Showing 99001 words to 102000 words out of 178062 words
Chapter 34 - MAR ADAMS BOOK 3 COMPLETE BY AYSHA BAGUDU.txt
ya zuba mata idanunshi “ idan bamuje ba har ta bude taga documents dinka kaga ai ka shiga matsala inda wayata ce kad’ai wannna mai sauki ne “ko wayarki kad’ai ba abu ne mai sauki ba “ya fad’a yana sake shiga tashin hankali “wallahi nadiya kin cika care less dayawa just rike takarda ya zame miki aiki “
“Wani irin careless gareni ?nifa banga dalilin da zai sa ka damu kanka dayawa ba .maryama tana da ilimi da fahimta my heart ka fito ka mata magana a zahirinka,ya kamata tasan komai ka saketa ka nemi ta rufa maka asiri muyi rayuwarmu that’s all idan son samu ne ni ba haka bane araina ya cigaba da kallonta atsanake tana magana da d’agawa “yes ni ba haka bane araina banason boye boye arayuwata nafi son komai forwardstret ka saki maryama kawai sannna ka koma gida idan kace baka son maryama akwai wanda zai maka dole ne ?” numfashin ya sauke kawai yana dubanta “ my heart ya kamata ka furta mata saki .”
“Kinga mu bar maganr nan haka nadiya nemo mana mafuta lallai ya kamata documents dina da wayarki su dawo garemu “nadiya tayi shiru kawai tana dubansa dan ita a halin yanzu rashin sakin maryama ya zame mata qalubali ga rayuwarta zata só kafin suyi aure ya zamanto babu wata halaka atsakaninsu amman ta rasa dalili da yasa yaki sakinta bayan kullum lallabashi take akan ya saketa “.ya mike zai wuceta tayi saurin riko tafin hannunsa cikin nata cak yaja ya tsaya kafin ahankali ya juyo gbdy ya fuskanceta , cike da matsanancin sonshi ta qara taku biyu ta zube jikinsa muryarta cike da rauni tace “my heart ko ka fara son maryama “?numfashinsa ya hau sauke mata a fuska da wuyanta “ka fad’a min idan ka fara sonta ne ni na hakura na bar mata kai ?” tayi mgn a shagwabe kamar zatai kuka hannuwansa duka ya kai ya zagaye kugunta dashi ,inda nadiya ta sake shige masa sosai tana tado masa da sha’awarsa “kema kinsan ke kad’ai zuciyata take so “amman me yasa ka kasa sakin maryama ni so nake naji ka raba kanka da ….bata qarasa mgnr ba taji saukar lips dinsa akan nata alamun tayi shiru “sau nawa zan fad’a miki bata cikin rayuwata ?ba dai saki kike da bukata nayi mata ba ?”ta gyda masa kai tana mai lumshe masa ido “ki kwantar da hankalinki zanyi “.
ai nadiya bata tsaya wata wata ba ta soma sucking din lip’s dinsa ,sun dade suna shan bakin juna kafin ahankali suka tsurawa juna ido “ina sonka my heart. “baki kai ni ba .ni dai nasan nafika sonka.”
kanshi ya girgiza mata yana cewa “kowa nashi ya sani amman ina mutuwar sonki nadiya ke kinsan irin abubuwan da nayi facing kafin mu kasance tare gashi sakacinki yana neman sakamu cikin matsala “in sha allahu my heart bazamu shiga matsala ba .”
sun dade makale da juna suna tsara yadda zasu bi maryama su amshi abubuwansu a hannunta ,”shiru maryama tayi tsaye tana duba screen din wayar kafin ahankali ta sake maidashi cikin durowa ta ajiye “ko me yasa suke son damun rayuwarta haka ?”ta cigaba da zama shiru tana nazarin muryar da taji yanzu wanda shine karo na uku da taji ,yadda zuciyarta ta kasa yarda cewar yaya sadam dinta bai mutu ba yana raye haka ta kasa yarda cewar wannan muryar ba muryarsa bace zuciyarta ma tafi tsaiduwa akan muryarsa ce .ranar dai kowa ya kalli yanayin maryama yasan babu lafiya kuma sai ya tambayeta amsa d’aya take bayarwa shine babu komai yayinda acan bangaren yaya sadam da nadiya abu na farko da suka fara shine trancking din number wayar nadiya domin su san takaimaiman inda maryama take cikin sauki kuwa suka gane inda take sakama kon wayar na kunne har lokacin.”
Maryama ta numfasa daga zaunen da take tana duba agogon hannunta tsaki taja saboda lokacin tashi aiki ya kusa."ahankali ta dafe ha’barta da hannu d’aya ta kalli office din mr ata taga aikinsa kawai yake yana amsa kiran mutane wani tsaki ta sake ja tana cewa “Ko me yasa sai dani zashi ganin abokin kasuwan cinsa byn ga sauran mutane nan ? bayan kamar mituna talatin mutane suka fara watsewa ahankali tana zaune kowa ya wuce har madam some aka barta ita kad’ai zaman jiran mr ata.”
