..Kamar ta Allah..!
Abunda basu sani ba ai Daman in Dubunka Zata cika rasa Dubara kake yi Hajiya gefe ta koma tayi bakam tana karban kowa yadda yazo mata Sannan tana Daina yarda da kowa ta gama Sarewa da lamarin duniya sannan Haj.uwani bata san wani abu ba ita adole tana shigema hajiya tasan wasu sirrukan ai ta Dade da Cin Taliyar karshe tunda Hajiya ta ganota ta DAina bata labarin abunda ya Shafeta da ya"yanta..
Har Falonta tazo tana bin bakin jin ina Amina take taki Fadamata Saboda Sai Daga baya tasan ma Aminar bata bata nan shima abakin Haj Nasara taji Data Tambayi mallam yace hakane ita mamakinta Daya meyasa Hajiya ta Kauda Amina Daga gabanta..?
Ko madinar Aka Turata sai dai tana Tunanin ba Haka bane Tunda taji ana mganar Dawowar Danmallan din Cikin wannan watan..
Sai Hajiya ta bangarar da Tunanin Haj.Uwani da cewa Amina ba Nisa tayi ba Jarabawa take yi a inda take in ta gama Zata Dawo to ganin suma su Hanne sun fara sai ta yarda da mganar Hajiya aranta tace ita wannan auran ai su Amarya da Balaraba sun gama gantallar dashi.
Dayake itama ba Aminar ne agabanta ba Sai ta Watsar da mganar ta Ita yanzu babu abunda ke gabanta sai Shirye shiryen dawowar Nazeem gabadaya Cikin Sati mai Shiga yace mata Zai dawo gabadaya in ya Dawo kuma aikin da zata karisa ai kadan ne har ta Fara hango kanta ta Cika Burinta mganar Anty Amarya kuma bata gabanta tasan ko giyan wake tasha bazata fasa mganar nan har wani yaji ba..Kuma tasan Mama ta sha gaban Bokansu har Mganin Data Karbo ma Sakina sai da mama ta labartamata Dariya kawai tayi in su suna zaune ita ai ta Dade da kwana atsaye kan Cikar Burinta ko kofa bata taba badawa ba ballatana a samu matsala..!
Ashe ashe bata sani ba shi Allah ba"a masa Dubara sannan a lokacin Daka ke Tunanin ka Rufe kofar gefenka ta kofar da bakayi Tunani ba sai Allah ya Wangale taa asirinka ya gama Tonuwa a idon Jama"a.


*******


Kamar yadda Aisha tayi ma Hajiya alkwarin ta kuma ta gayama Amina bata sauya Shawara ba Haka take tasa keyar Amina Kitchen in suna Girki da Saude ta rika gani tana koya mata Saukakkun girke girke,Tun Amina na Tura baki tana kunkunin tana barcinta ya Aisha na takura mata har tazo ta saki ta Fara maida hankali To Saboda ko ta koma Daki Yakaka ke Fatattako ta dole ta Dage tana maida Hankali ballema ya Aisha data koyi Fada tunda tayi aure.
Haka Zata Zaunar da Amina tana koyamata yar shagwaban nan da yadda zata rika ma ya Danmallam mgana da karaiyaya Amina sai ta Dinga Dariya aranta tana Fadin a ina ya Aisha ta san wasu abubuwan agidan kamar in ka samata Hannu abaki bazata Cija ba Kamar ya Aishan tasan abunda take Tunani ta Dunkure mata kai tana fadin"Ban son iskanci ana koya miki yadda zaki zama Tauraruwa wajen ya Danmallan kina Iskanci ko..?
Nasan kina mamakin ina duk nasan wadanan abubuwan ko..?
To ai gidan aure makaranta ne Amina sannan tunda ya siyamin babbar waya nake dan shige shige ina koyan wasu abubuwa sannan Addini ma ai ya koyamana yadda zamu yi mu"amala da kowa har da gidan auranmu..!
Amina ta jinjina kai Domin tana ganin yadda ya Aisha ke yi in ya Usman yana gari kwalliya da salon mgana da kwarkwasa duk tana gani kuma tana Dauka Domin a Zahirin gaskiya itama tana so ta zama mace sannan tunda ga inda kaddara ta kaita ai sai ta Dage Uwa uba kuma taci Uban Sakina ta nuna mata nasu ba irin nata bane Sannan bazatace ta fara son ya Danmallam ba ammh sun fara Shakuwa da juna tunda koyaushe suna Tare a waya kullum Cikin Tambayar baki da wani Damuwa ko.?
