Showing 132001 words to 135000 words out of 145917 words
ta Haifamai yan Biyu Duka maza bai karbi Yaran ba sai da ya yi sudujul shukur Yayi ma Allah Godiya sannan ya Dago ya karbesu hannun Aba yaran kamar yayi kaki Sai dai sun Dauko Fuskar Amina kadan da idanuwanta sannan Kuma Indentical ne bamai iya bambamcesu
Kadan ya gansu ya mikama Sarood su da Bakinta yaki Rufuwa Ya shiga Dakin da aka kai Amina ya ganta Hankalinsa ya kwanta ganin tana Numfashi haka ya Rumgumeta yana kwarara mata addu"a tasha albarka kamar me ya Tsausaya mata domin Hajiya ta fadamai da kanta ta Haihu bai Taba zaton Amina zata iya Haifan Daya da kanta bama biyu ba.sai gashi Allah yayi ikonsa..!
Danmallam Aliyu ne mutum na Farko Daya fara Kira ya fadamai karuwar Daya samu Aliyu ya tayasa murna Bakinsa har kunne yana Fara"Barkallahu Fika Ya shehi..Amina kwaila yanzu ta zama giwar mata..!
Umar yace"Kai fa banza ne meye kuma na Tuna baya..?
Aliyu nayi ta mai Dariya shima bakinsa har kunne yace"Hakane fa..To Allah ya raya Allah yayi musu albarka Sai mun zo barka..!
Da haka suka yanke kiran Kowa cikin Farinciki Aliya shi ya koma gida ya Fadama Aliya sai ta kara jin Imani ya Shigeta ta kuma kara yarda Duk abunda yaso Faruwarsa sai ya Faru..!
Sakina take tsausayi domin suna waya tasan Halin Data ke ciki har Cire mata Mahaifan da akayi yau wagari ya waya..?
Duk wanda ya bari Duniya ta Rudesa ya gama yawo haka zai zo ya kare a Duniyan ba riba Lahiran ma haka.
Kafin yammah Labarin Haihuwan Amina ta Zagaye Dangi kaf yan"uwanta ba wanda bai ji wannan Haihuwar ba ya Aisha ce duk ta Kira ta Fada musu Hanne da Hamida sai Tsallen murna suna Tunanin Waya ga Amina da ya'ya har Biyu..?
Ya Aisha har ya Sadiya ta kira ta Shaida mawa ita kuma ta kira Sa"adatu Fatan Allah ya raya sukayi Saboda Duniya ta koya musu hankali Sannan dukkansu sukace bazasu gayama Sakina ba kada Hankalinta ya tashi susan Halin Datake ciki..!
Har Jordan Labarin Haihuwan Amina yakai da Gusai suna ji da gayyar aka Dinga Fada a tsakar gida har Mamanmu daje wani karamim Daki tana jinya taji,Domin tana jin mgana sai dai bata iya mayarwa ne sannan kuma bata gani yanzu idon ya koma sai Lalube.
Taji Haihuwan Amina sai kukan zucci Lalle ta yarda Zakaran da Allah ya Nufa da chara..!
Sakina ma ta ji Domin Aliya ta kirata ta Fada mata Kuka take yi reras dataji Labari shikenan Burinta bazai taba Cika ba har Abada bazata ga k'wanta aduniya ba..Tayi kuka ranar kamar ranta zai fita ita kanta Anty A"i ta kasa lallashinta Domin tana tausayama Sakina gashi har yanzu basu kara ji Daga Bakin Danmallam ba ballatana makomar auran nasu sannan Sakina tace bazata kirasa ba Domin bata san da wani ido xata kallesa ba Anty A"in ne ma ta kirashi da wayar sakinar bai Dauka ba..!
Haka Allah ke tsara lamarinsa Sau Tari wasu Burukan namu mattatu ne har mu koma ga Allah bazasu taba Cika ba..!
Amina haka ta farka ta ga Kyautar da Allah yayi mata tayi kuka ta share Hawayenta ta Rumgume ya"yanta wani son su na kara kamata Ya Danmallam Yahadasu duka ya Rumgume lokaci Daya yana Fadin"Allah ya albarki Rayuwarki Noor Dake da zuru"arki gabadaya..!
Amina na sharan Hawaye a kafadan Mijinta Uban ya"yanta UMAR YUNUS ABDULRAHAMAN BAZANGA murya shake ta Furta"Ameen Ameen Hubby..!