Mr ata ya d’an leko yana cewa maryama “kin shirya ? tace ”yes na shirya !”ta furta muryata a raunane jakarta ta d’auka ta rataya kana tayi hanyar shiga lift sai dai duk ranta a ‘bace yake ,bayan ta wuce ya fito cikin sauri inda ya had’u da wani matashin saurayi goye da kayan aiki na spray din gida da office ,fuskarsa rufe da face mask haka ma ilahirin jikinsa sanye da kayan aikinsu mr ata ya tsaidaishi yana cewa" who are you? "Uhm amm spray control ." "wa ya kiraka ? "wani daga cikin maaikatan office dinka ce ta kirani “suna cikin hk maryama ta d’an dawo baya kad’an tana cewa” sir lokaci na tafiya fa "okay.! ya fad'a ya wuce matashin saurayin “.
Sadam ya ciro wayarsa ya fara duba tracking number a wayrasa kafin ahankali ya shiga cikin wani office ya fara dube dube can aka kirasa a wayarsa "eh nadiya na samu na shiga office din da tracking ya nuna min nayi sa’a babu kowa aciki amman fa kisa ido sosai idan kinga dawowar maryama kiyi maza ki kirani na fito dan banason muyi face to face daita no matter how zata iya ganeni “.ya fad’a tare da katse kiran yana cigaba da bubbud’e durowas din duk wanda ya bude ya duba sai yaga bai ga abinda ya kawosa ba yayi shiru tsaye yana tunani ko ina ta ajiye wayar da document dinsa yasan dai idan bai ga documents din da wayar nadiya anan ba lallai yana cikin jakarta kenan?” Ya rabbi sadam zai sake koma zuwa gidansu kenan ?”inji cewar zuciyarsa “a’a ka sake duba tracking sosai kafin kasan matakin da zaka dauka ,"yana cikin wannan tunanin sai ga daya daga cikin securities ya qaraso yana cewa” who are you looking for?ya juyo a hankali baka ga alamun kayan aiki ajikina ba spray control ne? amman may yasa sai a wannan lokacin zaka zo? " eh ! wacce ta kirani ne tace nazo by this time saboda mutane sun watse ,"Okay shikenan ka cigaba da aikinka “ thank you “!ya fad'a yana sauke numfashi security ya juya shi kuma ya cigaba da aikinsa ,"
ahankali motar mr ATA Ke gudu akan titi shi da kansa yake tuki wanda escort dinsa da direbansa sunyi mamaki da duk inda zashi tukashi akeyi amman a wannan lokacin yace duk suyi zamansu .” ahankali ya kalleta tana zaune a gefensa ta kawar da kanta gefen titi tana kallon motocin dake wucewa
ya dauke kanshi ya maida Kan titi ya cigaba da murza stearing mota yana tunani taya zai rabata da tunanin wannan matacen mutumin ya dasa nashi tunanin a zuciyarta ,dan dai yayi imani tunaninsa take yi ,ya sake waigowa ya kalleta cikin haka wayarsa ta dauki gara mara sauti ya tsaida motar a gefen titi yana amsa kiran bayn ya gama wayar ya kira sunanta a kasalance "maryama !" "yes sir ! ta amsa batare ta kallesa ba , mutumin da zamu hadu dashi yayi cancelling din haduwarmu wani sanyay yen numfashi ta sauke najin dadi tana godiya ga allah ,zata wuce gida da wuri akan lokacin "bari mu juya zuwa office "taso ta roki alfarmar ya sauketa ko a bakin titi ne ta samu mota da zata qarasa daita gida ,amman babu hali tana magana yanzu zai maida maganar bala'i dan haka ta hakura idan ya sauketa a ma'aikatan ta kama gabanta tana jinsa ya juya ya dauki hanyar komawa office.”
ahankali yaya sadam ya cigaba da duba document din a bangare dabam dabam still bai gani ba to yanzu idan banga wayar da file din ba fa ya kenan ? to kuma idan ya zamo yana jakarta fa ko kuma ta bawa wani ajiya fa ?amman bari na cigaba da dubawa ? "madadin mr ata ya tsaya ta sauka a bakin ma'aikatan kai tsaye ya shige ciki daita a haraban kamfani yayi parking ya bude ya fito ya zagaya bangaren da take zaune yana kiran sunanta "maryam.”! alokacin tana daf da qarasa fitowa ta tsaya tare da rungume hannuwanta a qirjinta "yanzu tunda anyi cancelling aikinmu me ya kamata muyi "?me ya kamata muyi kuma ? ta maimaita abinda ya fad'a acikin ranta amman a zahiri kam tayi shiru ta rasa amsar da zata bashi ” ko zamuje office ki had’a min coffe na sha ? “coffe kuma ”! ta furta a fili tana yatsina fuska "eh ko bazakiyi ba ?"
