Showing 78001 words to 81000 words out of 145917 words

Chapter 27 - TAFITA ZAKKA BOOK 2 COMPLETE.txt

04 Nov 2024

83955

Lokacin Tafiyarsa bai yi ba ammh sai ki kalleni kina Dariya..,!
Amina tace"To ai kunya nake ji..Kuma kuma..!
Ya Aisha tace"Kuma me..?
Amina tace"to ai naga shi babba ne. !
Dariya ya Aisha tayi kafin tace"to ai ke kin ji Dadi ma baki san sirrin auran irin su ya Danmallan ba..?
Gaki da kuruciyarki Amina da Shagwaba da Yarintarki zaki sacemai Zuciya shi kuma ya lalace akanki Wlh irin ku an fi sonku kiyi ta Jidalinki yana lallabaki shiyasa na Fada miki shima wannan Jidalin naki aikwai Inda ZAI miki amfani balle nasan shima ya Danmallam din ai yana son soyayya..!
Amina tayi Dariya "To kuwa matarsa bata iya ba..bandai sani ba ko wannan Sarood din..!
Ya Aisha tace"Ke ya akayi kikasan bata iya ba..?
Amina tace'Tab ai na Zauna da su..!
Aisha tace"ai bata iya komai ba sai Fadin rai ita kuma wannan Sarood din naga kamar ta Biye mata sun maida ta wata wawiya ma..!
Amina tace"ai kamar ma wawiyar ce..!
Dunkure mata kai ya Aisha tayi tana Dariya tana Fadin"Tunda ke kin iya sai ki Dage ki rikitamana yayanmu.!
Amina taji kunya ta kasa mgana.
Tundaga ranar ta Bude kunne tana kwasan Abubuwa awajen ya Aisha Da gaske take yi duk sai ta nuna ma su Sakina basu iya komai ba Aminene ai Ta musu Zarra.
Bangaran karatu kam sai da ya Aisha tasha mamakin Amina ba inda baza"a bude mata a Qur"ani ta karanta ba Hadisi kuwa tunda ga na farko har na bakwai suna kanta sannan ta haddace Arba"una Hadith sira ma haka Tajwid wasu Littafan Ya Aisha mamakin Amina ya isheta sai da ta Furta mata tace"Yanzu daman Amina kin iya wannan duk abubuwan kike iskanci a makarantar islamiya da Haddda..?
Amina Dariya kawai tayi tana Fadin"ai ya Aisha ba kowani Hali muke sani na mutanen da muke Tare dasu ba..Muna sanin wanda suka bayyana mana ne..!
Ya Aisha ta jinjina kai tace ba Shakka ko bangaran Boko sai da ta Kusa raina kanta sun yi kunsan mintinaa Talatin suna hira da Usman Cikin Harshen Turanci Amina bata kage ba sannan ba Turancin yan koyo ba Turancin ya Zauna abakinta sosai har Usman sai da yayi mamaki yace mata"Amina fa tana da kwakwalwa..In ta samu cigaba da makaranta sosai zata Zama wani abu watarana. !
Ya Aisha ta jinjina kai tana Fadin"Agida ko sai kace bata gane komai..Bama Damuwa tayi da karatun bafa..!
Dariya yayi yace"ai irin su sun fi raina ma mutane hankali da basa ganewa nan kuwa sun fi kowa Dauke komai Lokaci Daya..Muma lokacin muna Secodary sch muna da wani Dan ajin mu haka mai suna yahaya kamar wawa fa ana karatu yana wasa wlh a Exam shine Overoll..!
Ya Aisha tace"irin Aminace..A aji Dakikiya a Result sai kaga ta Doke kowa ko su hanne Dake maida hankali Tana gabansu..!
Usman yace"Da yawam irin masu baiwar nan basa samun masu Courage dinsu ne in ana kushe su ana cewa basa yi sai su boye baiwarsu sun fi bayyanasa wajen wanda ya yarda suna da ita kanta baiwar..!
Ya Aisha ta jinjina kai domin tagamsu da hakan yanzu sannan baba mallam koda yaushe Cikin Fada yake Uwata yar baiwace nan gaba sai mun baku mamaki aiko gashi ta bata yau wlh Bata Taba jin Amina tayi Turanci ba Duk azatonta batajin komai sai Tsinta tsinta.
Daman haka Lamarin Allah yake Tsammanin Abunda baka Tsammani ba..!


*******


Bayan kwana Shida..!


