Showing 120001 words to 123000 words out of 145917 words

Chapter 41 - TAFITA ZAKKA BOOK 2 COMPLETE.txt

04 Nov 2024

83953

karshe Bayan an Daura auran aka shiga taya juna Murna ya jafar yayi mamaki Lokacin Daya ga wanda Hanne ta aura har ya bashi Hannu sukayi musabaha bai daina mamaki ba.
Har sai da shi yace mai""Ya jafar Allah ya Rubuta Amina ba matata bace..Hannatu ce matata..,!
Ya jafar ya jinjina kai aransa yana kara yima Allah kirari.
Su Danmallam suna cikin jama"a suna ta Faman gaisawa da mutane Bakinsa har Kunne shi da Aliyu,da Nazir nan kasan ransa Halin da Amina take Ciki yake so ya sani Sakina kuma bata gabansa bai san Halin Datake Ciki ba Sannan basu kirasa ba shima bai nemi kowa ba.
Suna cikin gaisawa da Mutanan ne ya Hango Amina suna tafe ita da Zafira Amina ta saka Hijabi mai Ruwan Sararin Samaniya kalan leshinta da Takalminta mai Saukakan Tudu tana Tafiya cikinta yana gaba da ita Saboda Girmansa har suka shige gidan mallam
Ayadda Danmallam yaga Fuskarta ta Kumbura ne yasa Hankalinsa ya tashi yaja Hannun Aliyu suka bi bayansu Baya son yaga Amina na cikin Damuwa,suna shiga kuma haraban gidan yan bazanga suka taresa ana ta gaisawa yasa basu samu karisa cikin gidan da wuri ba.
Amina kuma daman Ya Aisha ne tace Hajiya na kiranta, taso ta jira su taho dasu Hanne suna Sauya kaya yasa tace Zafira ta rakota su suna chan ko Mganar auran Aba din ma basu sani ba sai bayan tahowarta sannan Anty Fadila take fadamusu itama Mijinta ne ya kirata ya Fadamata.
Amina har ta shiga Shashen Hajiya ta zama abar kallo da Sha"awa suna shiga Falon cike da jama"a.
Da Hajiya suka ci karo da ta fito Daga Dakinta Taci gayunta itama bakinta Har kunne Amina suna gaisawa da yan Falon yawancin yan"uwan Hajiya ne taga dai ana nuna tw ita bata san me ya faru ba.
Yakaka ce Amina ta Hango zaune itama ta sha gayunta ta karisa suka gaisa Yakaka na fadin"wasu baki ne suka zo suna son ganinki..Hajiya ta saka aka kiraki..!
Hajiya ta kariso wajensu zatayi mgana kenan sai ga wata Farar mata gajera ta fito Daga Dakin Hajiya bayan ta wata mata ce itama suna yanayi sai da tana dan tsawo ita.
Hajiya na ganinsu ta juya tana Fadin"Yauwa Nenne ga ma Aminar nan ta kariso..!
Ta fada tana riko Hannun Amina har gaban matar da Amina ta kasa Dauke Ido a kanta.
Wacce aka kira da Nenne ta Rike Hannun Amina cikin Fara"arta take Fadin"Allahu akbar Rahina..Kinga Aminar Aminullahi..Allah ya rubuta Ba matar sa bace..Rabo ne rabo ne ya Haddasa abubuwan da sukayi ta Faruwa..!
Wacce aka kira da Rahina tabi Amina da kallo Kafin tace"Ba Shakka yau naga Amina..Aminar da kaf Danginmu ba wanda bai santa ba..Sannu Amina Allah ya raba Lafiya..!
Tafada tana kallonta sai Amina ta kasa mgana ta koma tana Binsu da kallo Hajiya tace"Bafa ta gane ku ba inaga sai kun mata bayani..!
Tafada tana Dariya.
Nenne ta kara rike Hannun Amina Tana Fadin"Amina baki gane ni ba ko..?
Ai nasan baki sanni a Fuska ba sai Muryata..Nice fa NENNE..Nennen Aminu fa..!
Sai alokacin Amina ta Gane ina ta san muryan Ido ta waro kafin tace"Nenne..!
Nenne na Dariya tace"Alkwarin Allah ya Cika Amina..Aminu da bai Sameki ba..Sai Allah ya kaddara yar"uwarki Hannatu ce RABONSA..!
sai amina ta kara zaro ido Cikin mamaki bata samun Damar mgana ba Ya Danmallam da ya Aliyu suka shigo Falon bayan su kuma ya Nazir ne yana Cema yan Falon Tawagan Angon Hannatu zasu shigo su gaida su.