“sorry sir am not in the mood" ta fad’a kamar zatai kuka "meke damunki ?”nayi nayi ki fad'a min abinda Ke damunki ko zaki rage jin damuwar dake damun zuciyarki kinki ,"sir ko zaka fad'a min kai ma dalilinka na “wad’an nan tambayoyin “damuwa da abinda ke damuna ? meye matsalata ?ta tambayesa a zafafe tana juya masa baya " wai ma dole ne sai ka tmbyeni abinda ke damuna da matsalata ."?ta fad’a muryarta na rawa .”
"Bana son jin damuwar kowa kema bansan dalilin da yasa nake son sanin damuwarki ba ,ya tsinci kanshi da fad’a mata haka “ya d’an lashi lips dinsa na kasa kad’an kana ya cigaba da magana “me ma kike tunani akaina dan na tmbyeki damuwarki ? " dole nayi tunanin wani abu ,dan kaine da kanka kace baka bukatar jin matsalar kowa da damuwar kowa kuma kowa yasan wannan yana daga cikin dokokin aikinka to me ysa zakayi ta tambayata akan abinda ya shafi rayuwata ?"dan allah ka barni naji da abinda ke da...."bansan me yasa na tmbyeki ba bare ki samu damar fad'a min rubbish and nonsense ya katseta ta hanyar fadar hk yana fidda numfashi sama sama "me yasa ka tmbyeni to ?”me ma yasa kamin mgn bare har na fad'a maka rubbish and nonsense“
"yadda kaima baka bukatar a shiga rayuwarka nima haka nake bana bukatar ana shiga rayuwata kawai kana son qarawa mutun damuwa akan wanda yake ciki .ta fad'a tana jan tsaki zata wuce taji ta makale ajikin mutun , tayi tayi ta motsa ta kasa sakamakon gefen rigarta daya makale da murfin mota "me kake kokarin yi sir ?me yasa ka rike min riga "what.”? ya furta a razane yana dubanta "naga alamun kana son wuce gona da iri daga ta’ba min jiki yanzu kuma ka dawo rike min riga ko ance maka ni din rin wadan nan mata ne dake banzatar da kansu a gurinka ? .
"ni kike fad’awa haka ?kenan wannan tunanin Kike yi akaina ?okay tunda tunaninki kenan zan san abun yi “ nan take jikinta yayi sanyi tsoro ya kamata yanzu idan ya fusata ya turata wani guri acikin ma'aikatan yayi reping din fa ?nan take wani tsoron ya sake mamayeta ,ta juyo ahankali idanunta ya sauka akan gefen rigarta dake makale ya hade da murfin mota an rufe yayinda mr ATA ke tsaye yana faman fitar da hucin numfashi "ganin ba rike mata riga yayi ba yasa ta shiga tashin hankali mai tsanani muryarta na rawa ta soma bashi hakuri "am very sorry sir karka yi fushi dani dan allah dan har jijiyon kansa sun tashi sunyi rudu rudu saboda bacin rai "idan zakiyi irin wannan hauka ki fara tunani ,ni ba irin wadan mazan bane nonsense kawai ya fad’a yana wuceta "am sorry sir!” me yasa na fad'a masa son raina batare da nayi tunani ba ? Sam sam bai kamata na fad'a masa haka ba tunda babu wanda ya ta'ba fadar wani mugun abu akansa kowa kaji yayi magana akansa sai dai ace shi din miskiline mai kamewa baya shiga harkar mata "dan allah sir kayi hakuri madadin ta wuce gida kamar yadda taso sai ta tsinci kanta da biyosa tana sake bashi hakuri .”