Nazeem ya Diro gumel Ranar wata Laraba da yammah tun Safe Haj.Uwani ta kasa zama ayi chan ayi nan tasa su Baba lami sun shiryamai kayattacen abincin daya fi so Priderice da soyayyan kaza an yi pepe dinta da kunin aya,Tasa su Akilu sun Share masa Dakinsa an gyara an goge an Baza Turaran wuta Duk ta kasa Zaune sai da ya Shigo gidan Abunda yafara bata mata rai duk yadda Taci Burin Dawowarsa sai da ya Fara Shiga Shashen Hajiya suka gaisa ya Dade ma suna Hira sannan ya kariso wajenta ammh Dayake yar Duniya ce sai bata nuna mai ba ta karbesa Cikin maraba da lalenta kamar ko yaushe.
Ya Duka yana gaisheta ta amsa Cikin Sakewa tana Fadin"An gama karatu gabadaya Nazeem an dawo gida..?
Daman ance kowa ya bar gida..Gida ya barsa..!
Yana Dariya kansa a kasa yace"Hakane Mommy..Mun dawo sai Fatan mu samu aiki atayamu da addu"a..!
Tana Dariya cin nasara tace"ai kama samu aiki ka gama Nazeem..kai fai tashi ka karisa Dakinka kayi wanka ga abincinka nan tafe. !
Ya mike yana mata godiya har ya fara Tafiya tana Binsa da kallon alfahari ganin ya kara girma sam bai yi kama da ita ba yafi kama da Mallam ne kuma suna bala"in kama da Danmallan.
Juyowa yayi yana Fadin"Mommy ina Umai..?
Ya jikinta..?haj.uwani tace"Taji Sauki har ta koma ma islamiya da Hadda.
Kai ya jinjina ya fice yana fadin Allah ya bata lafiya..
Yana fita itama ta fita Kitchen din Tsakar gida tace su kaimai abincinsa da komai da komai tana Tsaye sai da Taga an Dauka an kai ta koma Shashenta ta Kira Batula ta Fadamata Dawowar Nazeem.
Batula tace"Dakyau..To gobe zan yi Sammakon zuwa Minna in samu mama na mata bayani yadda ake Ciki Zaki ji..!
Haj Uwani tace"Nagode batula..Kada kiyi sanya..Kinsan wani Lokacin jinkiri ma yana batamana aiki. !
Da sauri Batula tace"Haba a baya ma ban yi sanya ba..Ballatana da yanzu da muke gabda Cikar Burinmu..?
Kedai sai kin jini..
Daga haka suka sauke wayar Haj.Uwani Bakinta har kunne sauran matan ma su Anty Amarya sai Da Daddare suka san Nazeem ya Dawo da suka gansa Falon Mallan har suka gaisa
Mallam yaji Dadin Dawowarsa Saboda Nazeem akwai natsuwa ga Hnkali yana ta mai fatan alheri da fatan samun aiki mai kyau.
Ranar Hajiya Uwani bata Samu kebewa da Danta ba washegari ma Tare da yan"uwansa Nasir da Jafar suka shigo mata ranta ya sosu sai bata nuna ba ta barsa sai da ya kwana Biyu da ya shigo gaisheta da Safe tana Dakinta taji suna gaisawa da Umaima da Jikin nata yayi sauki yanzu har tana Fitowa falo ta Zauna.
Daman jiransa take yi yana shigowa bayan sun gaisa ta sako mai mganar Dake ranta Cikin Dakiyarta tace"Tunda ka Dawo gida..sai ka fara bin Baban ku sa"idu gidan gona kana Duba wasu abubuwan tunda kaima Harkan kasuwancin nan ka karanta..Wani abun gwara ku masu Dukiyar kuna kusa zaku fi ku kula dasahi Dakyau akan bare..!


