Showing 93001 words to 96000 words out of 178062 words
Chapter 32 - MAR ADAMS BOOK 3 COMPLETE BY AYSHA BAGUDU.txt
daya zaka maidashi makiyinka abinda shi bazai ta’ba yi maka ba kenan .”tana gama fadar hk ta juya ta kama gabanta baba qarami yabi bayanta da kallo ” daman ita haka zuciyarta take sam bata goyon bayan karya koda kuwa akan kanta ne kuma tabbas yasan gsky ta fad'a masa sai dai me zai yi yanzu ?” ya cigaba da zama a wajen yana tunani maganganunta."
Mmn Sudais
[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 27
Gabad'ayansu a tsaye suke acikin office dinsu fuskarsu d'auke da murnar samun nasarar da sukai
a jiya inda madam some ta zagayo ta tsaya kusa da maryama tare da dafa kafad'anta tace "duk wannan cigaba mun samu ne saboda ke . maryama ta saki kyakkyawan murmushi wanda yayi matuqar bayana kyawunta sannan tace " karki ce saboda ni ,nasarar gabadayanmu ce, kuma kowa acikinmu tayi kokari .
"kowance daga cikinmu ta cancacin yabo na mussa man tunda tare mukayi, wannan cigabanmu ne gbdy. ". sukai murmushin jin dadi suna sake yaba mata "amman fa duk da haka kin cancanci a miki ban girma ,kuma kinsan wani abu ?maryama ta girgiza mata kai tana cizan lip's dinta na qasa . "yanzu gbdy a kamfaninmu kece sama da kowa kuma kece wacce tafi kowa iya tsara zane mai d'aukar hankali you're the best maryama ."
"maryama ta sake yin murmushi batare da tace uffan ba ."sultana dake zaune tunda suka soma maganar bata ce komai ba sakamakon jin haushin babu ita ciki presentation din , sai dai aranta tace "in sha allahu wannan dariyar da kike yi sai tazame miki damuwa arayuwarki .
Ahankali yusura tayi taku ta nufo inda maryama take tsaye rungume da hannuwanta duka a qirji tace "ai sani ne bakuyi ba wannan nasarar ba komai bace a wajen maryama ,ai nasara a koda yaushe tana biye daita ,duk abinda tasa gaba sai tayi nasara, ba akan aiki ba kawai , ko akan karatu haka take akwaita da kwakwaluwa ko lokacin da muke karatu first class take d'auka ita din yar baiwa ce "karki manta ni din marainiya ce ta gaskiya tun da na bud'e idanuna na ganni acikin maraicin kinsani mahaifina ya rasu tun ina yarinya kakata data rungumi maraicinmu da kyau take nuna mana qauna muraran sai dai itama bamuyi tsawon rayuwa daita ba ta rasu kinga babu yadda zanyi dole na jajirce nayi karatu "duk da haka maryama ke din yar baiwa ce ,"kunga mu bar mgnr haka muyi aikin dake gabanmu kafin mr ata ya shigo ya fara rikita mana lissafi ". inji cewar maryama ."gabad'ayansu sukai dariya tare koma mazauninsu kowacce ta soma aikin dake gabanta .”
Alamun kira ne ya shigo wayar maryama adaidai lokacin da take qoqarin zama ta kai kallonta ga wayar tana duba number dake yawo a screen din wayar "number da ake yawon kiranta dashi ne wanda ta d'auka ko sultan ne sai dai daga baya ta fahimci bashi bane "dan ta nemi numbersa taga ba iri daya bace, ta d'aga kiran tare da yin shiru daga can bangaren ma shiru akayi ana sauke mata numfashi acikin kunnenta dan tana jin sautin saukarsu ahankali ta fara taku ta nufi kofar fita daga cikin office din yayinda sultana ta zuba ma bayanta ido ganin yadda take bada step tana rausaya abun burgewa yarinyar tana da shep na d'aukar hankali ,ba lallai kowani nmj ya ganta ya iya hadiye miyonsa akanta ba".maryama ta numfashi kana ta cire wayar a kunneta ta duba har lokacin mai shi yana kan layi sai dai babu alamun wannan saukar numfashi muryarta can kasan makoshi tace "hello !sai dai shiru taji babu amsa .
"hello wake magana? "ta sake yin mgn still dai shiru ne ya biyo baya kusan second biyar babu alamun zaayi magana dan haka tayi disconnecting din kiran ta nufo office tana tunanin kiranta daakayi mata kwanakin uku da suka wuce akace mata daga office ne wai tazo da wuri bayan tazo din kuma taji shiru bata ga kowa ba sai mr ata wanda tayi imani ba muryarsa bane ,to waye ya kirata ?"waye wannan da yake son dagula mata lissafi ?"ta furta a kasan ranta tare da samun guri ta zauna ta kasa aiwatar da komai tana sake zurfafa tunaninta lallai ya kamata ta nemi mai wannan number da yake kiranta taji dalilinsa na kira wayarta yana damun rayuwarta ."
