Showing 105001 words to 108000 words out of 178062 words

Chapter 36 - MAR ADAMS BOOK 3 COMPLETE BY AYSHA BAGUDU.txt

baya tayi shiru tana jin mummunar faduwar gaba gabad'aya daga securities din bakin get din har na cikin ma'aikatan da masu tsaronsa babu wanda bai yi mamaki ba dan basu ta'ba ganin haka daga garesa ba har gara ma masu tsaronsa zasu iya cewa suna ganin yana yiwa mahaifiyarsa amman wata mace daban wannan ne farko ."ki bar wannan banzar tunanin naki ki shiga"ya fad'a yana hura hanci jiki a matukar sanyaye ta shiga ta zauna ya maida kofar ya rufe mata sannan ya soma qoqarin zagayawa inda kafin ya qarasa tuni a ruwa ya bud'e masa ya shiga ya zauna yana ware qafafuwansa wanda ya zame masa jiki sannan a ruwa ya shiga mazaunin direba ya tada motar suka nufi get ."






Shiru suna zaune a bayan motan sai driver a ruwa a mazauninshi, haka nan taji hawaye ya ziraro mata a sanda suke hau babban titi , ahankali ta juyar da kanta tana kallon gefen titi tana sheshekan kuka wani dogon tsaki yaja ,tana jinsa kamar zata juya ta kallesa sai kuma ta fasa,ta ci gaba da barin kanta a inda yake ya motsa bakinshi kamar zaice wani abu shima sai kuma ya fasa ya ciro d'aya daga cikin wayoyinsa dake qara mara sauti yanayin yadda taji yayi maganar tasan oga amar ne, bisa dukkan alamu maganar mai mahimanci ne "karka damu dole zan nemeka cikin satin nan "eh duk acikin satin zamuje gurinsa in sha allahu to gsky dai ban gama tantacewa ba, tsarin farko zanbi ko kuwa wani tsarin ne amman dai duk abinda ake ciki zan nemeka sukai sallama kana ya dan tsaya yna kallona"wallahi kukan nan yana maseefar kona min rai ."ya fad'a yana sake jan tsaki mutun yayita kuka baya tunanin halin da mutane zasu shiga” yayi maganar acan qasan makoshinsa ."






shiru tayi tana assessing maganarsa, ta juyo a sukwane taga ita yake kallo fuskashi a hade tamkar wanda aka aikowa da sakon mutuwa ."ahankali ta dauke kanta tare da tsaida hawayenta tana lissafi maganarsa "wallahi kukan nan yana maseefa kona min rai ,mutun yayita kuka baya tunanin halin da mutane zasu shiga "bata gama tunanin makomar maganarsa ba taji ya matso kusa daita sosai tare da daura kanshi akan kafad'anta wanda yasa ta sauke naunayen ajiyar zuciya "please maryama ki daina tunanin matacce haka ."numfashi ta sauke kawai .
bata ankara ba taji ya kamo hannunta mara ciwo cikin nashi "ina son ki daina tunaninsa ,ko zaki min wannan alqarin ?"tun kafin tace wani abu ya cigaba "yes I know you can do it for me "kiyi saboda ni bansan dalili ba maryama bana son ganinki cikin damuwar nan zaki daina tunaninsa " anya kuwa zata iya kuwa? Not thinking of yaya sadam dinta bayan a yanzu bata iya kwana ba tare data yi tunaninsa ba ? "Kullum sweetheart dina tana fad'a min yawon tunani yana illata zuciyar dan adam ta kallesa a tsanake tana sauke numfashi ".