Ya Dade yana mamakin kalamanta kafin yace"Mommy ai baba Sa"idu kuwa ba bare bane kema kinsani..Kada ma ki Fada baba yajiki bazaki ji Dadi ba sannan shekaru aruru yana kula da kasuwancin Baba ko Da rana Daya bamu taba jin kansu ba..Sannan infact ma ni bana Sha"awar aiki a karkashin Mahaifina gwara na samu aiki na tara gumina..Na ma yi interview da wani kamfanin Sarrafa fata dake Lagos sun ce xasu neme ni Albashi 100k sukace zasu rika Biyana Duk wata..!
Kafin ya gama mgana ya sha Harara nan ta Rufesa da Fada tana Fadin"Inda Uzairu ya fika kenan shi Burinsa ya gama karatu yazo ya taimaka ma mahaifinku kai kuma Shashaha kana wani mganar kamfani Dubu Darin banza..?
Kasan iya adadin Dukiyar mallam ne..?
To ahir dinka..ba inda zaka yi aiki sai karkashin mallam kuna chan sake da Baki wasu dagachan nesa suna amfana da abunda yake watarana mallakin ku ne.
Gargadi na shine in mallam yamaka mgana ka amsa mai wlh ka kunyatani sai na sabamaka..!
Har ya fice yana mamakin me yasamu mommy ne take irin wannan mganganu ?
Washegari Batula ta kirata tace Mama tace yau da Daddare ta tunkari mallam da mganar bazai mata gaddama ba.
Cikin jin Dadi da Nasarar ta Ta tunkari mallam adaran Daman ita keda Turaka yana cin abinci ta lamkwashe kafa agabansa tana Fadin"Mallan nace tunda Nazeem ya gama karatun nan ya Dawo gida kafin aiki ya samu kasan kasar tamu yadda takkoma sai Kana da wani asama..Sai naga Tunda shima bangaran Kasuwanci ya karanta mai zai hana ya fara Bin Sa"idu gidan gona yana ganin waau abubuwan yana taimakai ko wajen Rubuce rubuce ne tunda naga Jafar ke taimakamai shima kuma kaga ga aikinsa..!
Har ta Sare da ba nasara taji mallam yace"Hakane..Zan m Sa"aidun mgana sai ya fara Binsa yana da kyau hakan Zai taimakamai..!
Haj.Uwani taji kamar ta goya Mallam Dole ta karama Mama kudi haka ta shiga yi ma mallam godiya sai da ya ji mamakinta.
Abunda bata sani ba wani abun yana Tarda Sa"a ne mallam yayi la"akari da nazeem ya Dawo gida Zaman banza zai yi kafin ya samu aiki daman kuma yana da wannan Tunanin shiyasa bai mata gaddama ba.
Da Safe da Aba yazo su gaisa ya Sanar dashi yaji Dadi Sosai,suna ma Cikin Tattaunar ne sai ga Nazeem ya shigo gaida mallam nan ya sanar dashi bai iya cewa komai bs tunda Haj.Uwani tace in yayi gaddama sai ta sabamai.
Shi dai zai bi umarninta dana mallam ne ammh yana samun aiki bazai Zauna ba.
Aranar suka fara tafiya gidan gona shi kanshi a wuni Daya kawai da yayi aikin Lissafi kadai ya yi sai da ya Jinjina Dukiyar baba mallam Aba na Fadamai a duk sati ana Fita da kwai Fin na miliyan Daya sai da ya Rike baki ya dai san gidan gonar babbane ammuh bai Taba maidakai akai ba.
Da Daddare suka Dawo Haj.Uwani daya Shigo Falonta Tana jansa da Hira anan nema ya gayamata tana jin Uban kudi ta zare ido tana Fadin"kaji ko..?
To ban da na gonakinsa kila in kaji abunda yake samu a shekara sai kanka ya Kasa Dauka..!
Sai jin Dadi take yi tana Mirmishi shi dai wannan baya gabansa dukiyar Mallam bazata Burgesa ba Tunda ba nasa bace.
Kwana Hudu da Fara zuwan Nazeem gidan gona da Sakar masa ragamar Wasu abubuwan da Aba yayi Mamammu taji labari shima suna Tare ne taji yana waya da Nazeem da ya gama ta tambayeshi yake fadamata Tare suke kasuwancim mallam yanzu yana taimakamai sosai da Umarnin mallam din.
Mamanmu jiki na rawa ta koma Daki ta kwalama Anty Amarya Kira ta Sanar da ita abunda Aba ya Fadamata.
Anty Amarya ta lailayo ashar ta maka kafin tace"Ammh Uwani dai an yi bakar Tsinanniya..Allah dai ya Tsine mata albarka..
Mamanmu ta amsa da Ameen madina da gaske take yi fa..!
Anty Amarya tace"Ai na rigata..Nasha gabanta wlh..!














*Janafty**TFZB2019*


*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*




Mamanmu tace"To yanzu menene mafita..?
So nake ki nuna ma Hajiya Uwani ita din banza da wofi..bata isa ba kuma bata kai ba wlh..
Anty Amarya tayi kwafa kafin tace"Ki kyaleni da ita Dayyaba..Ni yanzu abu Daya ke gabana Umar yazo ya tafi da Sakina Madina,kuma Hakan na gabda Faruwa saboda Cikin sati nan mai shiga yana tafe sakinar ma ke fadamin jirgin yawo zai fara yo gaba da kayansu..Kinga suna komawa shikenan hankalina ya kwanta Sai na Fuskanceta na nuna mata bata isa ba Daga ita har Sa"idun sai sun Dawo karkashin cewata ai Fara Bin sa gidan gona ba shi ne Mallam ya sakar mai komai ba Tukunnah dai Dayyaba akwai sauran rina akaba..!