Sai Amina ta juya suka Hada ido da ya Danmallam ya sakar mata ido ita bashi ma take kallo ba Wanda ya shigo ne cikin Farar shadda da babbar Riga shi da wasu maza su uku.
Su ya Danmallam suka basu waje su ka kariso tsakiyar Falon suka Duka suna gaida wadanda ke falon.
Kan Aminu na kasa ne Yaji Nenne na Fadin"Aminu yau dai naga AMINA..yau naga Amina..!
Take fada Hakoranta duka suna Waje..Atare Aminu da Danmallam suka Dago kansu.
Shi Danmallam Wanda aka kira da Aminu yake kallo shi kuma Aminu Nenne ya kallo sai kuma karaf suka Hada ido Hudu da Amina..
Mennarsa da rashinta yasa kadan ya Rage bai Haukaace ba itace agabansa ta Sauya har da Tsohon Ciki ma ajikinta..!


















*Janafty**TFZB2028*


*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*




Aminu kallon Amina yake yi da wani mamaki a saman fuskarsa yana mamakin ganin sauyawarta da komai ma acikin shekaru biyu da wani abu daya shafe bai ganta ba abunda yasa ya kasa daina kallonta Katon Cikin Dake jikinta wannan ya kara tabbatar mai da gaske ya rasa Amina rashi na har Abada..!
Shi kuma Danmallan kallon Aminu yake da wani abu acikin ransa kamar almara sai yaji ransa na kuna da wani kishin Aminu acikin ransa in ya tuna abubuwan da suka faru sannan Abaya Amina taso Aminu shiyasa yaji wani Duhu ya mamayesa na ganin Aminu da irin kallon dayake bin Amina Dashi ko shi mallam bai tattauna dashi kan wanda Hannatu zata aura ba abunda a bazata yajisa.
Aliyu dake gefensa shima Aminun yake kallo saboda ai shima yasan Labarinsa sai da Dariya ta kusa kamashi yadda yaga Shehi yake kallon Aminu kamar zai shakeshi yana Faman sakin Huci Sama sama.
Aliyu ya raba ta gefen kunnensa yana Fadin"Cool Down mana Shehi..!
Hararansa yayi kafin yace"Ta ina naga Wani Cool down baka ga yarda yake ta kallemin mata bane..?.
Ko ba auran Hannatu a kansa bai san Noor ta Haramta garesa bane yake binta da kallon Daya wuce ka'ida..?
Aliya na Danne dariyan sa Lokaci Daya yana Fadin"Yi hakuri zai bari..Kallo Daya ne fa na Musulunci..!
Wani Kallo da yayi ma Aliyu sai da ya matsa yana Dariya lokaci Daya yana Fadin"Ana Asif..Shehin Amina..!
Kwafa Umar yayi bai kara mgana ba Amina yake satan kallo ransa yayi fari Daya ga bata kallon barayin Aminu yanzu sai ya karkata yana kallon Aminu sai yaga kansa na kasa suna mgana da wanda ke gefensa ajiyar rai yayi har yana Hararan Aminu ta gefen ido Aliyu na ankare dashi yana Dariya aransa yana Ayyana wani irin so Shehi ke yi ma Amina..?
Bai taba ganinsa ya nuna kishi kan abu ba sai ayau din nan.
Nenne kuma na rike da Hannuwan Amina Fara"arta taki gushewa sai Faman washe baki take yi har gaban su Aminu dake Durkushe shi da Nura da Abokin aikinsa Oscar duk da yanzu ya Daina waka ammh ana tare ba"a rabu ba.
Har gabansu takai Amina tana Fadin"Aminu kaga abunda nake fada maka ko..?
Na sha Fada maka Allah ya Boye wani abu Tsakaninka da Amina saboda irin son da kayi mata..Rabo ne..Wannan Rabon ne ya raba Tsakaninku sannan da kuma Kaddaran auran yar"uwanta Hannatu Allah mai iko Amina..Rahinatu kin ga Ikon Allah ko..?
Rahina ta jinjina kai kafin tace"Nagani Allah ya rabasu lafiya. !
Ta amsa da Ameen Aminu dai kansa na kasa ko Dagowa bai yi ba Amina na haka ta kasa sakewa sannan mamakin yadda al"amura suka juye basu barta ba.
Nenne tace"Ina mijin naki Amina..?
Ance Babban yaron Hajiya kike aure wanda ke zaune a madina ko..?
Kai kawai Amina ta iya Daga mata Cikin Fara"a Nenne tace"Yana ina..?
Ina so na gansa ne mu gaisa..?