*Janafty**TFZB2030*
*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*
Sai da Amina ta kwana Hudu a asibiti sannan aka sallameta ta dawo gida,saboda tasha wahala sosai har ka ruwa sai da tayi akayi mata Dinki Yakaka ke kwana da ita a asibitin Hajiya sai tayi mata kara Sai dai tazo da Safe ita da Anty Hadiza Da rana kuma Hajiya nasara ke zuwa sai yamma suke tafiya tare da yan Dubiya matan su ya Jafaru har Dangin Yaya sun zo barka goggo Jumai ta koma Hadeja sai ya"yanta ne suka zo sukayi ma Amina barka da sauka.
Suna komawa gida aranar Yakaka ta saka aka nemo mata Murhun karfe da Itace domin tace jego mai kyau zatayi ma Amina bata son gantali wai wanka jego a gas ko a Kittle Hajiya kuma ta bata goyon baya aka hado mata da Tukunya gwarwa babba ta saka ruwan zafi ta saka aka nemo mata ganyayyakin wanka dasu ta Dafa ma Amina ta gasheta tas Amina ta zata zata yi kuka sai kuma batayi ba sai ma Dadin Ruwan dataji saboda jikinta sai Tauna suke kasusuwanta duk sun Sage Lalle ta kara jinjina ma uwa ba abun wasa bane Ta kara ganin Daraja da kimar yaya koda bata araye,Sannan tayi kuka,kukan yadda Rayuwarta tazo a wani yanayin da mahaifiyarta bata taba jin dadinta ba har ta koma ga Allah.
Hajiya ita ta wanke yaran nan tas Hajiya Nasara ta shiryasu Yakaka na ta musu tsiyan sun ga Sabbin mazaje sun Rude ana ta Dariya ita kuma Anty Hadiza tayi girki Sarood da su Anty Fadila nata Faman gyara gyaran gida kowa ka gani Bakinsa har kunne Sarood har Cikinta ya fara fitowa Amina duk yadda taso ta share Sarood da jin haushinta ta sakar mata ganin Tunda ta Haihu a asibiti take wuni yau ma suka dawo gida da ita sai kama ayyuka take tana da Saukin kai da Dadin mu"amala ba ruwanta.
Aliyu da matarsa sun zo duba Amina tun tana asibiti Amina ta ki sakar ma Aliya fuska duk ko yadda take ta wani Shige mata aran Amina tace ai kuma kin makara gwara ki koma inda kikafi auki ta dai karbeta sama sama ammh bata yarda ta saki jikinta da ita ba.
Yan"uwanta kaf ba wanda bai kirata a waya ya gaisheta ba tare da barka da arziki Har Ya Jadwa dake Jordan ita da Goggo Husai sun kirata sannan Hotunan yaran tuni duk yakai ko"ina ya Nasir da ya Jafar suka Dauka a wayoyinsu suna turama mutane mamaki dai ya kare tunda ga Amina da ya"ya har Biyu a lokaci Daya.
Su Hanne kuwa kullum sai sunyi mgana da Amina ji suke kamar su yi tsuntsuwa su gansu suna ta fatan Allah yasa mallam ya barsu su zo suna.
Tunda akayi Haihuwa Danmallam gidansa yake kwana shi da Sarood duk da nan take yini sai dare suke komawa chan gidan tayi ta mai Hiran yaran tana santinsu aransa yana Fatan itama Allah ya Sauketa Lafiya.
Washegarin ranar da suka Dawo Daga asibiti Dadaddare sai ga Mallam yazo shi da Danmallam da Aba aka kawo musu yaran suka kara ganinsu Mallan ya kalli Danmallam yana Fadin"Ka musu Huduba ne..?
Kai ya girgiza kafin yace"A"a mallam..Daman kai nake jira..kayi musu Huduba da sunan YUNUS DA SA"IDU..!
Mallam da Aba bakinsu yaki rufuwa saboda murna Hajiya na wajen Mallam ya kalleta yana Fadin"Hajiya kina ji dai Mazajen naku ma sunan mu sukace..To basu dai fimu ba. !
Dariya aka sanya cike da Farinciki nan take mallam yayi musu huduba da sunan da Babansu yace aka samusu sannan ya diga musu ruwan zamzam da Dabino abaki kafin ya Hadasu duka ya Dafa kawunansu yana musu addu"an kariya..