Mamanmu gabadaya yanayinta ya Sauya jin kalaman madina har suka gama wayar sama sama take amsata tana faman mata gatsine,Har dai ita mamanmu tagaji ta katse kiran lokaci daya tana bin wayar da Harara tana fadin"Haka kurum na kiraki da kudina da wayata ki Zauna kina neman gayamin mgana ina Dalili..!
Dukiyar ai bataki bace Ko shi mallam din Daya tara bai Damu da ita ba sai ku kuna ta neman halaka kanku Saboda ita har kina Fadin har sa"idun sai ya Dawo karkashin cewarki..?
Haka kurum ba kara sai ki maidamin Miji kamar kwallo ki dinga garasa yadda kika ga Dama to wlh madina Baki isa ba kan Sa"idu zan iya yin komai Ciki har da Raba Hanya Dake sai kowa yayi ta kansa kan mene ina Dalili wannan Bakinciki ina jin Dadi na Samu yadda nake so aikuwa Allah ne ya Hada mallam da Sa"idu ban ga mai rabasu ba haka kurum Madina ke wata mganar banza..!
Surutun ma tana yi ne bata san tanayi ba Aba ne ya fito zai shiga bayi yaji tashin mganarta har ya shiga ya fita tana mganganunta shiyasa ya Leka Dakin nata yana Fadin"Balaraba ke da waye kike ta fada haka..?
Tun dazu nake jin tashin mganarki nama Zata ko da hamida kike ne sai na Leka Dakinsu naga sun kwanta ita da Jawaad.
Sai alokacin mamanmu ta Dawo Cikin Hayyacinta ta fara inda inda tana Fadin"Ni da masu yarenan ne yan iskan sai su kira ka suna maka gwaranci ko kai basa kiranka..?.
Ya saki labulen yana Fadin"To da kin ji sune ai sai ki kashe wayar ki ni ai bani da Lokacin Sauraran irin su. !
Da haka ya koma Dakinsa Mamanmu ta Sauke ajiyar zuciya ta biyosa tana Fadin"Shikenan kuwa haka zan dinga yi musu sai mu rabu lafiya. !
Aranta sai taji salama da Aba bai Tsinkayi wasu daga cikin magnganunta ba.
Ai data shiga goma ba uku ba.


Acikin Satin kamar yadda Danmallam ya Tsara jirgi ya fara yo gaba da kayansu saboda yayi ma iyayansa da matansa siyayya musamman ma Amina Komai ya gani sai yace zai ma masu Ciki kyau harda kayan jarirai masu kyau duk ya siya ammh bai bari Sarood ta gani ba sannan yazo da Ruwan Zam zam mai yawa saboda mallam yamai mgana yana so da Dabinio sai sauran abunda ba"a rasa ba kuma bai sanar da kowa shi da Sarood zai taho ba sai dai agansu kawai.
Kwana Biyu Tsakani kayan suka iso Jafar da Nasir suka je Filin jirgin Kano suka karbo kayan Direct Gidan mallan akayo da kayan Dakin Hajiya Daman kowa yasan in irin wannan ya faru kayan da komai Shashen Hajiya ake ijiyesu kafin ya Danmallam din ya sauka.
Sakina ana chan ana shiri miji zai Dawo tayi gyaran kai tayi kunshi Sannan tayi gyaran jiki da na chan Shawaran Aliya ne ita ta Hadata da mai kayan matan ta siya awajenta.
Miji kawai take jira ta riga ta gama Shiryawanta.