"banason ki illata zuciyarki ko babu komai kina da qarancin shekarun ,kinyi kankatar da zaki jefa rayuwarki cikin over thinking haka .ta sake kallonsa taga har lokacin ita yake kallo sai dai fuskar nan tashi a hade take "nasan daga yau zaki daina ko? ya fad'a yana matse yatsun hannunta cikin nashi sai dai ta girgiza masa kanta ,alamun bazata iya ba, sai ya sake langwabe mata ya dawo kamar wani abun tausayi yana murza tafin hannunta cikin nashi .tayi qoqarin zare hannuta ya damke sosai yace "Please maryama wai mai yasa bakya tausayin kanki ne ?"
yayi mata tambayar yana mata tafiyar tsutsa a tsakiyar hannunta tayi saurin zare hannuna daga nasa tana yarfarwa kamar wadda wuta ta kona saboda wani yanayi da taji ya taso daga hannun nashi zuwa cikin nata, cikin kankanin lokaci ya zagaye dukkanin ilahirin jikinta ,cikin sarkewar murya tace "no sir I can't bazan ta'ba dainawa ba yaya sadam fa jinina ne ko babu aure atsananinmu babban yaya ne a wajena .“ina tabbatar maka idan babu baba gali a raye da yaya sadam yana raye shine ma daurin aurena .da mahaifina da mahaifinsa uwa daya uba daya ta yaya kake tunanin zan iya mantawa da wannan dangantar?"






ahankali ya lumshe mata tsumammun idanunsa yace "shikenan ba’a bukatar ki daina tunaninsa ki cigaba da tunaninsa idan kina só ma kema kije ki haqa rami ki shiga ki binne kanki “kai a ruwa miko min kwalin sigari "sigari kuma ?"ta furta a razane baqar maganar daya fad’a bai mata ciwo ba kamar abinda yake qoqarin aikatawa yanxu .a ruwa ya miko masa tare layter ja ya kar’ba ya bude ya ciro Karan sigari daya ya rike batare daya kai bakinsa ba duk tana kallonsa yayinda idanunta suka sake ciccikowa da ruwan hawaye ya janyo hannuta mara ciwo ya saka layter ciki "kunna min !"ya fad'a yana miko mata sigarin , zaro idanu tayi waje tana dubansa cike da matsanancin mamaki .hankalinsa kwnace yayi mata wannna banzar maganar aiko sai ganin hawaye yayi sharr suna gangaro mata ." numfashi ya sauke sannan ya sake kamo hannunta ya cire layter sa ya kunna sigari ya fara zuka ahankali ahankali hannu ta kai ta toshe hancinta tana tunanin abun yi ita kam tayi data sanin shiga motarsa mutun kamar mai ajanu sam shi baya son zaman lafiya yanzu daga magana me ya kawo batun ta kunna masa sigari ko shan sigari saboda Allah?"yayinda shi kuma ya kai hannu yana shafa goshinsa zuwa keyarsa .”






ahankali ta juyo garesa still hannunta na rufe da hancinta "sir !” ya kalle a d’age da gefen idanunshi “warin abar nan yana damuna "gara ki saba."gara ta saba kuma ?"wannan wace irin banzar magana ce " tayi maganar aranta “zuwa yanzu yaci ace kin fara sabawa da warin sigari "inna ilaihi "ta furta a fili"ita kam ta rasa gane inda maganganunsa suka dosa me yake nufi da hakan kuma?” tunda ya soma zugar sigarinsa bai kalleta ba sai yanzu da ya wani tsareta da tsumammun idanunshi da suka fara canza kala tare da dage mata girarsa d'aya yace "tsoro kike ji ne ?" cike da jin haushi ta fixge sigarin a hannunsa ta manna a gefen hannunta mai ciwo "kina hauka ne ?"
yayi mgnr a firgice yana cigaba da kallon hannun "kasan illar abinda kake yi kuwa ?muna cikin mota kana sha mana wannan qazantar "ka kuwa ma san yadda nake ji idan naga kana shan wannan abar ?"ta qarasa maganar tana juya masa baya sakamakon kukan daya kwace mata ."