Yau da gobe bata bar komai ba sannan ita ai Zuciya tana son mai kyautata mata Amina tana da Budaddiyar zuciya ne shiyasa nan da nan mutum ke Shiga ranta abunda bata sani ba shi ya Danmallam ai jinin jikinta ne shi da take Dauke da Kwansa acikin jikinta,Sannan kuma ba kamar Soyayyarsu da Aminu bane,da ba Sakewa Cikin Tsoro da Fargaba tayi ta wannan kuwa a sake take sannan in suna waya sai tarika jin wannan fa ai mijinta ne wani abu ke shiga ranta batare data sani ba.
Sannan abunda ya Faru Tsakaninsu ya Haifar da wani bond mai karfi wanda Bawa bai isa ya hasaso farkonsa ba ballatana karshensa ba abu Daya ta saani tana jinsa aranta sannan tana Kishi da Sakina daman chan tana jin haushinta balle yanzu da suka Hada miji ko sunanta taji sai ranta ya baci bata ma Damu da balarabiyar nan yadda ta Damu da Sakina ba.
Ko kwana Daya yayi bai kirata ba ta Dinga fushi kenan tana Tura baki in ya Kira taki Dauka Sai Yakaka ta mata Fada da cewa"Tsiya na Dake Sarkaci Takwara..Haka ake karban miji a Hannun kishiya..?
Amina na hura Hanci tace"To bashi bane Jiya fa bai kirani ba..!
Yakaka ta aika mata da Dakuwa tana Fadin"Kin ga naki nan..?
Don bai Kiraki ba sai me..?
Ai kinsan yana da uzuri ko..?
Kada ki Dauka sai ki barma ita balarabiyar ki koma baya ke ko yan Dubaran nan na yaran Zamani da suka iya su Tadama Mazajensu hankalinsu in suna nesa saboda su zo wajensu da wuri baki iya ba,Sai Sakarci da Kunkuni kadai kika iya..!
In yakaka ta fara fadanta bar mata Dakin Amina ke yi abunta ranar kuwa sai taja mai aji Zata Daga kiransa in kuma ta Dauka yana mgana ta basar dashi yasan Laifinsa sai yayi mirmishi yace"Amina kiyi hakuri..!
Sai ya fara fadamata Uzirinsa sannan Zata Hakuri koda yaushe Cikin Tambayanta lafiyanta yake yi tana Bashi amsa ba wata matsala bawani Hira suke ba na ma"aurata ba sai dai suna Hirar abunda ya shafi mganar da Amina ta Fadamai koda yaushe sai tace mai yaushe zai taho Ranar dai yace mata"Cikin karshen watanan..Sannan yana so yazo da Sarood su yi Sati Biyu sai su koma Tare da Sakina..!
Ai Har suka gama wayar Amina bata kara Dariya ba wani Tukikin Takaici take ji wato zai zo da wannan balarabiyar sannan ya koma da Sakina ita ko Oho..?
Sai kuka da Ya Aisha tazo ta ganta Tana kuka Har Hankalinta ya tashi ta Zata ko jikin ta ne take jin wani abu..?
Sai Amina na kukan ba Hawaye tsabar Takaici tace"ba ba..ya Danmallan bane yace wai zai zo da balarabiyar matarsa ba..Sannan in sun tashi tafiya su koma da wannan gajerar matar tasa..!
Galala Aisha ta Saki baki tana kallon mgana kafin ta Tsintsire da Dariya Amina ganin haka yasa ta kara bare Baki ya Aisha ta buge bakin tana Fadin"Kefa ko ya'ya Dubu Zaki haifa na tabbata wannan iskancin naki bazai barki ba..Miye na bare min baki kmar na yankaki Salon yakaka Dake Daki Taji tace nayi miki wani abu..!
Amina ta hura Hanci kafin tace"To bake bace ina gayamiki mgana kina min Dariya ba .!
Ya Aisha ta matso ta kama Hannunta tana Fadin"to na bari kanwata gayamin yaki keso ayi..?
Amina tace"To ni kada ya tafi da Sakinar nan gaskiya..ni fa kadai zai bari anan kuma sai ya Dade kafin ya Dawo. !
Ya Aisha tace"Yanzu waya isa ya hansa tafiya da matarsa Amina..? Ai bamu isa ba matarsace kuma kinga Daman achan take sannan duk keki keda matsala ina nan ina Koya miki irin kissar da zai saka Miji yazo gareka bai sani ba kin ki Dauka nace miki watarana ki sakamai kuka kice cikin ana Miki motsi ke zaki mutu ki Tadamai hankali yayi lallashi ki kinyi Shuru Da gudu zai taho ma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login