Showing 87001 words to 90000 words out of 178062 words

Chapter 30 - MAR ADAMS BOOK 3 COMPLETE BY AYSHA BAGUDU.txt

takwas a gida take masa "adamcy !"mami ta kira sunansa ahankali ata ya juyo yana kallonta kafin ya dauke tsumammun idanushin daga cikin idanun maminsa ya yunkura ya tashi ya zauan yana dafe goshinsa da hannunsa daya kusan minti goma mami ta dauka tana kallonsa batare da tayi yunkurin cewa komai ba sai dai yanayinsa take karanta yanayinsa yau tamkar wani mara lafiya tana kallonsa ya gyara zamansa tare da numfasawa ya zare takalmin qafarsa da duk dottin unguwar maryama ne yayi shiru kawai yana kallonsu gabansa na fad’uwa .”
tsawon lokaci mami ta dauka tana dubansa yayinda cikin zafin rai ya kamo lips dinsa na kasa ya soma cizawa da karfi sakamakon hawayen da yaji yana kokarin son zubo masa." wani irin nauyin zuciyarsa tayi "yana ji yadda qirjinsa ke masa zafi da ciwo tamkar an daura masa dutse mai shege nauyi a sama kirjinsa yanayinsa yasa hankalin mami yayi matukar tashi duk abinda kaga ya maida adamcy haka baqaramin abu bane ."






guri mami tasamu nan kusa dashi ta zauna tare da kamo tafin hannushi cikin nata tana mai cigaba da nazarin yanayin daya yake ciki ,ka natsu ka kwantar min da hankalinka adamcy ka daina sakawa zuciyarka damuwa too much idan ba haka ba zaka Sakani a tashin hankali. fad'a min wani abu ya faru ne a AGC ?tayi masa tambayr cike da kulawa irin ta uwa hannusa ya kai goshinsa yana sauke numfashi "zuwa Ibrahim uku bai sameka ba ko akwai wata matsala ne data taso ?dago tsumammun idanushi yayi yana kallon mami dasu "ni a wajena babu wata matsala sai dai ko daga garesa "to allah yasa shima haka .ka kai dare a waje a ina ka tsaya haka”?shiru yayi gabansa na cigaba da luguden bugu “ko kuma nace ina kaje daka kwaso dotti mai muni haka .”
Takalmansa yabi da kallo yana mai runtse idanunshi “duk takalminka ya 'bata step da parlour'n ka ?shiru yayi kawai yana soso gefen kanshi "ko wajen wannan sabuwar maaikaciyar kaje ?sake kallonta yayi a d’an rikice "adamcy kana son yarinyar nan? "take yaji wani abu ya tsigar masa a gabad’aya ilahirin jikinsa yana yawo cikin ’ bargo da tsoka tsayawa yayi yana kallonta ya kasa kwakwarar motse ballanantana yace mata wani abu .”






ahankali 'mani ta numfasa sannan ta cigaba magana “wannan shine karo ba biyu dana tambayeka , irin wannan soyayyar zaka boyewa sweetheart dinka "?zan so naga yarinyar nan naga abinda tafi maryam dina dashi, nasani baza tafi maryam dina da komai ba, maryam dina yar asali ce yar dangi ce ,yar gata ce, kuma mai galihu ce ace mutun yana da dangina kamata ai abun ayi alfahari dashi ne “shiru yayi yana duban mami yana nazarin inda maganrta ta dosa "kenan dai hasashensa ya tabbata idan ya kawo maryama matsayin matar da zai aura ahlinsa bazasu amince ba, idan kuma sun amince zabasu sota ba zasu kyamaceta ?yayi wa kanshi tamabayr "ina son naganta adamcy da kyar ata ya samu ya had'iye abinda yaji ya tsaya matsa a makoshinsa sannan 'ahankali ya iya motsa lip's dinsa tare da kiran sunan mami " sweetheart ki bar maganr nan zamuyi later mami ta katse shi ta hanyar daga masa hannuta, nasan halinka adamcy bazaa qara maganar ba "ki kwantar da hankalinki yarinyar zata zo a gidan nan zaayi presentations kinga dole zaki ganta amamn fa babu komai a tsakanina daita bayan shaani na aiki ."ya fad'a yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa."