ahankali ya kwanto jikinta tare da juyo daita garesa ya sake makale mata ya janyo hannunta ya tsura ma hannun ido "kalli illar da kika yiwa kanki "?gara wannan rad'ad'in akan zafin sigarin da kake sha a gabana "bai san sanda murmushi ya bayyana akan fuskarsa ba sai dai ya gintse yace "marayam kina da rigima "ai kai ne rigimam me ."tayi maganr a kasan ranta tana zabga masa harara."ni kikewa wannan kallon ?tayi shiru tana qoqarin janye jikinta daga nashi “kince na kuwa san yadda kike ji idan ina shan sigari ?kawar da kanta tayi gefe dan bata ma son kallon fuskarsa sai dai ji tayi ya fixgota jikinsa gbdy ta kwanto jikinsa wani irin bugawa zuciyarta tayi ta sauke numfashi tare da tsuke qaramin bakinta tana kallonsa muryarsa can qasan makoshi yace “fada min me kike ji ?"zuciyata na zafi "tayi maganar kmr zatai kuka “amm da ni ina son ki saba daita "akan wani dalili kenan zan saba ?” ni wallahi bana son warinta yana mugun d'aga min hankali bama warinta ba ni d'an sigari ma banason shi a kusa dani "to ya zakiyi dani kenan ?"ya fad'a yana hura hucin numfashi da iskar bakinsa ya qarasa maganar adaidai lokacin da a ruwa yayi magana “yalla’bai mun shigo agege “nan yayi directing dinsa inda zasu sannan ya sake janyo hannuta yana kallo inda ta kona kanta .”






“Karki sake min abinda kikayi min yanzu kalli kiga har kin kona hannunki mutun sam baya abu da tunani yana magana yana hura mata gurin nan take taji ta daina jin rad’ad’i a wajen batare da ‘bata lokaci ba suka iso unguwarsu maryama a ruwa na gama parking maryama ta dauki jakarta tace masa "goodbye sir " yayi murmushi yace "till we meet tomorrow ".da sauri ta bud’e motar ta fita daga motar tana harhada hanya, but she felt as gangar jikina ce ta fito ta bar zuciyata a cikin motar tayi kokarin calming down din zuciyarta kafin ta karasa gida ahankali ta shigo gidansu kai tsye kamar yadda ta saba da part din umma ta fara tayi knowking har sau biyu taji shiru ta kai hannunta da zumar sake knowking taji kofar ta bude "a she ma kofar a bude take ta fad'a tana tura kofar shiga parlour'n babu kowa sai umma ita kadai zaune tayi shiru tana tunanin “lafiya umma ta zauna shiru haka?” tayi mgnr a kasan ranta kana ta tsaya tana kallon hannuta dake nade da bandage tana tunanin ta fad'a mata abinda ya faru yau a office ko tayi shiru kai bai kamata ba hankalinta zai tashi matuka bayan yanzu hankalinta a kwance yake bari mr ata ya gama bincikesa sai na fada mata idan da bukatar haka ta qaraso ta dafata tana kiran sunanta "umma nah ! .”






Umma tayi firgigib ta dawo haiyacinta yace "a'a yaushe kka dawo ban sani ba ?zo ki zauna ki huta kinji diyata ta zagayo daita gabanta ta zaunar daita akan dogon table din dake gabanta tana murmushi "me Ke faruwa ne umma tun jiya na lura bakya cikin farinciki?"meke damunki babu abinda ke damuna kawai dai kaina ke d'an min ciwo umma wannna ba ciwon kai kawai bane akwia abunda ke damunki baki saba boye min komai ba idan kika boye min zanji babu dadi umma dan allah ki fada meke damunki ?nace babu komai bari na kawo miki abinci kici nasan kin gaji dayawa ".umma karki min karya yanzu Kenan bazaki iya fada min damuwarki ba ?Umma ashe zaki iya boyewa diyarki abinda ke damunki ?dan allah ki fada min meke damunki tayi mgnr Kmr zatai kuka "tabbas akwai abinda ke damuna maryama ,mutane basa da amana maryama .”