Hajiya tace"Ina Rokon Allah yasa ku biyo masu sunanyenku..Domin kun Dace da Nagartattun sunaye..!
Aka amsa mata da Ameen basu wani jima ba suka tafi Amina ita kanta Bakinta yaki Rufuwa da wannan karan da Danmallam yayi mata eh mana ai ita yayi ma kara A duk duniya mallam da Aba sune ita Daman abun na ranta sai gashi ya Rigata wani kaunar mijinta da Soyayyarsa na kara shiganta Tunda ta auresa alheransa ke Lullube rayuwarta Allah ya barsu tare.
Su ya Aisha suna so suzo suna suka kira mallan suka mai mgana yace ai ya Danmallam baya taron suna Hajiya ta saka Baki tace na Dangi ne sannan kuma ai na Farko ne, gaba ba lalle su zo ba To sai ya amince kuma Daman yana son ganin yaran saboda akwai Tunasarwa Dayake Bukatar yi musu kan wani abu da suka manta.
Jin Dadi da sukaji Labarin mallam ya bada Izinin su taho ana Gobe suna ya Zulaihat da ya Ikram suka Diro sai Hamida da ya Zulfa Suka kamkame Amina suna Murna sai da Yakaka ta mata mgana akwai Dinki ajikinta Don na ta samu Jego mai kyau k'ashinta ya fara karfi shiyasa ta sami kwarin jiki Sannan Yakaka Jego take mata na Mutanen da sannan suna kauri abinci da Namoni da kifaye kawai takeci kafin me wannan Kibar na Amina kadan Tatafi ta riga tabi jikinta sai tafi kyau ma ahaka yar Duma Duma da ita..hamida ta Dauki yaran sai hawaye tana Tuna irin rayuwarsu ta baya Allah mai kyauta da kari Amina ce ta zama uwa haka..?
Kaunar yaran ya mamayeta ta kamkamesu sai da ya Zulaihat ta mata Tsiyan ba ita kadai bace uwarsu sannan ta amince suka Dauka da yammah sai ga ya Aisha ta Diro ita da ya Abida duk sai sukayi ma gidan mallam Tawaye gidan Amina suke yada Zango.
Sai Hira kawai ke tashi Cikin Farinciki Girkin suna agidan Baba mallam za"ayi su Anty Fadila da su Shamsiya sai matar ya Nazir itama tazo ita da Ya Jalela tare suka zo sune yan gayu zasu yi girki ya Zahra ma ita da Ya Abida sukazo Tunda garinsu Daya,Har ya Nazifa tazo ita da ya Fatima ya Akila ce bata samu zuwa ba sai ya Jadwa.
Hanne kuma sunyi waya sai da Safe zata zo.
Gida ya cika da Dangi an manta komai ana ta Hira da annushuwa Anty Hadiza tayi ma Amina kitso da kunshi Yan gusai da sukazo sai tsiya suke mata suna Fadin da wayau tana gyara yarta Harda Zafira akazo wacce za"ayi Bikinta nan da wata Uku.
Adaran Sai ga Akilu da zubairu sun zo ma Amina barka aranar suka dawo Daga Zaria sun je Rigistration sun samu Admmision,Sai da suka Dauki yaran suka kallesu suka juya suna kallon Amina Dake zaune tana shan Tea Akilu ya kara kallonta kafin yace"Tab..Su Aminene an zama uwa..Sai arage Rashin kunya..
Sai kunga hararan da Amina ta Sakar musu sai kun Dara su kansu sai da sukayi Dariya Fari tayi musu kafin ta Hura Hanci tana fadin"Banson Wulakanci..Kun dai san yanzu ni ba Sa"arku bace ko..?
Ya"yana Biyu..!
Dariya suka saka mata itama sai da ta Dara su kallonta suke yi suna mamakinta wai Amina ce ta Haihuwa lalle Haihuwa ta Allah ce.
Sun Dade kafin su tafi harda kudi suka bama yaran nasu Amina ta karba Tana fadin"Eyye..Kawu Akilu da Kawu Zubairu..!
Yanayin yadda tayi mganar ne yasa sukayi Dariya har Hamida Dake wajen tace"Mai hali dai baya fasawa. !
Akilu yace"Wlh kuwa hamida..!
Daganan suka musu sallama da Fatan Allah ya raya suka fita Daga Dakin sun dan bata Lokaci afalo tare da su ya Aisha kafin su tafi su suka zo da Umaima Hajiya tace su kawota ta zauna cikin Yan"uwanta zatafi sakewa..!
