Showing 168001 words to 171000 words out of 178062 words

Chapter 57 - MAR ADAMS BOOK 3 COMPLETE BY AYSHA BAGUDU.txt

ne dan kina son kiyi aure?” ta gyad’a masa kai tana cewa “eh to bawai ina son shi bane amman zan auresa dan naji ya d’an kwanta min arai nan take moond dinsa ya sake canzawa ya shiga kai kawo a filin office din .”Sosai tai mamaki yadda ya shiga damuwa “kar dai da gaske mr ata sonta yake kamar yadda ta fara tunani kamar yasan tunanin da take kawai taga ya dawo gabanta daf daita ya tsaya yasa hannuwansa ya rike kafad’unta yace “karki ga na shiga wani hali kiyi tunanin Ina yin shishigi ne acikin rayuwarki ,jikina ya bani baki son auren nan kuma banason ki auri wanda baki so kasancewar akwai illa saboda ni nan hakan ta faru dani kuma babu abinda auren ya haifar sai zallar damuwa ki manta da wannan ni ki aureni “






Tayi shiru tana tunani wannan Iko nashi “gaskiya ni dai gara na auresa zai fiyye min kwanciyar hankali akan na aureka shi mutun ne mai sauki hali mai kyakkwan muamula da mutane mutun ne mara girman kai da sanin kimar mutane mutun ne mai…”ai kafin ta qarasa mganrta sai Jin saukar mari tayi akan kuncinta sosai ta firgita ta dafe kuncinta ta tsura masa ido shima ita yake kallo ranshi a matukar’bace hawaye ya zubo mata akan fuska yace “kina hauka ne ko kuma kin fara shaye shaye ne ?”a gabana kike yabon wani katon banza har kike kuranta shi ?bayan ya gama maganar sai kuma yayi shiru ya juya mata baya yana fesar da iska yana duban hannunsa da ya mareta dashi “oh my god why adam ?”me yasa ka mareta?”yana cikin wannan halin yaji motsin takalmanta alamun zata bar office din juyowa yayi da sauri ya rungumeta tsam tsam ajikinsa gabansa na fad’uwa nan take jikinta ya d’auki kyarma amman ta kasa kwacewa yadda yake ji ajikinsa haka take ji ajikinta kamar an jona mata wutar lantarki cikin sanyi murya yake magana “ki fahimceni maryama banason ki aure wani ,ba wai Ina nufin karki yi aure bane a’a banason ki auri wanda bakya so ne .”




Wani haushi da bakinciki ya dinga shigarta yana mamaye ilahirin jikinta domin alokacin tayi tunanin zai ce mata shi yana sonta ne dan tafi son ya furta mata cewar yana sonta ba wai ta auresa batare da tasan matsa yinta ba kuma tayi Imani idan ta auresa a haka duk ranar data bata masa rai kai tsaye zai wulaqantata .wani haushi ya sake kamata sbd bai ce yana sonta ba ya wani rungumeta yana faman sauke ajiyar zuciya tamkar jinjirin daya kwana uku batare daya sha nono ba tana fama da radadin marin da yayi mata da rashin furta mata yana sonta bare ta samu damar aurensa ,ya wani rungumeta yana mata maganar banzar ko ina ruwan shi da zata auri wanda bata so oho ?”




ahankali ta soma mutsu mutsun kwacewa ya juyo daita suka fuskanci juna ya sake matseta yayi mata kyakkywan riko yana cewa“haba maryama me yasa kike jin cewar zaki iya auren wani ki bar ni “zan fi samun natsuwa da kwanciyar hankali ta bashi amsa da haka tana sheshekar kuka “bazaki samu ba maryama bazaki iya rayuwa da wani ba ke har yanzu baki fara Jin alamun cewar kina son adam ba ?”wannan kam gakiya ne ta fara Jin son shi har ma tana jin cewar bazata iya kwanaki dayawa batare datayi magana dashi ba domin duk yadda yake mata kallon tana son shi ashe abun da gaske ne lallai zuciyarta ta tafka mata babban kuskure domin dai son shine kuskure na farko da zatayi arayuwarta.”