Ahankali tai dealing number a qaramar wayarta ta shiga neman layin sai dai ba'a d'aga ba tana cikin wannan halin mr ATA ya shigo office din yayinda kwayar idanunshi ke kanta sai dai ganin hankalinta na kan wayarta yasa shi d'auke idanunshi akanta ya soma mgn a natse akan qokarin da sukai jiya "naji dadi sosai da qoqarinku na jiya na jinjiwa kokarinku "sir ai ina tunanin maryama ce ta cancanci haka,dan gsky ta cancanci jinjina har ma da especially thanks ".inji cewar madam some "ta fad'a tana murmushin farinciki .”
asukwane ya kalli inda take zaune inda tayi busy sosai wajen bincike layin daake damunta dashi a truecaller tana son taga da wani suna akayi registrater layin sai dai wani birkitaccen suna ta gani ."mr ata yayi shiru yana kallonta a tsanake yana nazarinta dan tunda ya shigo ya soma magana ya fahimci bata tare dashi,haka hankalinta yana wani guri dabam ya cigaba da kallonta kafin a hankali yayi taku biyu ya dawo kusa daita sosai yana kallon cikin wayar dake rike a hannunta still dai bata maida hankalinta garesa ba." abinda yafi tsana kenan daga gareta ta ganshi amman tayi kamar bata gansa ba aranshi yace ko number wa take kira hk "?amman a zahiri muryarsa a kausashe yace "some ke kinfi kowa sani ina bawa wad'an da kad'ai suka d'auki aikinsu da mahimanci ne lokacina,yayinda ita wannan macece da bata bawa aikinta mahimanci any way kizo kisame a office akwai ayyukan da zamu yi magana akansu yana gama fadar hk ya juya ya fice ."
Mr ata yana fita office dinsa ya koma ya zauna akan kujera yana juyi sai dai hankalinsa da nastuwarsa suna gareta ." yayinda ita kuma tayi busy gurin son gano ko waye yake son damun rayuwarta yana kallonta tasa wayarta ta dafe goshinta wanda daga gani ta rasa mafuta ne yasa tayi haka "to me yasa ba'a d'aga kiran ?"kuma idan ban kira ba bazan san kowaye ya kirani a akwanakin baya da km daren shekaranjiya har ma da yau din nan lallai ya kamata nasan kowaye daga cikin ma'aikatan kanfanin nan sosai mr ATA yake son yasan damuwarta." yana zaune a office dinsa amman kwayar idanunshi na kanta har sanda sultana ta shigo office din tana kiran sunansa wani irin mugun kallo ya jefa mata wanda yasa tayi saurin cewa”oh sorry sir congratulations sir duk da dai ni baa sakani ciki presentation ba wanda bansan ni laifin me nayi ba daaba sakani ba “wani irin matsefaffen haushinta yaji ya taso masa tun daga kahon zuciyarsa har zuwa kan fuskarsa sai dai bai yi magana ba ya cigaba da juyi akan kujera yana sake maida hankalinsa ga sarauniyarsa ."
ta sauke naunayen ajiyar zuciya kana ta cigaba da magana tana kallonsa "ko zan iya sanin dalili da yasa ni baa sakani ba bayan nima maaikaciyar kamfani ce kamar sauran ma'aikatan kamfani ?"irin Kallon da yake mata ne yasa gabanta ya dinga faduwa "I think kinzo office dan Kiyi aiki ne ?ta gyad'a masa kanta cike da rauni "okay pls kije kiyi aikinki ."wai dan Allah mai yasa ya Adam kake min hk Kmr ni ba jininka bace ?komai nayi sai ka nuna ni din ba kowa bace agurinka ,kasani wannan ba daidai bane this is not right ya Adam ko dan kaga na damu da kai ?"shiru yayi tare saisaita kanshi “kana yi kamar baka san me nake nufi ba alhalin kasani
“ka kuwa san irin son da nake maka ?"saboda kai na .." "actually get out ". ya fad'a a matukar fusace yana nuna mata hanyar fita da yatsan hannunsa d’aya tare da kiranta da nonsense."ranta a matukar bace ta fito da sauri tana goge hawayenta ta wuce maryama tsaye wacce kusan duk taji wasu daga cikin maganganunta ."
