Showing 33001 words to 36000 words out of 96407 words

Chapter 12 - FANSAR MACE Book Complete by Mrs Isham.docx

07 Aug 2025

3613

“ sorry dear abinda yasa haka ni mutum ce me son privacy, I love my privacy shisa ka” sun fahimceta tunda kowa yanada raayin sa

“shikenan to mu yi bacci da wuri saboda mu tashi da wuri gobe sunday zamu je shopping in mun yi saa Uncle Haydar ya kai mu,dan ya Sameer na masa magana yace min gobe akwai in da ze he, kun ga kuma Uncle baya zuwa aiki a weekend “

“ to hajiya Ameera “

tare suka haura sama ita ta shiga part din Adda su kuma suka shiga na su,dakinta ta shiga ta sa key ta rage Kayan jikin ta riga mara nauyi ta sanya ta kwanta.

Yana tsaye a corridor ya hango shiganta part din Adda, kwafa yayi yana tuna dazun da ta watsa masa ruwan zafi “za ki san kin yi da Sameer Ɗan gaske se ne miki abinda ba ki yi tunani ba shegiya figaggiya “ ya wuce part din sa.

A bangaren Haydar kuwa tunda ya shigo yayi wanka ya zauna yasa system a gaba ze fara aiki amma ya kasa tunanin ta gaba daya ya cika masa zuciya ko rufe ido ya yi ita yake gani a hankali ya mari kan sa da zummar ya dawo dede “menene abinda yake damunka ne Haydar,focus on your work “ ya faɗawa kan sa.

Washe gari bayan ta idar da sallah tayi azkar ne ta nufi bedroom din Adda suka gaisa fuska Adda da faraa ta ce “jiya yaushe ki ka tafi dakin ki?”

Dariya tayi “Adda mu na hira ki ka yi bacci abin ki shine na tafi”

“Ai haka na ke, daga zaran na miƙe kan gado shikenan bacci yake sace ni,yau ne Uncle din ku ze kai ku shopping ko? ”

Gyada kai tayi tace “ehh haka Ameera ta gaya mana jiya”

“Tom Masha Allah in kun je ki ɗauki duk abubuwan da ki ke bukata. kar ki tsaya kunya kin ji ko?zan gaya masa ya siya miki waya ma naga baki da waya “

“To Adda Allah yasa ka”

“Ameen” , “amma Adda meyasa ake ce masa uncle ?”

Ɗan dariya Adda ta yi “saboda shi takwaran kawu na ne to shine ne fa Hajja Hauwa take ce mai me sunan uncle lokacin da yake ƙarami, daga nan kawai sunan ya bi sa uncle Haydar,uncle Haydar” dama hakan na ranta ta rasa me yasa kaff yan familyn suke ce masa uncle bayan kamata ya yi su ce mai Yaya kamar yanda suke cewa Sameer yaya. Amma yanzu ta gane dalili.

“Oooh nagane bari in je in dubo su Ameera” part din su ta nufa da Meenal ta fara yin clear a falo tana video call daga ita se guntun wando da riga vest ko kallon ta bata yi ba ta shige bedroom inda take jin muryoyin su.

Wasan banza ta iske su suna yi kamar wasu yara se jefawa junan su pillow suke yi suna ihu da tsalle akan gado tsayawa tayi daga bakin kofa tana kallan su,tunawa tayi yanda suke wasa da Zaid da Aryan su yi ta zagaye gidan ko su yi ta wasan ruwa. Ganin su da tayi ya tuna mata da yan uwanta zuciyarta ne ta ji yana so ya fara yi mata zafi hakan yasa ta ɗaura hannun ta akai ta dafe setin gurin tana sauke numfashi .

Yusra ce ta fara lura da ita “ya ki ka tsaya daga bakin kofa ki shigo mana” duk sauran kallon ta suka yi murmushi yaƙe tayi ta shigo ta zauna.

“Ahh lallai baku da matsala na ɗauka zan shigo in same ku ko kuna bacci”

“To ai idon mu biyo tun 4 muke ta hira kin tashi lfy ?”

“Lafiya lau Zainab fatan kuma haka” Duk suka amsa da “Alhamdulillah “

“Kun san meye?” Yusra da tayi tambayan suka kalla suna jiran ji meye take son ce musu “se kin faɗa” “yau so nake yi bayan mun dawo daga shopping mu tafi yawo cikin gari tunda na dawo ban fita ba zaman gida is so boring” they all agree with her idea banda Alisha da bata sa musu ba ki ba.