dana dawo daga ijesha na biya kamfaninmu bread in takaice miki wai dan zaman danayi agida saboda rasuwar sadam ban samu na leka ba idan kika ga barna da gali yayi sai kinyi mamaki nan ta zayyane mata komai da irin matakin data dauka akanshi "tabbas baba yayi kuskure umma daman kuma haka mutane suke kullum cikin Kuskure muke amman kiyi hakuri umma ki bashi wani dama "da wannan damar mutane suke sake kashe mutun kullum ana yi maka ana baka hakuri amman ya zakiyi umma yanuwa ne ki yafe masa umma yanzu wannan matakin da kika dauka akansa idan kika dawo dashi bana tunani zai sake aikata laifin kuma dai kice Kike koyar da na tare dake ,idan mutun yayi maka laifi ka hukunta shi sai kuma ka dawo ka yafe masa “.shike nan na hakura amman saboda ke” maryama ta kwanto jikinta tana murmushin jin dadi tace "na gode sosai umma ina qaunrki .”umma ta shafa gefen fuskata "nima ina sonki maryama "kamar ance ta kalli hannun maryama tace “menene haka a hannunki ?”




Mmn sudais
[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗


BOOK 3


*AYSHA A BAGUDO*


WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim


Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.




Page 31




Zaune ya’yan ummi suke a bangaren hagu da damanta a babban parlour’nta har maryam, inda aunty shahida ta dubi mami tace “mami kince zaki fad’a mana abinda ya faru jiya tsakanin baba qarami da adamcy amman munji shiru gashi har muna shirin tafiya” ke dai shahida bari ,alamarin adamcy sai addua nan mami ta shiga rat ta’bo masu abinda ya faru a yammacin jiya ,murmushin farinciki ne ya bayyana akan fuskar maryam kasancewar tana mugun qaunar halaiyarsa” she really miss his face “a halin da take ciki zaune babu abinda take muradi da kwadayin gani kamar ta d’aura kwayar idanunta akanshi dan tayi mugun kewar fuskarsa da komai nashi ita fa tana ji aranta dan shi kawai take numfashi acikin duniyar nan ,ita fa duk abinda yake mata bai ta’ba rage digo d’aya acikin soyayyr da take masa ba, hassalima sai qaruwa da soyayyarsa take acikin zuciyarta ,haka kuma duk yanayinsa da abubu wansa da yake ma mutane da wanda yake mata bai ta’ba ‘bata mata ran da taji wai zata iya daina son shi ba. duk abinda yayi ma burgeta yake shiyasa tana jin rashin dadi aranta da ba namiji zata haifa masa ba .
dan zata so ta haifa masa yaro mai kama dashi sak da irin halaiyarsa idan ma da hali ya zartashi akomai
mami tana gama qarasa mganrta ta mike tsaye tace dasu tana zuwa ta nufi parlour’nta na biyu ta barsu zaune inda nana hauwa’u ta soma nata bayani daki daki“.“nifa ba hayaniyar da’aka yi jiya tafi komai damuna ba kamar fuskar yarinyar nan da’aka yi presentation daita .”