Cike da tausayawa maryama ta kira sunanta har sau biyu sultuna!sultana !!sai dai sultana bata tsaya ba sai ma qarasa wucewa da sauri tayi ,kai tsaye marayama ta bar abinda take ta juya ta nufi kofar office dinsa tana cewa "may I coming sir ?sai daya sauke naunayen ajiyar zuciya jin sautin muryarta mai sanyi sannan yace "coming !”dan tun safe bai ji muryarta ba sai yanzu ta shigo cikin office din a natse ta tsaya agabansa tana kallonsa a lokacin yana duba wani file dan haka bai dago ya kalleta ba ta cigaba da kallonsa a tsanake “kyau iya kyau ai dole mata su rikice akanka ganin ya shareta kuma tasan halinsa idan zata shekara tsaye matuqar bayi niyyar yin magana ba bazai mata ba .”dan haka muryarta a sanyaye tace "sir ina son nayi magana da kai ko zan iya ?”shiru yayi batare daya dago ba har ta cire da zai yi magana sannan ta jiyo sautin muryarsa acan kasan makoshi “uhm go and ahead “.
“Dan Allah sir me yasa kake yawon yiwa sultana ihu ko hantarrta fiyye da kowa acikin ma’aikatar nan alhalin ita din yaruwarka ce ta jini ?yana jinta amman yaki yin magana sai ma ajiye file din hannunsa yayi ya d’auki wani ya cigaba da dubawa "a zahirin gsky babu kyau abinda kake mata ai ko babu komai ita din jininka ce, kaga koma meye a tskaninku bai dace ka dinga disgata irin haka ba .
an ji mu idan ka mana ba wani abu bane kasancewar mu din ba komai bane a wajenka, amman ita kamata yayi ka manta komai idan ma akwai abinda tayi maka ka jata ajikinka "."ke wacece da zaki min wannan tmbyr ?" shiru tayi tsabar kunyar data mamaye ilahirin sansar jikinta Kmr ta nitse qasa haka taji ".sai daya gimtse ya murtuke fuska cikin tsare gira sannan ya sake maimaita mata tambayarsa "wacece ke tukunna ?"shiru maryama tayi ta kasa cewa komai duk da tasan zai iya aikata abinda yafi haka .”
“cikin ni dake waye ya rike past dinsa ya kasa manta komai “?ke da kika kasa manta abinda ya wuce a rayuwarki zakizo kina fadawa mutane nonsense and rubbish ".yayi mgnr yana tsareta da tsumammun idanusnhi masu matukar firgitarwa .“cikin ni da ke waye ya rike past disa fad'a min da har zakice na manta komai na jata ajikina ?"zuwa wannan lokacin ranta a matukar bace take kallonsa har ya rufe bakinsa ". "daman kana sane da past dina ne ?tai masa tamabayar zuciyarta na wani irin tsinkewa .
yay shiru yana kallonta d'an bashi da amsa da zai bata "koma dai menene zaka iya bata chance sir saboda soyayya tana bukatar kulawa kuma duk lalacewa kaso mai sonka sannan kayi amfani da damarka dan sultana na matukar sonka ." tana gama fad'ar haka ta juya har tayi taku biyu ta jiyo Amon muryarsa cikin yanayi na tashin hankali "wannna shine tunaninki "ta tsaya cak tare da juyowa tana dubansa kafin ahankali ta qara taku biyu ta yadda zai iya jinta sosai ".
“Bai wai shine tunanina ba, haka ne tana sonka kuma har ta furta hakan a yanzu wanda ni bansan sau adadi nawa tasha furta maka tana sonka ba amman dukkanin alamunta sun nuna .karka ga wai dan kana da kyau da kudi tare da nasaba kanemi ka wulakanta mutumin da ya damu da kai dan so .."are you still arguement with me?ya fad’a hk ta hanyar dakatar daita tayi shiru tana kallonsa taba jin wani irin mummunar fad'uwar gaba mai tsanani ."
Tana kallonsa cikin yanayin na jin kai ya mike ya tura kujerar da yake zaune akai baya kad'an ya fara taku zuwa inda take tsaye cikin tsananin tashin hankali taja baya da sauri jikinta na dan kyarma ya sake matsota sosai kamar zai rungumeta ajikinsa har suna iya jiyo bugun zukatansu cikin tsuma da karkarwa maryama tasa hannuta d'aya ta tokare qirjinsa dashi ji tayi kamar ta daura hannunta a saman dutse nan da nan ta soma furta kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun ,hasbunallahu wani imal wakil acikin zuciyarta.”
cikin d'an d'aga murya ya soma magana "ai nasani nasan ke kadai ce zaki iya wannan karfin halin ina fad'a kina fad'a ba .?"jikinta yaji yana rawa a saman qirjinsa ,naunayen ajiyar zuciya ya sauke sannan ya soma ja da baya tare da dauke kwayar idanunshi akanta yana mata gargadi da idanunshi ya koma mazauninsa ya maida hankalinsa kan laptop dinsa muryarsa can kasan makoshi yace "ba laifinki bane nasan dalilin dayasa kike min haka "me ka fad'a sir ? I don't know kuma karki qara tamabayata ."yayi maganar yana sake gargadinta da kwayar idanunshi sannan ya sake kai idanunshi ga laptop."karkayiwa mgnr wata fassaran dabam ni dai kawai na baka shawara ne dan ka gyara ina ma mata zasu kasance irina ?"dan ni bana daga cikin matan da zasu tsaya batawa kansu lokaci akan nmj ".