Amina ta Dago kanta tana kallon Dannallam da yayi saurin Dauke kansa Dukkansu suka bi wajen da kallo har shi kanshi Amunun Daidai da karisowar Hajiya wajen Dazu ta bar Falon ne sai yanzu ta shigo Nenne na ganinta tace"Hajiya wancan ne Mijin Amina..?
Ta fada tana nuna barayin da su Danmallam suke Hajiya ta murmusa kafin Tace"Eh Shine..Danmallan ka kariso ku gaisa da Mahaifiyar Aminu wanda ya nemi Amina da farko Allah bai yi ba..!
Tafada tana kallon Danmallan din Daya Hade ransa kanar bai taba Dariya ba,Aminu kallo daya yayi mai ya Maida kansa kasa azuciyarsa yana jin wani Nauyi Har yau har gobe bai Daina son Amina ba ya sota da dukkan Zuciyarsa ne sai dai ganin Danmallam a matsayin wanda ta aura sai ya Sare domin ai ta samu babban Goro ne.
Sannan duk da bai taba ganinsa ba yasha jin Labarinsa wajen Amina ashe shine mallan ya aura mata..?
Hakane mganar Nanne Rabo ne..Sannan bawa bai isa ya kankare abunda Allah ya Tsara ba,Sannan matar Mutum ya tabbatar mishi da itace Kabarinsa.
Har su Danmallan suka kariso gaban Nenne bai iya Dago kansa ba yana jin Nura na mai mganar ga Mijin Amina wanda ya kasa sa nan bai ko Kara marmarin kallonsa ba.
Ita kuwa kallon Danmallam take Cikin Fara"arta kafin tace"Masha Allah..Sannun kaji Allah yayi albarka..Ashe Amina kuma rabonka ce..?
Aminu ya so Amina son da bai taba yima wata Diya mace ba..kaganshi nan Saboda rashin Amina Dakyar muka samo Aminu da Addu"o"i da Nasihu yakusa shekara yana jinyar Zuciyarsa Dakyar da sidin goshi muka samu ya Farfardo nasha Fadamai yayi Hakuri yayi takwalli Akwai tanadin da Allah yayi masa agaba haka kuwa akayi kwatsam sai ga Mallam ya Dira a yola wajen Alhaji Babba da mganar Ya bama Aminu auran Hannatu yarsa..Shima bai yi gaddama ba, ya amsa domin na Fadamai daman itace maatarsa Amina kawai Sanadi zata zame sa..Gashi kuma komai ya Faru yadda Allah ya Tsara..muna namu ne Allah na nashi..Allah ya baku zaman Lafiya dukkan ku..Ita kuma Amina Allah ya sauketa Lafiya yasa abokiyar arzikinkace..!
Gabadaya suka amsa mata da Ameen har da Aminu da su Nura sai ya Danmallan yaji Nenne ta Burgesa kansa na kasa ya amsa mata lokaci Daya yana fadin"Mungode Mama...Allah ya kara girma..!
Ta amsa da Ameen ita da Rahina Amina dai kanta na kasa tana Satar kallon Aminu sai taji ya bata Tsausayi Ashe har jinya yayi tayi bayan rabuwarsu..?
Ai ita kanta Shaida ne Aminu ya sota sai dai bata Taba Zaton abun har yakai haka ba nan da nan sai Idanuwanta suka kawo kwallah.
Jin yadda Nenne ke Fadama Hajiya wuyar da suka sha kafin Aminu ya manta da komai anan ne taji har ya bar Kano da waka gabadaya ya koma Yola yana cigaba da kasuwancinsa shekara daya da wani abu kenan an samu ya Dawo Cikin Hayyacinsa..!
Hajiya ta jinjina kai ita kanta Lamarin ya Dauremata kai da Farko da Mallam ya Sameta da mganar zai nemi iyayen Aminu kan mganar Hannatu shi fa har yanzu sai yake ganin kamar bai kyauta ma yaron nan ba sannan da gaske yake yi tun a wanchan Lokacin da yace zai bashi Hanne.
Hajiya bata iya yin gaddama da Shawaran mallam ba Sai dai tayi Fatan Inda Alheri Allah ya Tabbatar in babu kuma Allah ya watsar da al"amarin sannan Tunda taga mallam ya Dage sai ta bishi da Fatan Alheri tasan yana da Dalili Tunda bai taba Tallata ya"yansa ba wannan din ma Domin da Dalili ne.