“Wallahi idan Kunga yadda yaya ya rungume yarinyar nan ajikinsa cike da tsananin kulawa da soyayya sai abun ya firgitaku .jin haka yasa maryam ta d’ago kanta da sauri gabanta na wani irin fad’uwa da matsanancin qarfi ta tsurawa nana hauwa’u eye’s dinta “runguma kuma !”ta tambayi kanta zuciyarta na wani irin tsinkewa da zafi yayinda har lokacin idanunta kyam akan nana hauwa’u gabad’ayansu suka natsu suna sauraron bayanin nana hauwa’u “wallahi aunty shahida wannan yarinyar da wahala ba yarinyar mafarkin yaya bace, kunsan ni na ta’ba ganin zanen hotonta akan table a parlour’nsa amman sau d’aya ne“.ko yanzu kuka gan yarinyar nan ,matukar kun ta’ba ganin zanenta zaku tabbatar da cewar itace yarinyar mafarkinsa ”na shiga ukuna !maryam ta fad’a acikin ranta hankalinta na tashi “tabbas nima na ta’ba ganin zanen hotonta a tsarka wuyansa amman a yanzu gaskiya na manta yadda kamanin fuskar yarinyar take dan cikin tsananin fushi naga hoton alokacin “maryam ta waiga ta kalli aunty shahida qirjinta na bugawa “kallo d’aya zaka wa maryam ka fahimci hankalinta yayi matuqar tashi da jin wannan mummunar labari gabad’aya annurin fuskarta ya d’auke “kada fa maganar sister ta zamo gaskiya yarinyar mafarkinsa ce ?”ai kuwa idan ya tabbatar itace da tata rayuwarta taza qarshe ina zata saka kanta ?”dame zataji ?”tasan shikenan har abada bazata sake rayuwa dashi ba .”babu ita azahiri ma yaki amsarta amatsayin matarsa ina ga ta bayyana ?.”duk tunaninta a yanzu da hope dinta akan cikin jikinta ne jira kawai take ta haifa masa babyn jikinta taga yadda zai yi raact ,zai cigaba da nuna mata qiyayya ne da babynsa ko kuwa zuciyarsa zata saduda ya kar’bi abinda ta haifa masa sai ga wani sabon tashin hankali ya kunno kai .”






“yanzu tunda yarinyar maakaciyarsa ce kamata
yayi mu nemeta muganta a zahiri domin tabbatar da gaskiyar da muke nema kafin musan matakin da zamu d’auka akai ai yadda bai bar maryam ta samu natsuwa da kwanciyar hankali ba wallahil azim shima babu shegiyar yarinyar da zai ji dadin zama daita .”suna cikin tautaunawa suka jiyo sallamarsa wanda yayi aciki kuma itace ta katse masu maganar da suke nan take kowacce ta had’eye maganarta cike da tsoro mai tsanani , ahankali ya qaraso cikin parlour’n ya tsaya ,cike da natsuwa yake dubansu fuskarsa a matukar had’e kamar koda yaushe yayinda maryam take dubansa hankalinta na sake tashi “ kawai tunanin yadda zata ga yarinyar take ji take sam ba abu bane mai yuwu ace mafarkinsa ta bayana ,dan bata ta’ba ganin yadda mafarki irin nasa ya zama gaske ba .”yana tsaye yana dubansu cike da zarginsu kira ya shigo cikin daya daga cikin wayoyinsa.ya d’aga yana amsa kiran mami ta dawo parlour’n ta zauna a inda ta tashi tana dubansa a tsanake "Eh muna bada wa !okay zaku iya had’uwa da ahmed zai yi maku qarin bayani akai alright zan maka text din numbersa “. yana gama fadar haka ya katse kiran "ahankali ya motsa lip’s dinsa mami kawai ya gaisar batare daya sake duban sha shin inda yanuwansa suke zaune suna kallonsa ba bare yayi ma har yayi tunanin gaishesu .” zabiba da nana hauwa’u ne suka gaishesa cike da tsoro ,suma kuma bai amsa ba sai faman cin magani yake dan jikinsa ya bashi maganrsa suke abinda suka kasa fahimta ne kenan shi bazai hanasu suyi magana akanshi ba amman ya tsani yaga suna maganrsa agaban wannan yarinyar maryam dan ganinsa wannan raini ne .”






Kallonsa kawai suka cigaba da yi fuskarshi babu annuri, kullum fuska kamar wanda yake cin fushi aunty Khadija tayi maganar a qasan makoshinta
d’an qaramin tsaki yaja kana ya juya a natse ya nufi step yana taku cike da jin kai da isa suka bisa da kallo kamar su saka kuka dan ‘bacin ran da suka gani a saman fuskarshi yayi mugun d’aga masu hankali “mami ta kallesu d’aya bayan d’aya tace "ya naga duk kunyi wani iri haka ?”wallahi mami bama jin dadin yadda adamcy yake nuna mana ki duba fa kigani mu yayyensa ko kallo

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login