“Zamu je ko Lisha “ tayi tambayar tana kashe mata ido daya

“ I don’t think so” tana faɗar haka ta kwanta a gadon tana jin su suna hira, amma ba ta tashi ba ita damuwar da take ciki a rayuwar nan ma kaɗai ya ishe ta. Ba domin ta zo gidan su da niyar ɗaukan fansa bane da ko murmushinta ba za su gani ba balle ta musu magana. Amma ba ta da zaɓi da ya wuce ta dinga pretending,dole ta saki ranta saboda ta samu shiga jikin su da kyau yanda zasu yarda da ita dakyau-dakyau amma in ba dan wannan ba da magana da murmushi sun jima da zama tarihi a gurinta.

Yau tsabar hiran da suke yi ko dinning din sun ki sauka su ɗauki breakfast. Ƙarshe ma sa me aikin su tayi aka kawo musu abincin dakin. suhudu su ka ci Meenal kuma na ta daban tana falo har yanzu video call din take yi.

Yau ma kamar jiya haka wannan saurayin ya dawo gidan amma kasancewar yau Sunday me gadi sam ya hanasa shiga babu irin magiyar da be masa ba amma yace ba ze yi kasada da aikin sa ba dan haka ya tafi. shi kuma yace yau in be ga Haydar Ɗan gaske ba tofa ba ze taɓa barın kofar gidan ba. Haka ya samu guri a bakin gate din ya zauna tare da cin alwashin ko kwana ze yi a gun yau se ya gana da Haydar.

Karfe sha daya su ka gama shirin su na zuwa kasuwa. ita de falazo ta saka da karamar riga ta ɗaura babban hijabi akai har yana sharan ƙasa, ta fito hannun ta riƙe da niqabi da za ta ɗaura. suna ganin ta da niqab suka kwace wai gaskiya bazata sa niqab ba, ta ƙi yin kwalliya sannan yanzu ta ce za ta sa niqab su ba su yarda ba, ba yanda ta iya haka ta hakura da sawa tunda sun kwace Adda dake zaune tana jin su se dariya take musu

“Yoooo ni na ga ikon Allah yarinya ta saba sa kayanta ku Kyale ta mana”

Adda ta faɗa tana riƙe haɓa,Yusra tace “ah ah Adda shopping fa zamu ba islamiyya ko kuma taron MSS ba “

Suna tsaye a falon Haydar ya sauko se baza kamshi yake yi ,yai kyau cikin shigan half jumfa sky blue da ya sanya duk gaishe sa suka yi cikin girmamawa

“Kun gama ko?” “Yes uncle “

“Adda mun tafi se mun dawo. yau yaran ki sun rantse ni zan zama driver su “

“Yooo ya za ka yi ku je kawai ku dawo uncle din yan mata “ gaba daya dariya suka yi harda Alisha dan itama abinda Adda ta c ya sanyata dariya sallama su ka mata su ka tafi banda Meenal da take can daki tana bacci.

Fitowa suka yi farfajiyar gidan already ya sa driver ya fitar masa da motar sa kirar Mercedes Benz wane. hakan yasa me gadi ya buɗe musu kofa duk suka fito ya yi saura Ameera da Alisha ne a ciki ba su fito ba tukun. Wani dadi ne ya ji ya kamasa tsabar farin ciki kamar ya zubar da hawaye lokacin da ya ga fitowar Haydar da sauri ya ƙaraso gun sa, time din yayi dede da ze shiga motar sa

“Sir Haydar dan Allah in ci arzikin fiyayyen halitta ka ba nı kaɗan daga cikin lokacin ka na zo maka da magana me muhimmanci” dakatawa yay ya juyo ya kalle sa amma se ya ga be gane sa ba cikin mutuntawa ya ce “saurayi faɗi ya aka yi “dede ta nutsuwar sa ya yi yace “ko zamu ɗan keɓance da kai ?”

Kallon su Yusra ya yi ya ce su shiga motar shi kuma ya jinginu da jikin motar yana harɗe hannun sa a kirji ya zuba mai ido.

“Sunana Muhajid Abbakar Sadeeq jiya nazo gurin ka an hana ni ganinka yallabai nazo maka da magana me muhimmanci “

“Ina jin ka Mujahid”

Ya ci gaba da faɗin “Taimakon ka nake nema akan ceton wani wanda yake cikin halin rayuwa ko mutuwa dan gidan s……..sa…..sa” sunan da yake so ambata ne ya sarƙe masa a baki ya fara in-ina jikinsa ya ɗau rawa, idanunsa suka fiffito kamar wanda ya ga mugun abu. ba komai ya gani ba face Alisha da ta fito yanzu ita da Ameera kallon direction da ya kafe da ido da har yasa ya shiga wannan hali na tashin hankalin Haydar yayi ya ga Alisha da Ameera tambayar kansa yayi to me yasa daga ganin su ya shiga wannan halin amma to meyasa.