Daman yana da Lambar Alhaji Babba tun wanchan zuwan da sukayi ya karbi Lambarsa basu taba mgana ba sai da Mallam din ya yanke shawaran zuwa chan yola suyi mgana sannan ya Kirasa suka Tattauna a kuma Satin Mallam yaje Yola shi da idi suka gana da Alhaji Babba ya kuma karbi mganar hannun bibbiyu sannan ya labartamai yadda suka sha Fama da Aminu mallam yaji Tsausayinsa sosai alokacin aka kira Aminu yazo jin Bukatar yasa bai yi gaddama ba. Ya Dauki hakan a matsayin nasa kaddaran kenan Mallam ya ga karamcin rikesa sukayi sai washegari suka juyo shi da Idi..
Sannan sun biyosa Daga baya akayi neman aure aka biya Sadaki da Lokaci bayan nan ne Aminu yazo suka gana da Hannatu kowannensu yayi mamakin ganin Dan"uwansa barin ma Hanne da tayi ta kuka tana tunanin me zata ce Amina..?
Shi kuma Aminu Kwatan kwacin Soyayyar da Amina keyi ma su Hannatu da wanda ke tsakaninsu yasa ya amince da auran Hanne Dari Bisa Dari.
Nenne bakinta har kunne take ta Godiya tana Fadin"Munga karamci Munga Kauna da kara..Allah yayi ma wannan zuru"ar albarka..!
Hajiya na amsa da Ameen aranta taji Dadi tasan Hanne bata fada hannun banza ba Nenne da zuru"arta masu karamci ne
Amina na chan tayi nisa cikin Tunani ashe har su ya Danmallam da su Aminun sun yi ma su Hajiya sallama sun Fice Daga Falon tana chan cikin Tunani bata ma sani ba sai da suka Fice ta waiga taga basu afalon sannan ta iya Sauke Nunfashi mai karfi Sulalewa tayi daga wajen Nenne ta koma kusa da Yakaka ta zauna suna Hira sama sama rabin Hankalinta na kan Dangin Hajiya yan maiduguri Dake ta shiga suna fita sannan suna kuma Rangada guda sai da Hajiya ta Tsawar tar musu sannan suka Daina ita Amina bata kawo komai aranta ba ta Dauka dai suna yi ne saboda Bikin su Hannatu.
Su Hanne take jira taji Dalilinsu na Boye mata Aminu ta aura Shuru Shuru basu kariso ba wayarta ta Dauka ta Dokama ya Aisha kira ta Dauka kafin Amina ta fara Mita tace mata suna kofar gida gasu nan shigowa..
Minti Biyar Tsakani sai gasu sun shigo Duka da Amaran har Sa"adatu da zugan su ya Jadwa Allah Sarki su ya Zulaihat suna baya baya duk sun yi wani zuru har su ya Jidda ma sun dan fi su Sakin jiki sai suka bama Amina Tsausayi sai da ta Share kwallah Bedroom din Hajiya aka shiga Dasu Amina bata bisu ba,ganin mutane nata shiga sannan su Nenne ma sun Shiga suga Amaryansu sannan taji Dadin zamanta bata so kuma tatashi.
Sai da ya Abida tazo ta mata mgana Sannan ta iya jijjibiwa ta mike tana mata Dariyan Amina ta zama uwar mata Baki ta tura batayi mgana ba..
Daga Dakin Hajiya Dakin su Hanne aka Maido su daganan sai Falon mallam Abun ya Sauya wannan karon Duba da abunda ya faru jiya.
Amina na shiga ta iske Hanne da Hamida sun hada kai suna kuka Sa"adatu kuma na gefe ita da ya Sadiya suma duk sunyi Laushi..
Cogewa tayi kofar Dakin da katon Cikinta tana Fadin"Meye kuma haka..!
Kun wani Hade kai kuna kukan munafunci..?
Sai alokacin suka Dago Hanne na kuka ta mike ta rumgume Amina,Amina sai ta riketa bata so tayi kuka tana Fadin"Ni sake ni ai fushi nake dake..!
Hanne ta Dago Cikin kuka tana Fadin"Me nayi..?
Amina tace"Yanzu Ashe Aminu ne kika aura shine jiya cikin ke da Hamida ba wanda ya Fadamin..?
Ai kun kyauta..!
Tafada tana kara shan kunu Hanne ta kara sakin kuka kafin ta juyama Amina Baya tana Fadin"Na kasa Fada miki ne Saboda bansan da wani ido zan kalle ki ba Amina..!
Amina ta juyo da ita tana Fadin"Ki jimin gulma irin na Hanne Hamida..Da wani ido kika Saba kallona don kaniyarki..?
Ta fada tana Maida abun wasa Hamida na sharan kwallah Tataso tana Fadin"Tunda yazo ta ganshi Hanne ke Cikin Damuwa..!
Amina ta kallesu shekeke kafin tace"To Saboda mene..?