“Ya zareta ajikinsa ya riko hannunta cikin nashi yana murzawa ahankali yace “maryama me yasa bakya tausayawa kanki ?”tayi saurin zare hannunta daga nashi tana yarfarwa kamar wanda wuta ta kona saboda wani blood rush da taji ya taso mata daga hannunsa zuwa nata cikin second d’aya ya zagaye duk ilahirin jikinta cikin tsarke war murya tace “me ya sameni da zanji tausayin kaina?”sannan dan nace zan auri wani ne yasa ka mareni ?”ya lumshe mata idanunshi ya bud’e yana kallon yadda take yarfe hannunta tace to “nasan kana da komai da duk wata mace zata so aurenka amman ni maryama bazan aurenka kuma kome zakayi gara na auri wani akan dai na auri mutun irinka “ bai san sanda dariya ya subuce masa ba, ..ya mugun tsareta da ido sannan yace “kamar zaki iya!” ta d’an tsaya tana kallonsa Tana assessing maganarsa yana kallonta with a broad smile akan fuskashi ta d’auke kanta tana lissafi “kamar fa ya gane ta fara son shi idan kuma bai gane ba tabbas cigaba da tsuyuwarta a wajen zai iya tona asirin zuciyarta bugu da qari ga tsayuwa na neman gagararta dan haka ta juya ahankali zata bar masa offie din taji ya riko tsintsiyar hannunta tare da fixgota zuwa jikinsa ya rungumeta yana jin wata irin tsantsar soyayyarta na ratsashi “






“Ina zaki ?”gida zan wuce !”kuma in sha Allahu daga yau bazan sake ta kowa inda kake ba dan baka you’re so wicked shiru yayi yana shafata kafin ahankali ya cigaba da mgn “gobe ne fa asirin wanda ya fitar da hadad’dun hotunamu zai tono ko bakya son kisan ko waye ?”ya fad’a tare da sausauta rikon da yayi mata zuciyarta na matukar zafi ta tsura masa ido tare da alamun son ya mata qarin bayani ajiyar zuciya ya sauke nan ya kwashe yadda akayi bincike komai ya fad’a mata “waye wanda ya fitar da hotunan?”zaki sani a gobe ta sauke numfashi tace “to sakar min jikina kuma dan Allah wannan yazamo karo na qarshe da zaka kai hannuka jikina “ba jikinki ba hatta komai naki nawa ne kuma ke baki isa ki hanani ta’ba wa ba “ni kam wannan abu ya fara damuna idan kana sona ne ka fito ka fad’a min tai mgnr tana harararsa “baza’a fada ba !ya qarasa maganar ahankali yana had’e fuskarsu waje yana qoqarin kamo lip’s dinta, tayi saurin kawar da fuskarsa gefe tana cewa “bana so abinda kake min kana sa Ina cin raina dayawa
Ina jin nadamar aiki a kamfanin AGC wallahi if Ina son naga wanda ya d’auke mu hoto da har abada bazaka sake sanyani acikin idanunka ba
ga ta’ba min jiki da kake yi ga rashin so ga mari.”




sarai ya fahimci abu biyu din nan sun fi bata mata rai ba wai ta’ba mata jiki ba ,rashin bai furta mata yana sonta ba da kuma marin da yayi mata yayi kasa da muryarsa sosai “kina son na furta miki kalmar so ne kafin ki amince ki aureni ?”tayi shiru tana kallonsa ,ya sauke mata numfashinsa a fuska ya cigaba da magana “ko kuwa kina son na baki hakurin marin da na miki ne ?wad’an nan maganganun d’aya fad’a mata ba iya cikin kwakwaluwarta da zuciyarta suka tsaya ba har ilahirin jikinta take jin tafiyarsu zata so ya aikata abu biyu din nan ,furta mata yana sonta da kuma bata hakuri “naga alamun kina bukatar hakan sai dai kuma bazan yi ko d’aya aciki ba idan zaki aureni a yadda nace fine idan bazakiyi na leave my office “ ya fad’a yana sakar mata jiki ya zagayeta ya nufi wajen zamansa.”