“Lafiya ka ke kuwa” ya jefa masa tambaya se a sannan su ka kalli wanda Haydar din ya yi wa magana. lokacin da ta yi arba dashi wani irin bugawa gabanta yayi se da ta ji naman zuciyarta ya motsa sannan ya fara harbawa fat-fat-fat wanda mutum inde yana kusa da ita sosai to tabbas dole ne ya ji heartbeat na ta,amma duk da halin da ta shiga be hanata kamewa da kuma tsuke fuska ba tayi tamkar bata taɓa sanın sa a rayuwarta ba.

Gaba daya ya gagara magana ya san tabbas idanunsa ba karya suke yi masa ba kuma ba gizo ba, tabbas wannan ita ce amma ai ta mutu kenan wannan fatalwarta ce a gidan ko kuma de wata ce me kama da ita.

Se mun hadu ranan Monday in sha Allah,kamar yanda ku ka sanı bana posting a weekend 🥰🥰

yawan comment da sharing da like din da zaku yi shi ze tabbatar min da kuna jin dadin wannan littafi,your comments really mean a lot to me ☺️❤️

Don’t forget to comment,share and like 👍

Today is Friday don’t forget to recite Suratul kahf, sannan a yi wa annabi salati. Allah ya sadamu da alkairin dake cikin wannan rana.

19 & 20_*🦋FANSAR MACE🦋*_

Story & written

By

MRS ISHAM

~The writer of ~

*NIDA PATIENT DINA*

*ASHE ZAMUGA JUNA*

*ƊAYA CIKIN BIYU*

*MAKIRIN IKO*

and now

🦋FANSAR MACE🦋

JARUMAI

WRITERS ASSOCIATION

📚📚📚🖋️🤩

19 & 20

Kallon Alisha yai ya ce “Alisha ku shiga motar ina zuwa” shiga tai batare da ta sa'ke kallon inda ya ke ba, a ran sa ya furta “tabbas ita ce,wallahi Alisha ce tunda ga shi ya kira sunan ta,to menene ya faru? “

“Mujahid shin ka san ta ne?” Haydar ya katse masa zancen zucin da ya ke yi, a sukwane ya kalle sa sannan ya kalli motar da ta shiga ya girgiza kai kamar wawa “ah ah ban san ta ba”

“Shikenan to ina jinka kana cewa meye ɗazun?”

“Sir abinda na ke son cewa na manta yanzu. hankali na ya koma kan gıda gobe zan zo se in faɗa maka” yana gama magana ya tafi ya bar Haydar tsaye cike da mamakin ɗabi’ar sa. da farko ya ce yana son magana dashi, yanzu kuma yace hankalin sa yayi gida, nan ya fara tunanin to meye dalilin haka ganin ze ɓata wa Kansa lokacine ya sa ya shiga motar.

Tunda ta zauna take jin ta tamkar a ƙaya ta zauna. gani ta ke yanzu asirinta ya gama tonuwa, domin ta na da yaƙinin Mujahid yana da alaƙa da gidan Ɗan gaske. me ze faru in ya faɗawa Haydar ita din wacece?hankalin ta gaba daya ya tashi. ganin Haydar ya shigo motar ne ya ɗan dube ta be ce komai ba yasa ta furta

“Is over for me. shikenan yanzu Haydar ya san gaskiya,yakamata mu na isa super market in samu in gudu tun kafin hankalin sa ya dawo kaina” wannan shine shawaran da ta gama yankewa saboda shine kawai mafita a gareta domin cikar muradinta, matukar tabar Haydar ya tsareta to fa shikenan wasanta ya zo ƙarshe, ita kuma baza ta so wasan ya ƙare ba har se ta ruguza ahalin Ɗan gaske da sauran su.

Su Ameera suna ta yi mata magana amma shuru ba amsa hankalin ta sam baya cikin motar yanda zata yi ta tsere kawai take tunani,yana driving yana kallonta ta mirror, jira ya ke su isa ya tambayeta meyake damunta.

Su na isa suka fita a motar za su shiga cikine Haydar ya ce “ina da magana da ke “ su Ameera suka shiga suka bar ta tsaye a gurin jin yace yana da magana da ita,kirjinta dukan tara-tara kawai yake yi, tsoron me ze faɗa mata take yi. amman sam a zahiri ba ta nu na ba ta iso gabansa ta tsaya ya buɗe baki ze mata magana kenan aka kira sa a waya hakan yasa yace mata “minti daya “ ya ɗaga wayar ya matsa gefe yana me juya mata baya.