Ko Amina in sukayi mgana in ta tambayeshi yaushe zai dawo sai yace ya kusa bai saka mata rana ba,yaki gayamata ranar da zai dawo so yake ya bata mamaki sai dai ta ga ya Kirata da Layinsa na Nageria.
Haka kuwa akayi Ranar laraba suka sauka da karfe sha biyun Dare,kwana Biyar da sau kan kayansu suka iso a kano jirgi ya saukesu saboda Dare ne yasa bai kira kowa ba suka samu Tashar Mota shi da Sarood sai jakar kayansu suka nufo gumel sai wajen Biyu da wani abu na Dare suka iso gidansa ya wuce kai Tsaye sai dai Sakina taga Bakin Dare sai murnanta ta koma Ciki ganin Sarood sai da ta nuna afuskantar duk yadda taso ta boye hakan Sarood ko Cikin Murna taje ta Rumgume Sakina Tana Murnan ganinta....
Sakina tayi yake kawai tana Tunanin yadda Umar ya maidata banza ai bai gayamata kafarsa kafar matarsa ba Tana jin dadi ta gagari Amina Zama agumel shine zai jajibomata wannan Sakaryan.
Dakin da aka bama Amina ta Zauna Sarood ta shiga sai dai yanayin Dakin da sauran kayan Amina Data gani yasa tasan an zauna adakin Saboda Gajiyan Hanya da kuma Dare yasa sai da Safe ta ma Sakina Zencen tunda suna Dawowa Umar Dakinsa ya nufa yayi wanka ya kwanta Sai barci sai da Safen suna kari Sarood ke tambayan sakina kayan waye tagani adakin ta..?
Sakina Cikin kissa ta ke sanar da ita kayan Amaryan sa ne Amina nan ta Zauna Sarood ta kallesa sai dai batace komai ba ammh ranta ya baci meyasa Sai Dakinta baga Dakinsa ba..?
Sannan wato ita aka raina meyasa bai ce ta Zauna Dakin Sakina ba..?
Kwafa tayi har suka gama karyawa batace komai ba Sakina sai jin Dadi take yi ranta Fes domin da asuba sai da ta ribaci Umar yayi wani abu da ita kuma taga Chanji Sosai yadda ya rikice mata sannan karin jin Dadinta yadda ta zuga Sarood Cikin Ruwan Sanyi batare data gane ba Tunda ita Sakaryace shi kuma Danmallan kunu yasha baisan wata mgana yasan Nufin Sakina tunda ba yau ta saba raina ma Sarood din hankali ba.
Ganin yadda ya Hade rai ne yasa Sarood din bata yi mganar ba Sai dai Daga yanayin ta sha ka matuka da Kishi Sosai.
Suna gama karyawan suka shirya suka suka nufo Gidan Mallam Jafar ya Kira yazo da mota ya Daukesu daman Tun shekaranjiya an san sun iso
Gida ya Rude da Murnan dawowarsa Gabadayansu har da Matan nasa duka Shashen Hajiya suka fara Sauka Har Sakinar domin ba hanyar da zata fara wucewa Shashen Anty Amarya ganin yadda ya Tsare gida..
Gabadaya matan mallam har da Anty Amarya nan shashen Hajiyar sukazo musu maraba su Hajiya Uwani kada aji labari sai barin jiki take yi Danmallan kallon Anty Amarya kawai yake yi yana Tuna labarin da Amina ta sanar dashi bai san Dalili ba sai yaji bai yarda da ita ba Tun balle ma ganin yadda take ta Kiftama Sakina Ido tana so su kebe suyi mgana ganin wannan balarabiyar da bata san da Zencen zuwa da ita ba, yana ganin su yayi kamar bai gani ba.
Nan ya barsu ya tafi falon mallam shi da Nazeem suka hadu da Aba suka gaisa basu Dade ba suka tafi gidan gona ya Dade shashen mallam suna kara Tataunawa .
Fitarsa ne ya bama Sakina Daman sulalewa ta koma Shashen Anty Amarya suka kebe Anty Amarya Cikin Bacin rai tace"Sai naga kuma wannan Sakaryan. ?
Sakina ta tabe baki kafin tace"Nima yadda kika ganta haka na ganta..Ashe da ita zai taho..!
Anty Amarya tace"To me kika fahimta da Zamansu tana nan a Hotonka ko kin Fahimci sauyi. !?
Sakina tace"Anya..?nidai ban Fahimci komai ba..!
Anty Amarya tace"To ki saka musu ido duk nasan aikin mallam na Dadewa yana Tasiri..!
Da toh sakina ta amsa mata suka Ciga da Kulle kullen su tana bata Labarin Tambayar da Sarood tayi na wacce ta Zauna Adakinta da abunda Sakinar tace mata Anty Amarya na Dariya tace"Gwara da kika fadamata haka..Sakaryan sai ta bisa da tsiya..Ai Amina ba zaman gidanki ba ma Mijin da garin gumel gabadaya ne ya gagareta. waya gayamata Barno gabas take..!
Sakina Tayi dariya kafin tace"Wlh kamar fa anyi ruwa an Dauke ko mganar fa bayayi..!.
Anty Amarya tace"Ai bazai yi ba..Wayama sani ko auran ya Dade da Mutuwa fasawa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login