a can kuwa office sake cigaba da dube dube yaya sadam keyi har ya samu nasarar bude durowar qarshen wanda yafi kowa ne wahalar budewa ya shiga duddubawa yana daga wasu file ,duk file din daya gani sai ya bude cikin haka yaci karo da wayar nadiya ya sauke naunayen ajiyar zuciya yana cewa allah na gode maka dan zaman wayar nan a hannun
Maryama zai iya zama matsala a rayuwarsu.”nadiya wacce Ke duba masa waje tana duba masa dawowar maryama taga dawowarsu ita da maryama dan haka cikin tsananin tashin hankali tace "me ya tsaya yi ne haka idan bai ga wayar da file din ba ya fito mana mu wuce kar akama mu, bari nayi sauri na samesa idan bai gani ba mu wuce kawai ."ta shigo da sauri rufe da fuskarta alokacin sadam yana shirin fitowa "idan baka ga file din da wayar ba kazo mu wuce mana me yasa kake bata lokaci ?" Me yasa kika biyoni Ke da nace ki jirani a waje ga waya nagani tasa hannu ta amshi wayar "gsky kayi kokari ina file ?”shi nake kan nema dan shine damuwata amman duk na duba koina ban gani ba.." sautin muryar mr ATA ne ya katsesu da sauri nadiya wacce ta shigo yanzu ta tsugunna ta boye akarkashin table tana sauke numfashi ,shi km yaya sadam da ke tsaye da kayan aikin spray control ya soma kokarin fita daf da zai wuce mr ATA yaji sautin muryarsa"wait!yaya sadam tsaya cak gabansa na luguden bugu dan baya son su had’u da maryama dan kallo d’aya zata masa taganeshi mr ata ya tsaya yana dubansa "are you done?yes sir !” na gama ina sauri ne zani aiki wani guri "okay zaa tura maka kudin aikinka daga asusun kafaninmu zuwa naku “okay sir ya wuce da sauri ya bar nadiya akarkashin table ."
Ganin da nadiya tayi mr ata ya zauna ta fito da sauri ta soma tafiya tana waigen bayanta yayinda maryama Ke tafiya tana magana da zuciyarta kamar yadda tasa ba , daf da nadiya zata fita daga cikin office din ita kuma maryama na qoqarin shiga office din suka ci karo da juna cikin tsarkewar murya maryama ta furta "am sorry !nadiya batai magana ba ta sake rike mayafin data rufe fuskarta dashi gam "excuse me who are you?kina aikina a AGC company ne?”ko kuma kina bukatar wani abu ne ?Shiru nadiya tayi tana qoqarin guduwa .”shi kuwa mr ATA daga inda yake zaune acikin office dinsa ya hangosu tsaye ya tsura masu idanunshi yana kallon dawa maryama take magana ?haka jikin maryama ya bata ta bud’e fuskarta matar taga ko wacece ai kuwa maryama tayi taku biyu tasa hannu zata zame mayafin da nadiya ta rufe fuskarta dashi nan take nadiya tasa hannuwanta duka ta tura maryama da iyakar karfinta maryama ta tafi luuuuu ta fad'a Kan durowar karfe nan take hannunta ya bugu da gefen karfen nan da nan sai jini ya balle "ouch ta saki qara mai sauti sannan ta matso da sauri ta rike hannun nadiya dake rike da kofar shigowa tana qoqarin zare hannunta maryam ta sake damkewa nan suka shiga kokuwa da juna ,har maryama ta samu ta mike tana qoqarin ta zame hannun nadiya ta dake damke da mayafin fuskarta inda wayar dake rike da hannun nadiya ya fadi kasa maryama tabi wayar da kallon mamaki “ai wayar da’akawo mata ne dazu da safe .”
Nadiya ta tsugunna da sauri ta dauka tana mikewa mayafin fuskarta ya zame kafin ta rufe fuskarta tunin maryama tagan fuskarta ,a matukar rikice ta furta sunanta " anifa ! tana rike hannunta dake tsiyayyar da jini wanda adaidai lokacin mr ATA ya soma qoqarin qarasowa inda suke yana kiran “stop !amman ina idanun maryama sun rufewa babu abinda take furtawa sai sunan anifa ki bani wayar nan bazan sakeki ba sai kin bani wayar nan dan bazan bari ki tafi koina ba batare da kin bani wayar nan ba.” ta qarasa mgnr adaidai lokacin da mrs ATA ya qaraso ya rike hannun maryama yana cewa “meye kikeyi haka ko kinyi hauka ne”?” Ka sakar min hannu karka bari ta gudu a matukar fusace ya zare d’ayan hannunta dake rike da nadiya ya hadasu waje daya wanda hakan ya bawa nadiya damar juyawa da sauri maryama ta juyo ta kalli bayan nadiya tana furta "sir sir sir !!! "dan magana ma yaki fitowa daga cikin bakinta tana kokarin fisxgewa daga hannunsa "ke kina hauka ne baki ga jinin a hannunki ba ?ta girgiza masa kai "tana kallon hanyar da nadiya tabi “zakiyi wasa da lafiyarki ne akan shirmen banza ?" rasa yadda zatai dashi yasa kawai ta fashe masa dan wani rikitaccen kuka mai tsananin cin rai tare da zubewa ajikinsa .hannuwansa duka yasa ya tarairayota ya rungumeta tsam ya hadeta da faffafan qirjinsa .”
cikin tsananin tashin hankali ya soma tafiya daita zuwa cikin office dinsa ya zaunar daita akan kujerar hutawarsa ,kuka sosai maryama take tana ciza harshenta da qarfi dan zuciyarta banda zafi alokacin babu abinda take mata “tana son sani me