Ta na ganin wannan opportunity din ta silale ta bar gurin ta nufi hanyar fita a super market din. tana tsaye a bakin hanya ta kare fuskarta da hijab dinta se kalle-kalle take tana roƙon Allah ya kawo mata abun hawa cikin gaggawa se ga napep ko ciniki ba su yi ba ta faɗa ciki tana sanar dashi in da ze kai ta. har ta shiga napep din hankalin ta bawai ya kwanta bane gani take Haydar ze biyo ta a baya se da suka yi nisa tukuna ta samu relief, dede hanyar da za'a shiga anguwa uku wajen titin jirgin ƙasa man napep ya ƙare. sauka tayi me napep yace ta ba sa kudin sa ta tari wani saboda babu inda ake saida mai nan kusa, amma naira daya babu a jikinta, ta rasa yanda zata yi dama niyar ta in sun İsa gida ne ta karɓi kudi a gun inna ta bashi, to ga yanzu yanda ta kasance.

“Alisha” ta ji an kira sunan ta gagara motsawa tayi saboda ba ta san wanene idon ta ze gane mata ba. Ganin ta ƙi waigowa ne yasa shi cewa me napep din “nawane kudin ka malam? ”

“Dari tara ne” hannu ya sa a aljihu ya fito da gudan 1k ya basa sannan ya zagayo ta gabanta suna kallon juna. me napep kuma ya tura napep din sa yayi gaba wajen ya yi saura su biyu kawai

“Alisha dama kina raye?ya aka yi ke ba ki mutu ba. Sannan me ki ka je yi a gidan Ɗan gaske? “

“Kai ne ya kamata in yi wa wannan tambayar mujahid, menene dangantakar da yake tsakanin ka da ahalin Ɗan gaske?. Meyasa dan ka gan ni za ka sanar da Haydar Modibbo Ɗan gaske asalina? shin ka san abinda wayannan mutanen suka yi min ?”

“Nooo Alisha ban sanar dashi komai ba lokacin da na gan ki kwakwalwata dakatawa yayi da aiki “

A fusace take kallan sa ta san karya ya ke yi mata, hannun ta duka biyu ta sa ta chakumi wuyar rigarsa “karya ka ke yi Mujahid ka yi kaɗan ka yaudare ni,babu mahalukin da ya isa ya dakatar da ni daga abinda na fara,da kai da kasan gaskiya da kuma su din duk ba ci gaba da rayuwa za ku yi ba”

Tayi maganar tana zaro ƴar ƙaramar wuka a kugunta ta sa mai a wuya,ganin dagaske illata sa zata yi ga layin shuru babu kowa yanzu saboda yanda ake zabga rana,murya na rawa ya hau faɗin “Alisha ki dakata ki saurare ni,na rantse ban sanar masa da komai ba wlh ki yarda da ni”

“Ba na taɓa yarda da duk wanda ya yi kokarin wargaza min shirina, motsi kaɗan ka sa'ke yi zan raba wuyanka da gangan jikinka.“ tayi maganar tana matso da wukar setin maƙoshinsa

“A…ali…..sha na je gurin sa ne domin magana akan abinda ya shafe ku ke da family din ki, na je neman taimakon sa ne da kuma sanar dashi rashin adalcin da aka mu ku”

Yanda ya ke magana ya tabbatar mata da ya san abinda ya faru dasu to amman ya aka yi ya sani ? Saboda babu wanda ya san abinda ya faru a wannan daren nan, daga ita, se su wayanda suka aikata musu hakan ,se kuma Allah da ya ke ganin komai amma se ga shi Mujahid ya san abinda ya faru to taya aka yi ya sani kenan?, waye ya sanar dashi wannan magana. Tsabar zuciyar ta a bushe ya ke ko tsoron yanda ya fita girma bata ji ba, saboda Mujahid din sa’an Zaid ne kuma babban abokin Zaid.

“Ya aka yi ka san wannan maganar Mujahid ?”

“To kin sa min wuka a wuya ta ya zan gaya miki gaskiya ? “

Ba ta cire wukar ba se da tace “don’t try to act smart, wlh ka yi kokarin yaudarana ba za ka tsira ba”

Yana in-ina ya ce “na amince” cire wukar ta yi,hannu yasa yana shafa wuyansa da ya kusan bakuntan lahira se da ya gama haki tukuna ya soma cewa

“Ban je gurin Haydar Ɗan gaske saboda ina da alaka dashi ba,se dan tattaunawa akan maganar kisan gillan da aka yi muku. Amma ganin ki ya matukar tsorata ni, na shiga firgici da tunanin me yake faruwa dani hakan yasa ban iya ce masa komai ba na tafi,ban bar cikin anguwar ba se da na ga kun tafi hakan yasa na tari mashin na bi bayan ku, amma bayan da ku ka isa se na ga kina neman abun hawa a bakin titi bayan ki na bi dan ganin ina za ki je “

“Duk na ji wannan,go straight to the point“

“Na san komai akan abinda aka yi muku duk wani bayani ina dashi. Wallahi Alisha kawai banda yanda zan yi ne amma na so ɗaukar mu ku fansa amma waye ze tsaya min ta ina zan fara?sannan kuma yanzu ƙasar nan ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login