Kusan kwana sukayi basu barci ba sai da Yakaka ta kora Amina taje ta kwanta yaran kuma sun fara kuka iyayansu suka Daukesu duk da Amina ruwan nononta ya kawo Dr Ghali ya Rubuta madaran da aka siya ana kara musu dashi suna da tsotson tsiya in ji Amina don ma Yakaka na mata jan Ido da sai ta horar dasu da yunwa Amina ce fa ai sai Allah kadai ne zai iya mata..!
Washegari da Hidimar suna aka tashi su Mamata gidan Aba suka koma suka kwana da Safe suka shiga gidan mallam suna taimakawa da aiki,an yanka Raguna Hudu kowannen Biyu sannan an yanka kaji da Zabbin na Gidan gonar Baba mallan chan gidan su ya Zulaihat suke ta gyaransu da kuma aikin abinci duk ba su yi Taro ba isu isu ne kawai sai mutanen Gusai.
Da Safen sai ga Aliya matar Aliyu tazo ita da yaranta zuwa karfe goma sai Mutanen yola Hanne da mijinta Aminu har cikin gida ya shigo ya zauna afalo suka gaisa da su ya Abida bayanan Amina ta sakayo Lullubi ta fito suka gaisa Hanne ta Dauko mai yaran ya Dauke su yayi musu addu"an aransa yana ganin mganar Nenne wato Aurensa da Hanne ne Sanadiyar Haduwarsa da Amina ita kuma auranta da Danmallam shine silar Haduwarsu da Amina Allah kenan ya Musu addu"a ya ijiye musu kudi yayi musu sallama kano zai wuce sai in zai koma zai Biyo ya Dauki Hanne su koma gida.
Hanne ta rumgume Amina tana murnan ganinta ta Rumgume yaran ta kalli Amina kafin tace"Amina wai da gaske yaran nan naki ne..?.
Amina ta Harareta kafin tace"Ba nawa bane..na mami Hanne ne da Mami Hamida..!
Tafada tana Dariya ita Hanne gani take kamar wasa ta Yafito Hamida tana Fadin"Hamida kinga ikon Allah ko..?
Amina an shiga kwaryan manya..!
An zama uwa..!
Amina na dariya batace musu komai ba Hamida tace"Sai a rage jidali Tunda an zama uwa ko Aminene..?
Amina tace"To Allah yasa ya ragun kunsan ba yin kaina bane..!
Suka Hada Baki wajen fadin"To yin waye..?
Sai da tayi Fari sannan tace"Na Allah ne..!
Dariya Hanne tayi ta Daka mata Duka abaya Amina ta sosa wajen tana Fadin"Lala sai na fadama Hubby na..!
Dariya suka kwashe mata suna Fadin su Hubby an jiki..!
Tun Safe Amina tayi wanka ita da yaran suka fara shiga suna fita suna fita gadonta kuma cike da kayan suna yan"uwanta sun mata kara ba wacce tazo Hannun Rabbana Aba ma da Turamansa da kayan yara Mallam ma kaya sai wanda ya gani Amina ba abunda zatace ma yan"uwanta da iyayanta sai godiya domin sun mata komai aduniya wajen ganin sun ingata rayuwarta.
Ya Danmallam bai zo gidan ba Ranar suna Saboda mutane sun dai yi waya da Safe da wayar Sarood daman ai nan ta kwana tare dasu ya Abida,wajen azahar sai ga su ya Aisha da kololin abinci kala kala lemuka daman da ruwa tun jiya aka Sauke su nan da nan aka fara Cin abinci Daman tuni kowa yayi wanka ya Shirya kansa Yakaka da Safe gidan Baba mallam ta koma tace bazata iya ba ta bar ma su Abida gidan su shakata..
Abun da ya bama Amina mamaki Sai ga Sa"adatu da ya Sadiya har da ya Jidda sun zo mata suna abun Sai da ya bata mamaki ammh bata nuna ba ta Saki Fuska suma sauran yan"uwa suka karbesu hannu Biyu da suna Dari Dari Daga baya suka shige Cikin yan"uwana ana ta Hiran masu Ciki su ya Abida da su ya Zeenatu har ya Zulaihat duk ciki garesu su ya Ikram kam yama tsufa tana ta fama dashi Chan da yammah sai ga su mariya da Samira yan makarantar Haddarsu Amina baki ta rike tana kallonsu tace"Su Mariya ne da su Samira. !