Hamida ta kalli Hanne kafin tace"Saboda Tana jin kunyarki..Zata auri Saurayinki..!
Amina tayi wata Dariya kafin tace"Ammah wlh Hanne kin bani mamaki yau ko ban yi aure ba ni mai bar miki abunda nake so ne..?
Ai kin wuce haka a wurina na Daukeki kamar uwa Daya uba Daya ko Mijina ne ya nuna yana sonki ni mai basa goyon bayan ya aureki ne ballatana Wani Saurayi chan da muka yi soyayyah ina cikin yarinta..Wlh Hanne ki saki jikin ki ki daina Damuwa Dani Dubeni ni ban nemi komai na rasa ba ya Danmallan ne Duniyata yanzu komai baya gabana .!
Suka Saki baki suna kallonta Amina ta Shafa Cikinta tana Fadin"Baku ga alama ba ma..!
Ta karishe fada tana kashe musu ido Sai gashi sun kwashe da Dariya har da Tafawa ya Sadiya da Sa"adatu sai suka Tsargu tunda basa jin me suke fadi sai suka ga kamar sunayi dasu ne.
Hanne tace"Amina dai bazaki taba Sauyawa ba. !
Amina tace"Dillah nayi hankali fa..Nan da wani Lokaci ni Uwa ce..Kun ga kuwa Dole na rage wasu abubuwan..!
Suka Hada Baki wajen fadin"Ba shakka Mami Amina..!
Dariya suka saka gabadayansu Kafin Amina ta rumgomsu dukkansu tana Fadin"ku daina kuka..Insha Allahu Alheri zaku tarar a gidajenku..Hanne ina miki albishir da kin Dace Aminu mai Kirki ne zai kula Dake..Sannan kin samu Suruka mai kirki irin Nenne..Kema Hamida duk da bansani ba..Nasan kema kin Dace saboda Baba mallam bai taba ma ya"yansa Zabin da bai kamata ba..!
Gabadaya sun yarda da mganarta sai gashi Amina ita ke faman lallashinsu Sa"adatu da ya Sadiya basu mata mgana ba itama tayi kamar bata gansu ba Gabadaya Haushi suke bata sannan Daman basa wani shiru da Sa"adatun sai kallonta suke yi ita ko har da gayya take turo Cikinta Tana Tafiya irin ma masu Ciki aranta tace Dan Bakinciki sai dai ya mutu..
Su ya Abida ne duk suka shigo Dakin da su ya Jadwa da sauransu Su ya Zulfa sai da ya Aisha ta jawo su suka shigo nan suka hada kai da Hamida suna ta kuka an basu hakuru sun ki Dainawa Amina na gefe ita bata ma kuka ganitake yi a kyalesu su koka Domin Abun kukan ne yazo.
Suna cikin Hakane ya Aisha ta Fallasa Labarin Auran Aba da Hadiza Amina mamaki ya kamata baki Bude wato shiyasa Dazu ake ta nuna ta tasan Anty Hadiza kuwa Diyar Goggo Yagana ne lokacin auran su ya Aisha ita tayi musu ma gyaran jiki sannan Da ita akazo wannan Bikin Dazu ta ganta tana Sanye da Hijabi sai Faman Dukar dakai take yi Ashe shine Dalili


Kawai sai taji Hawaye ya kawo mata Alherin Mallam bazai fadu ba sai dai sumai Fatan ya gama da Duniya Lafiya.
Nan fa su Ya Jadwa suka Rangada guda ya Jawahir cikin Hawaye tace"Yaya tatafi..Ga Wata YAYAr ta dawo..!
Kai Allah ya saka ma Baba Mallam da Alheri gwara Balaraba ta san ba mai yi sai Allah sannan da ranta zata ga Aba da wata mace sai dai Bakinciki ya kasheta muguwar mata..!.
Sai kuka ya Jamila ne ma ke nuna mata su ya Zulfa da sukayi wiki wiki ga bakinciki ga kunya ammh bakinta ita da ya Jadwa bai yi shuru ba sai Dakin ya koma na koke koke Su Hamida nayi su ya Jadwa nayi sai da Hajiya Nasara ta shigo ta tsawa tar sannan kowa yayi Shuru.
Daganan Shashen mallam aka kai su Hanne yayi musu nasiha shi da Aba da Sauran yayyi irin su Ya Danmallam Amina dai ta gaji da Zirga Zirga tana Bangaran Hajiya sai alokacin Taga Sarood duk yadda taso ta karbi Fara"an Datake mata kasawa tayi Domin wani Kishi ne ya taso mata afakaice Hararanta tayi ta Dauke kanta ita kuwa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login