"yanzu kai haka zaka qare rayuwarka ?we will talk about it later “yana gama fadar haka ya shige bathroom."shiru mami tayi tare da bin kofar daya rufo da ido ."tarasa gane abinda ke damun tunanin d'anta shine zurfin ciki shine miskilanci shine jin kai shine rashin son magan shine rashin kunya ya rabbi ka taimakeni ni idan son yarinyar ma yake ya kawo min ita amatsayin wacce zai aura zan fi samun natsuwa dan gara yayi aure da zaman da yake haka tana bukatar ganin ya'yansa masu tarin yawa gashi ance maryam mace zata haifa tana son duk abinda ke cikinta amamn taso ace d'a namiji zata haifa masa domin kuwa haihuwar da namiji yana bawa uwa kariya daga duk abinda zai taso gaba na tashin hankali ,domin ita karon kanta misali ce tayi imani da babu adamcy acikin rayuwar ita da ya'yanta mata da tana ji kuma tana gani zata kaskanta acikin dangin ubansa amman tun yana yaro yake takawa duk wanda ya nemi ya kawo mata rainin hankali burki ."






Bangaren maryama har qarfe d'aya na dare idanuta sun kasa runtsawa ta yunkura ta tashi ta zauna sosai a tsakiyar katifarta ta janyo pillow ta rungume tsam a qirjinta tana going over maganganun mr ata tana son ta gano wata gaskiya da yake qoqarin boye mata ,wani bangaren na zuciyarta sai taji tana so ta yarda a cikin yanayinsa akwai alamun soyayya amma kuma acikin maganganunsa kwata kwata babu wata alama ,acikin kwayar idanunshi ma zaa iya tabbatar da akwai wani abu acikin zuciyarsa .”shiru tana tana tariyo irin kallon da yake mata domin son gano wani abu .”girgiza kai tayi tace “wad'an mugayen idanuwan nashi babu komai acikinsu sai tarin firgici "Idan kin san baki tashi aure ba a yanzu kar na qara ganin kin kula sultan magana ma ta fatar baki kar ya qara shiga tsakaninku dashi maganarsa kusan ta qarshe kenan to me yake nufi da hakan shi bai ce yana sonta ba sannan kuma zai ce karta kula wanda ya nuna yana sonta ."






Kwakwalwa maryama ta bude sosai duk abinda mr ata ya fada sun samu kyakkwan mazauni acikin
zuciyarta ta rufe shayayyun idanunta ta jingina bayanta da jikin gado ta sake rungume pillown dake makale a qirjinta tana jujjuya maganganunsa tana kuma yin filla filla da su tana so ta fito da komai daga rami daya shige ya fake a ciki, ta sake tariyo hirarsu da sultan a kanta ta kuma hada da maganar sa, ta so ta fahimci abubuwa da dama a kansa amma wani abu guda daya yafi komai girma, he is smart duk abinda yake yana yinsa da gogewa idan ba mugun karantarshi kayi ba bazaka ta'ba gane inda ya dosa ba , maganar sultan kuma wannan ba wani abun damuwa bane a wajenta saboda a yanzu ba soyayya bace a gabanta kamar yadda ta sheidawa mr ata bare tayi tunanin aure a nan kusa , abu daya yake tsaye a cikin zuciyarta wanda yasa kwakwalwata ya kasa samun kwanciya shine yaya sadam dinta da take jin har yau cewar yana raye ."






Washegari maryama bata samu zuwa office da wuri ba sai wajajen karfe goma da wasu mintuna dan tuni duk wani maaikacin dake aiki a qarshin AGC yana cikin kuma yana kan aiki jiki a sanyaye ta shigo office dinsu bakinta d'auke da sallama ta gaishesu ta cire jakarta sannan ta samu waje ta zauna tare da yin shiru tana kallon sauran abokan aikinta da suka dukufa suna kan aiki madam some ta shigo tace "sai yanzu maryama ?me yasa baki d'aukar aikinki da mahimanci ai shikenan daman idan kana jin mugunta bakayi wa kanka ba ai baka cika mugu ba. "maryama ta kalleta a kaikaice sannan tace "madam please me haka yake nufi ?"ina nufin duk ranar da sir ya gaji da halinki ya dakatar dake kinga ai kanki kika cuta ,"maryama ta numfasa sannan tace "duk abinda Allah ya hukunto akaina daidai ne "ai shi kenan kuma daman muslim’s din nan haka kuke da taurin kai ,ga aikinki gobe zaa kar'ba idan kuma kingama shi a yau mrs ata zai ji dadi maryama tasa hannu ta kar'ba tana cewa me zaa zana? ahankali madam some ta soma mata bayani tana gama mata bayani ta fita ."