Suna dariya Mariya tace"Wlh mune su Amina..!
Sai dukkansu sukayi Dariya Hamida ta Fadama mariya Dayake suna Chart ai sukace sai sunzo sun ga Amina da abunda ta haifa aiko sun sha kallo Amina ta zama zara aciikin wata Duk inda tabi ita ake kallo ta zama abun Sha"awa kuma duka taron Saboda itane nan suka Hade dasu Hamida suna ta Hiran baya da irin abubuwan da suka faru Lokacin suna makaranta Har Sa"adatu ta shige Cikinsu
Dayake abun na malamai ne ba Kida ba wani Hayaniya ko Hotuna ta wayoyinsu suka taru yan"uwa suna ta Daukan kansu ya Danmallam kuma yayi walima achan masallacin Baba mallan anyi wa"azi sannan an ci an sha an raka yara da addu"a da Fatan Allah ya rayasu.
Aliyu na Tare dashi a matsayinsa na Amini sai su ya jafar da suka Dawo Daga wajen aiki da yammancin ranar tunda matan suna chan gidan Amina sai suka Sauke gajiyarsu Shashen Mallam nan sukaci abinci suka cigaba da Hira.
Aliya kuwa sai haba haba take da Amina abu kadan tace Amina kaza amina na yankwanata sai da Hanne ta mata mgana Amina ta mata wani kallo kafin tace"Ke ni fa na tsani Cusa kai..Ni ba kawartace ta kama kanta..!
Hanne tace"Kodai yaya ne ki mata uzuru ai don ke tazo.!
Amina ta bangaje Hanne tana Fadin"Naji..!
Hanne ta Bita da kallo Baki Bude akwai Hallayan Amina da Har Abada bazata iya sauyasu ba ance Hali ai Zanen Dutse ne.
Su mamaki ma ta basu da suka ga suna mgana da Sarood Cikin Harshen Labarci wayar Sarood din DanMallam ya Kira yace ta kaima Amina saboda ya yi ta Kiran wayanta bata Dauka ba Shiyasa ta kawo ma Amina ta karba sukayi mganar yace ina ta Jefar da wayarta tace bata sani ba suna cikin kaya mganar komawarsu asibiti yayi bayan yace mata sun yi mgana da Hajiya in sukaje kawai za"ayi ma yaran kaciya ne su Huta Amina tace ba Matsala Duk yadda suka yanke har ya bata Aliyu ya kara mata barka Sannan sukayi sallama ta fita Falo ta Nemo Sarood ta bata wayarta..
Hamida ce sai da tayi mgana ta kalli Amina sanda ta shigo Tana Fadin"Lalle Matar ya Danmallan kece kika kware da Labarci haka sai yarata kuke ke da yar Balarabiyar kishiyarki..!
Amina ta harareta Saboda su Sa"adatu na wajen yasa batayi mgana ba ammh ina ita ina wani Sakin jiki da Sarood ai kishiya sunanta Kishiya duk da tana da Kirki ammh dai kowa yayi ta kansa abunda ya faru agidansu ai Ishara ne ga masu sakarma Kishiya Ragamar gidansa da ya"yansu duk da ba Duka aka taru aka zama Daya ba akwai nagari acikin na banzan ammh Dai na banzan su sukafi yawa.
Sai dare ya Danmallam suka zo da Aliyu da su ya Jafar suka Dauki yaran su ya Aisha na fadin ayi ma yaran alkunya Danmallam yace kul..Da Mallam da Aba za"a dinga kiran su sune alkunyansu Daganan sai suka ja bakinsu sukayi Shuru ranar dai gidan Amina ya Cika da Baki duk nan suka kwana Ya Danmallan kuma da Abokinsa Dakin su Nazeem suka kwana..
Washegari wasu har sun yi shirin komawa irin su ya Zulaihat Sai ga Sakon mallam zai yi mgana dasu Dukkansu anjuma sai tafiya ta fasu kowacce ta Share waje ta zauna aka cigaba Da Hira Saboda an Haadu ba"a son Rabuwa da juna...gidan Amina aka kawo kan ragunan da aka gyara suka Dafa suka ci sannan Naman kuma achan su Mamata suka soya sai da aka musu nasu tunda dagachan aka Rabasa yadda kowa zai shaida harta Aba da Baba mallam an yi musu kullin su na Nama Anty