Idan ta fahimcesa so yake ya nuna mata qarfin Iko bayn yayi nasarar tursasa zuciyarta da gangar jikinta sun fara jin wani abu akan shi ,ya fara koyar daita soyayyarsa ,to ko dai zata amincewa aurensa ne kamr yadda ya bukata ?kai Ina bazata iya wannan kasadar ba domin auren irinsa babu abinda mutun zai tsinta aciki sai zallar damuwa ta kasa motsa gangar jikinta tana shawara da zuciyarta bata jin zata sake d’aukar dogon lokaci tana aiki dashi yana zaune zai ji ta auri wani irin kallon da take masa ya fahimci kallon mugu azzalamu take masa haka nan yaji babu dadi aransa jiki a sanyaye ta juya ta fice daga office din tana jin tarin damuwa bayanta yabi da kallo yana hura hanci tare da lumshe idanunshi bayan wasu mintuna talatin da fitartata daga office dinsa ya hango fitowarta tana goge idanuta ta nufi hanyar sauka qasa aranshi yace sarkin yan kuka ranshi bai masa dadi ba yaji kamar ya tashi ya bita ya dawo daita sai kuma yaga gara kawai ya barta wuce .”








Tunda maryama ta koma gida ta rasa meke mata dadi ,ka kasa sakewa da zarar ta tuno kamaninsa sai gabanta ya yanke ya fad’i “ya ilahi kanta ta sunkuyar kan daks din daikinta tana addua acikin zuciyarta dan ta rasa me yake mata dadi ,Ina ma batasan shi ba ,Ina ma aiki bai had’ata dashi ba haka dai tayita tunani tana addua kar Allah yasa son shi yayi tasiri a zuciyarta, da adduar Allah ya cire mata tunaninsa cikin zuciyarta suku suku ta qarasa wuni umma ta lura da yanayinta amman ta share ta dan kota tambayeta tasan zatace mata babu komai qarfe takwas da wasu mintuna na dare tana kwance akan katifarta taji shigowar sako wayarta nan take ta soma qoqarin dubawa taga sakon daga mr ata ne da sauri ta shiga ta soma dubawa .”




“Slm how are you doing ?I just want to apologize for what happened today I’m sorry for today I’m not a wicked man has you think and I’m not a bad person I’m so sorry I’m not intention to hurt you please kizo gobe koda shine zai zamo zuwanki na qarshe .”


Wani irin sanyayyen ajiyar zuciya ta sauke tana sake karanta sakon tana jin wani sanyi na ratsa ilahirin jikinta sai dai tayi shiru tana tunanin amsar da zata tura masa ta d’auki sama da wasu mintuna talatin a qarshe ta tura masa “is okay “Tana gama tura masa ya kirata har missed call hudu bata d’aga ba dan bata son ya sake dasa mata abinda zai dameta wanda take ji ma akanshi zatayi iyakar qoqarin ta ta raba kanta dashi bazata ta’ba yarda sonshi tayi tasiri ba .”