“really?
ya fad’a tare da dago kanshi yana dubanta muryar a fusace "ke da kika kasa manta mutumin daya mutu arayuwarki saboda son da kike masa shine zakice bakya daga cikin matan da suke iya bata lokacinsu akan nmj"? kenan ke din ba mace bace ? ko kuma ke din makaryaciya ."ta bud'e baki zata sake magana taji sautin muryarsa yace "go ....."mutuwar tsaye tayi,ta saki baki tana dubansa har sanda ya sake cewa "I saida go back to your work." ta juya da sauri ta fara tafiya "kai mr ata mugun mutun ne ,a gaskiya sultana baki yiwa kanki adalci ba ko kuma nace zuciyarki ta cuceki irin wannan mutumin zaki so “? Kwata kwata mutun bai da fahimta Jifa daga fad'a masa gaskiya ya hau kan mutun yana qoqarin razana mutun har yasa hanjin cikina ya fara hautsenewa ta qarasa fitowa tana bugo masa kofar da karfi ."
Shi kuwa mr ata tana fita wani irin dariya ne ya taso masa tun daga kasan zuciyarsa har zuwa kan lip's dinsa na kasa a zahiri ma kana iya hango hakan a tattare dashi dan kasa rike dariyar yayi "uhm tana cikin rukunin mata jarumai ,sannan karfin halinta na matukar burgesa most especially dakiya, gata da shegen tsoro amman tana qoqarin gurin dannewa ta fad'a min mgn son ranta lallai ba a banza zuciyata ta rasa sukuni akanta ba, daman kuma an halicceta ne dani ,duk abubuwa da yake mata yana mata haka ne saboda ya auna gudun zuciyarta akanshi kuma ya gano adadin gudunsa da alamun nan kusa zuciyarta zata makance a soyayyarsa ,shi din kwararren dan kasuwa ne sannnan kuma kwararren mai gane shaukin só né a karon farko aka fad'a soyayyarsa tabbas zai gane duk da cewar tana da jarumta amman kuma akwai burbushin tsoronsa da qaunarsa acikin kwayar idanunta "marayama kenan rigima zalla ko ina ruwanta da matsalar wata ?ban da rashin sani irin nata ina ita ina bawa wata damar ta so abinda zata so daga baya ."
flaks cup din tea ya d'auka ya kai bakinsa yana kurba ahankali yana kallonta tana kai kawo "me yasa ma na shiga harkar wannan mutumin taja tsaki tana rike kanta "wallahi yau ya gama bata min rai ta fad'a a fili tana furzar da iska mai zafi tana cigaba da sake neman number "cikin saa aka dauka akace " hello daga can bangaren "he..hello maryam ta furta cikin rawar murya bai bari tayi mgn ba ya cigaba da nashi mgnr "allah yasa kece mai wayar nan ina ta kiranki kina tare da saurayinki ko mijinki ne ni dai bansani ba na fad’a miki kin yarda da wayarki amman baki tsaya ba yanzu ina zanganki na baki wayarki maryama tayi shiru tana jinsa har sanda ya dasa aya ,kawai ta tsinci kanta da ce masa kana ina yanzu?" ta fadi haka ne saboda ta gano wanda ke damunta da kira yace"Ina nan Ikeja ta wajen jara shopping mall "wai muna da d'an nesa dan ina wajen aiki amman da ace daga gidanmu bamu da wani nisa amman ko zaka iya kawo min wayar wajen aikina sai na baka kudin mota har ma da qari ?"okay babu matsala a ina awajen aikinki yake ?."nan take maryama ta fad'a masa sannan ta koma cikin office tana zance zuciya.”
Bayan awa biyu mr ata ya shigo office din a natse gabadayansu suka natsu suna sauraran bayaninsa bayani yake masu akan nan da sabon wata zasu bar wannan kamfani zuwa wani dabam su cigaba da gudanar da aikinsu amman hankalin maryam naga kofar shigowa jira kawai take taga daya daga cikin securities yazo kiranta ,muryarsa a dake ya kira sunanta "maryam! ta juyo da sauri