Maryama ta mike ta dauki jakarta ta fice daga office din ta koma qasa office din da'aka maida ema.
yayi matukar mamakin ganinta amman dake bai san zuciyar mr ata bace kawai ya sakar mata murmushi yana murnar ganinta wunin ranar tana tare da ema inda mr ata bai sanyata acikin kwayar idanunshi ba amman dai ance masa tazo kuma har an bata aiki sai dai bai nemeta ba duk da kwayar idanunshi ita suke son gani amman ya danne saboda kar ya bada kofar da wasu zasu fahimci halin da yake ciki ."
karfe shida daidai maryama ta hawo sama ta ajiye aikinta a gaban madam some dake zaune tayi mata sallama tace zata wuce gida tana gama fadar hk ta juya bayanta ya hango daga inda take zaune tana rausaya kmr ba daga wacan jagwal gwalaliyar unguwar take fitowa ba komai mata tsab tsab kuma a natse . ya hard'e qafafuwansa waje d'aya yana cigaba da kallon yadda take juya sansar jikinta anya kuwa bazata koma saka asalin kamilalliyar suturarta ba ? dan irin wannan tafiyar ai sai wani yayi masa ganganci ,haka ma the next day a kasa tayi aikinta tare da ema duk yadda mr ata yaso ya ganta taki yarda su had'u aranta tace "aiki take masa ba jikinta ta kawo masa ya dinga ta'bawa ba yana yin yadda yaga dama ita ba ."






Tsawon kwanaki biyu kenan bai sanyata acikin idanunshi ba sai dai ya hangeta daga nesa ta shigo ko ta sauka hankalinta ma gabad'aya baya Kanshi tsabgar gabanta kawai take, yana zaune akan kujera sanye da riga da wondo blue sai yar cikinta light blue yayinda nick tied dinsa ya kasance brown colou hannunsa rike da wani nicktie din brown yana nadewa ahankali har ya gama ya soka cikin aljihun gaban rigarsa yana kallonta ta shigo office din some . gata ga office dinsa amman ko d'aga ido tayi ta kalli office dinsa batayi ba haka yana kallonta ta juya yaga ta nufi qasa wani zazzafan numfashi ya sauke sannan ya yunkura ya mike ya fito ya biyo bayanta tana zaune tare da ema da wasu ma'aikatan takalmansa ya shigo office din ,kamshin sanyayyen turarensa daya ziyarci hancinta da kuma bugun da zuciyata yayi ne ya tabbatar mata da shine ya shigo "good morning sir "!!! duk ma'aikatan dake cikin office din sai daya gaishesa illa ita qoqarin juyowa take ta gaishesa taji sautin muryarsa a zafafe "ke me kike yi anan ? cikin tsananin firgita, da tsinkewar zuciya da tsoro, tare da kyarman jiki, ta qarasa juyowa ta fuskanci inda yake tsaye sanye da suit yayi matukar kyau kamar wani matashi dan shekara talatin” just one second na baki ki tattara ki koma inda aka ajiyeki. tamkar gilmawar walkiya yaga ta zabura ta mike ta rungume jakarta da kayan aikinta gam-gam cikin tsuma da karkarwa ta bace .




wani irin masifeffen dariya ne ya taso masa tun daga kasan zuciyarshi har zuwa kan lips dinshi amman dole ya taune lip din shi na kasa kana ya gimtse ya murtuke fuska cikin tsare gida yace.ema "! yes sir ya fad’a cike da girmamawa “da alamun kagaji da aiki damu ko ?"no sir wallahi babu ruwana sir bance .."
“enough! ya d’aga masa hannu “to be your last warning. iya abinda ya fad’a kenan ya juya ya koma office dinsa sai lokacin hankalinsa ya dawo gangar jikinsa duk lalacewa ko wani abu bazai had'asu ba gara tana sama yana kallon duk abinda take ."ranar kusan tare ma sukai aiki akan presentation dinsu dake motsawa ,yadda bata sakar masa fuska ba haka shima wanda daman shi kusan fuskarsa a daure take .”aiko ta gane bata da wayo dan ya lafta mata aiki kamar me dan haka a matukar gajiya ta qarasa gida tayi wanka tayi magriba da isha’i saboda tsananin gajiya ma bata ci abinci ba ta kwanta.”


******


Yau ne ya kama zaa gabatar da presentation zaune mr ata yake tare da client dinsa mutun uku a gidan mami tun daga sama yasa akayi decoration har zuwa kasa surayya ce ta fara fitowa sanye cikin riga da siket na suit tayi juyi kamar yadda yan fashions desings keyi sannan ta koma gefe ta tsaya sannan yusura ma ta fito tayi Kmr yadda surayya tayi mutun na uku some ce sai wasu maikata guda biyu sai maryama wacce ta sauko cikin doguwar riga ta rike gefen rigar kad'an tana rausaya tamkr wata fure wani murmushin ne mai daukar hankali kwance akan fuskarta wanda ya bayyana wushiriyarta da dimples dinta ,tayi matukar kyau sosai mr ata ya gyara zama yana kallonta tun daga samanta har qaraso saukowa kwayar idanunshi na kanta .”
Mutane da suka zo ganin new design dinsu suaki tafi yayinda mutun daya acikinsu yace "wooo gsky naji dadin ganin representation dinku yayi min kyau sosai thank you so much mr ATA "wannan desings din ya bambamta da sauran desing daka saba kazo da wani salo dabam daman kuma ina da yakinin AGC company ne kawai zatayi min abinda zai kwanta min arai akan kowani kamfani dan haka akan wannan suprisse din zanyi double din order kaya."