*****


Washegari Wanda ya kama ranar laraba da kusan jiya maryama tazo aiki tana zaune tana aikin zane tana daddaga littafai tana dubawa sai ga yusura ta shigo ta qaraso kusa daita ta tsaya tana cewa maryama ina son muyi wata magana dake dan nayi tunanin nazo gida na sameki amman kunyar haka yasa na kasa zuwa maryama ta bar abinda take tare da mikewa tsaye tana fuskartata ina jinki yusura
“dan Allah Kiyi hakuri” hakuri kuma wani hakuri ai tunda mr ata yace kubani hakuri km kin bani hakuri komai ya wuce araina ,nasani ina sake baki hakuri ne saboda ban kyauta ba domin idan kowa yayi zarginki ni bai kamata ba kasamcewar tare muka taso ki yafe min karki tsaneni dan Allah “kai haba yusura wallahi babu komai nasan qauna ce tasa haka duk mai sonka shine zai ga kayi wani abun batancin ya nuna damuwarsa wallahi babu komai komai ya wuce ni dake qawaye ne kuma wannan matsalar bazata rabamu ba ,”haka ne maryama ta fad’a tana rungumota jikinta ta sausata rungumar datai mata tana cewa amman idan bazaki damu ba mai yasa kukayi wannan hotunan?” mukayi ko akayi mana?” to waye wanda ya iya munafurci haka ?”wallahi yusura ban sani ba kuma har yanzu nan da nake tsaye a gabanki ina wannan tunanin amman mr ata jiya ya tabbatar min an gama bincike” nifa tunanin yan gidanku dan wallahi idan gidanku suka gani akwai damuwa gara duk ma’aikatan kowa yasani akan mutanen gidanku .”




“ai tunin an wuce gurin dan sun gani shine ma dalilin rashin zuwana aiki kwana biyu sai da mr ata da wani abokinsa kukaje gida suka bada hakuri sukai masu bayani dalilin da yasa hakan ta faru yanzu dai komai ya wuce yanzu haka ban jima da fitowa daga office dinsa ba kuma yace zuwa anjima za’a kar’bi wayar kowa dake office din nan ,duk maganar da maryama take acikin kunnen sultana tayisa daga office dinsa ya hango maryama tana magana da yusura abayansu kuma sultana ce tsaye tana sauraronsu tana zance zuci “ina ai bazan bari ya duba wyata ba kafin ma ya duba na goge komai , sosai yake kallonsu ta cikin glass sai dai idanunshi kyam akan sultana yake yana nazarinta yana kallonta ta juya da sauri yayinda shi kuma ya cigaba da juyi akan kujera kai tsaye wani office dabam sultana ta shiga ta fad’a bayi jikinta na rawa ta shiga photos dinta tana cikin neman hotunan taji ya fixge wayar a hannunta yana cewa “me kikeyi anan ?




Mmn sudais
[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗


BOOK 3


*AYSHA A BAGUDO*


WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim


Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.






48


saurin d’auke numfashi sultana tayi tana dubansa fuskarta da bayyananen tsoro tace “uhmm amm babu komai kawai ina son goge wasu tsofafin hotuna ne acikin wayata “tsuma mmun idanunshi ya zuba mata yana mata wani irin wulakantaccen kallo mai razanarwa”lallai ma yarinyar nan tana da matuqar rainin hankali kenan har yanzu bata ma san waye shi ba ?“tsofaffin hotunanki zaki goge ?”ya fad’a yana kallon wayarta dake rike a hannunsa“eh tsofafin hotuna nake son na goge dan wayar tana hanging da alamun hotuna ne suka masa yawa.“
“kin tabbatar?”tayi saurin gyad’a masa kai alamun “eh!”jikinta na wani irin shaking alamun rashin gasky tana jin kamar ta fixge wayar daga hannunsa sai dai babu dama aikata hakan dan ko giyar meye akanta bata isa ba,bama zata fara gwadawa ba “.




“maryama !”
Ya kira sunanta tare da lasar lip’s dinsa na qasa “yes sir !”ta amsa masa cike da girmamawa tana kallonsa” ungo wayar nan ki duba min hotunan dake cikin har recently deleted ”yayi taku biyu ya qaraso inda maryama take tsaye ya mika mata wayar .”maryama tasa hannunta ta amsa ta shiga daddanawa tana dubawa ,shi kuma yayi shiru tsaye yana kallon sultana wacce hankalinta yayi matukar tashi fiyye da tunanin mai karatu”.
muryar maryama na rawa tace “ga..”gasu nan sir! “ga hotunanmu nan acikin wayar sultana wanda ke nuna alamun da wannan wayar aka fara d’aukarmu “nan take gaban sultana ya bada wani irin dum jikinta ya cigaba da kyarmar da yake mr ata ya kar’bi wayar a hannun maryama yana duba wa” ai nasani nasan itace.”