" that's great mr ATA ya fada tare da mikewa tsaye yace "just a second !yasa hannuwansa a aljihun wondon suit dinsa ya qarasa inda yammatan suke tsaye "sannuku da kokari aikinku yayi kyau "thank you sir suka hada baki gurin fadar haka" sir ko zamu iya zuwa mu canza ?yes of course" ya fad'a yana kallon cikin kwayar idanun maryama tayi kyau matuka itace ta fara yin hanyar sama yabi bayanta da wani shu'uminn kallo tare da yin taku a hankali yabi bayanta da kallo ,jikinta a sanyaye ta dan juyo dan kallon bayanta ai kuwa ta zame tayi baya luuuu zata fadi kan tayis aiko da wani irin sauri mr ata yasa hannuwansa duka ya tarota bayanta ta fado jikinsa ."






Mmn sudais
[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗


BOOK 3


*AYSHA A BAGUDO*


WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim


Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.




Page 26


Cike da sanyin jiki mami tabi bayan mr ata da kallo kafin ahankali ta d'auke idanunta ta maida kan baba qarami dake tsaye zuciyarsa cunkushe da haushi da bakinciki abinda mr ata yayi masa "kinga kalar tarbiyar ki ko ?a gabanki d'anki yayi min zagi bayan ya wulakanta maganata "tukuna ma ina alqawarin da kika min na cewa bazai yi aikin nan ba "?numfashi mami ta sauke kawai wanda hakan yayi sanadiyar qara hassala baba qarami dan haka a tsawace yace" kin tsareni da idanuwa kin kasa cewa komai tunda kinsan da had'in bakinki yayi komai ."shikenan tunda ke da d'anki kunyi son ranku amman fa ki sani bashi kuka ci." mami ta sake kallon baba qarami dake surfa maseefa ta hade hannu wanta waje d'aya kasamcewar ta rasa me zata ce masa ya fahimce ta .kusan mintuna goma ta d'auka tana kallonsa batare da tayi yunkurin dakatar dashi ba ko ce masa wani abu ba har sai daya gama amayar da abinda ke ransa sannan ta gyara tsayuwarta muryarta cike da laushi ta soma magana "dan girman allah baba qarami kayi hakuri kai ma kasan halin adamcy da taurin kai "sai da ya ta'be bakinsa sannan yace "ai dole kince min nayi hakuri tunda ke da d'anki kun gama ci min mutunci mami bata damu da maganarsa ba dan tasan kad’an daga halina idan ranshi ya ‘baci kamar adamcy ne .”








sake kwantar da murya mami tayi "ni dai hakuri nake baka kuma in sha allahu..."saurin d’aga mata hannu yayi dan baya da bukatar alqawari ta "dakata ya isheni haka karki cika min kunne naji amman wallahi wallahi kinji na rantse ki ga yawa wannan d'an iskan d'an naki ya kiyayyeni kar ya sake gigin sake aikata mana haka "shikenan hakan ma bazai sake faruwa ba zai kiyayye yayinda aranta tace “bama zai cigaba da kula da kamfanin ba ,ya bar maku har abada domin dai tasan halin d'anta idan yace yes yes ne haka zalika idan yace no tô no ne tunda yayi mata alqawarin bar masu kamfanin tasan bazai ta'ba dawowa ya canza magana ba."da rarrashi da komai uncle jay da yaya Ibrahim da mami suka samu ya hakura ya fice daga parlour'n tare da sultan ."
yayinda mr ata ke zaune akan kujera a bedroom dinsa yana zukar sigari ahankali yana magana a fili "wannan mutumin so yake sai muyiwa juna rashinmutunci tukun zai fita a tsabgata,ko ina ruwansa da yadda zanyi da rayuwata? zanyi aiki a duk lokacin da nake so kuma dole ku barni koda kuwa ranku bai so “saboda son zuciya irin nashi kawai ya zauna yana biyewa ya'yansa inda ni d'ansa ne zai min haka ?"ya tambayi kanshi yana jan dogon tsaki tare da shafa sumar kanshi da hannu d’aya sannan ya mike ya fad’a kan bed dinsa yana cigaba da zugar sigari ."






Direban daya d'aukosu maryama, yusura ya fara saukewa sannan maryama, karfe goma daidai na dare maryama ta shiga gidansu part din umma ta shiga inda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login