maryama ta d’ago kanta da sauri ta kallesa “na dade da sanin itace nayi haka ne kawai dan na kamata da hujja “.yayi maganar yana dawo wa kusa da sultana ya tsaya ji kake tass tass!! ya d’auketa da wasu gigitattun mari har biyu ajere wanda yayi sanadiyyar da numfashin maryama ya tsayawa cak, ya daina bugawa tare da dafe kuncinta tamkar itace ta sha marin dan tasan zafin marinsa yaso qara mata wani marin sai dai ganin maryama na shirin fad’uwa ne ya rikota cikin zafin nama ya makaleta da jikinsa hankalin maryama yayi mugun tashi ta kwanta lamo ajikinsa tana kyarma numfashi ya fesar ta hancinsa sannan ya kai bakinsa daidai saitin kunnenta yana mata magana .”






halin da sultana ta shiga kafin ta dawo haiyacinta kuwa Allah ne kad’ai masani , ta wani zuba masu ido ganin yadda yanayin adamcy ya canza duk ya wani susuce akanta yana shafa kanta zuwa bayanta kamar wata jinjira yayinda bakinta yake motsawa ahankali ahankali “kayi hakuri karka sake marinta “tayi magan cikin tsananin tashin hankali ,bakinciki ne ya tokare ma sultana kahon zuciya wanda yasa hawaye ya fara zuba daga idanunta tunda take arayuwarta ba’a ta’ba tozartata irin na yau ba“mari kuma agaban maryama?mr ata ya maida kallonsa ga sultana yana hura hanci “this is your last warning sultan if I ever seen you do something like this wallahi zan kasheki da hanuna dan babu wanda zai min irin wannan tozarcin na kyalesa.”




“Kuma karki d’auka dangantakar dake tsakaninmu na duba”no ban duba wannnan halakar ba, kuma daman Kinsan bazan ta’ba duba wannan danganta kar ba, abinda na duba ke ma’aikaciya ce acikin wannan kamfanin kuma dokar ma’aikata shine idan an kama mutun da laifi za’a fara bashi warning tare da dakatarwa “.
yana gama fad’ar haka ya mika mata wayar ya tsaida idanushi akan maryama wacce ke kwance ajikinsa ya sake kai bakinsa daidai saitin kunnenta“malama ai sai ki tashi ko dan kin lafe.”
ya fad’a tare da qoqarin d’agota daga yadda ta kwanta ajikinsa da sauri ta qarasa barin jikinsa ta koma gefe guda ta tsaya tana cewa “ I’m very sorry sir bansan ya’akayi na kwanta ajikinka ba .”sultana kuwa ranta a matukar ‘bace take kallonta batasan adadin tsanar da takewa maryama ba ita dai tasan tsanace irin wacce take jin zata iya rabata da duniyar gabad’aya.”




“Ya adam you slapped me in front of this useless girl “?zaki ‘bace anan ne ko sai na qara miki nonsense kawai and kuma na dakatar dake zuwa aiki karki kuskura na d’aura kwayar idanuna akanki da sunan kinzo “ maryama muje ya tasa maryama gaba suka fice daga office din suka bar sultana tsaye cikin quna rai da ‘bacin rai .”kai tsaye office dinsa ya shige inda maryama take biye dashi abaya ya zauna a mazauninsa tare da tsura mata ido yana kallonta”.muryarta a sanyaye tace “na gode sosai sir duk da nasan kai din mutun ne da baka son ana yawon maka godiya akan abu amman dai dole zan gode maka thank you so much mr ATA ban cin kai ni nasan bazan ta’ba gano wannan gaskiyar ba a karo na biyu ka sake zama silar yaye duk wata damuwata” .”






Tunda ta soma magana ya tsurawa bakinta ido yana kallo yana Jin kamar ya Kai bakinsa ya tsosa ,sai dai har tai shiru

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login