Showing 132001 words to 135000 words out of 178062 words
Chapter 45 - MAR ADAMS BOOK 3 COMPLETE BY AYSHA BAGUDU.txt
wani matsugune acikinta har bakin get din gidansu ya rakota sai daya ga shigarta sannan ya juya ya wuce gida .”
Ahankali ya shigo parlour mami ya ajiye yar saman suit dinsa akan hannun kujera idanunshi na kan mami dake tsaye ta d’ago ta kallesa a natse kafin ahankali ta qaraso zuwa inda yake ta tsaya tana tambayarsa”lafiyarka meke faruwa na ganka haka ?”shiru yayi kawai yana hura hanci tasan halinsa a duk sanda yayi haka baya bukatar acigaba da damunsa akan abu “ ka qarasa d’akin ka kayi wanka kazo kaci abinci kanshi kawai ya gyada sannan ahankali ya zagayeta ya haye sama bayan wasu mintuna mami taji shiru bai sauko ba ta nufi dakinsa a zaune ta iskeshi shiru cikin yanayi na tsananin tunani ta zauna kusa dashi “wai meke damunka ne “?ta tamabyesa cike da kulawa “babu abinda ke damuna sweetheart ko kina tunanin akwai abinda zan iya boyewa kyakkywar mahaifiyata ?”harara shi tayi tana cewa ”akwai mana sau nawa ina tambayarka abu kace min babu komai alhalin kuma ni nasan da komai din .”shiru yayi batare da yace uffan ba “nifa nasan halin d’ana,nasan yanayinsa kuma nasan yanayin damuwarsa kawai dai ka fad’a min “ya kamo yatsun hannunta cikin nashi yana cewa “babu komai sweetheart just believe me, I can’t believe you adamcy amman dai me kake son kaci muna da rice and stew da farfesun kan rago muna da tuwon semoveter da miyar danyar kubewa da cat fish, muna da light soup daakayi mix dinsa da kan rago da kayan ciki da busashen kifi muna da ..” sweetheart alkubus zanci .”
“ alkubus zaka ci bayan shekaru masu yawa rabon daka ci “?“yes shi zanci sweetheart ya fad’a yana lunshe mata tsumammun idanunshi shiru tayi kawai tana kallonsa ,kin bude idanunshi yayi saboda gabadaya jinsa yake acikin wani iri yanayin kamar ya yi kuka ko ya samu salama a zuciyarsa da Kyar ya bude idanunshi sakamakon jin shirun mami “kiyi hakuri sweetheart nasan bazan samu ba “babu wannan ranar da d’ana zai ce ga abinda zai ci ni kuma na kasa masa tayi maganar kamar zatai kuka “na dade ina expecting haka kullum burina naji kace zakaci abinci da mahaifinka yafi so shiyasa naji maganar wani iri”bari naje nayi maka just ka bani lokaci kad’an yanzu zanje nayi maka alkubus “ ta mike ta fita da sauri tana goge gutun hawayen daya cika gefen idanunta.”
“Kai umma qamshi allubus din ya cika koina agidan nan ,da gaske maryma?allah kuwa barin ma qamshin miyar maza maza kije kiyi fresh up kizo kici tun kafin yayi sanyi “okay umma ta fad’a tare da nufar hanyar dakinta da sauri .” bangaren mr ata zaune suke shi da mami akan gado tana bashi alkubus abaki “sweetheart !”bata amsa ba ta tsaya tana kallonsa me kike tunani haka ?”ina tunanin wasu abubuwa da suka gabata ne sannna kuma ina kallon kyakkywan d’ana .”sweetheart ki daina dogon tunani haka kinji kin rasa abba amman kuma kina damu biyar ina son ganinki cikin farinciki’ “uhm ta furta a kasan ranta sannan ta soma mgn “kana son ganina cikin farinciki amman zuciyarka ta kasa amsar zabina kuma farin cikina ?”tayi maganar cike da rauni ina tsananin jin tausayin maryam” yanzu haka nata rayuwar zai kare cikin rashin jin dadin rayuwa?mai yasa adam?ni abinda nake so kuma yafi komai mahimanci arayuwata shine ka yarda ka kuma amince da cewar cikin jikinta naka ne kuma zaka so shi kamar yadda naka uban ya soka ya kuma nuna maka gata ,ina son naga murmu shi akan fuskar maryam I just want to see the smile on her face .”shiru yayi yana kallonta kafin ahankali ya motsa lips dinsa “sweetheart kin kasa fahimtar zuciyar adamcy dinki abinda bazai ta’ba yuwa bane is not possible na amince …”
Cak zuciyar mami ta tsaya ta daina bugawa yadda ya kamata tare da zuba masa idanunta” ki rabu da damuwar yarinyar nan kawai ta girbi abinda ta shuka dan Allah sweetheart ki bar min maganarta ,ki barni a yadda na tsaida zuciyata shiru ne ya biyo baya kafin ahankali ta cigaba da motsa labbanta “batun wacan yarinyar fa ?”yayi shiru kawai yana dubanta fuskarsa da alamun tambaya “wacan yarinyar data shigo rayuwarka nake nufi ko ..”ko itama bazaka ce wani abu akanta ba ka kawo min ita ni zan fad’a mata cewar kana sonta kuma nasan zata fahimceni ina son naga ka zama cikakken mutun adamcy duk da kai baka bin umarnina ni zan maka komai amatsayina na uwa zan baka farinciki daka qasa bani saboda tsnanin son da nake maka ta qarasa maganar kamar zatai kuka “tunda naji zuciyata tana son ganin yarinyar tabbas rayuwar adamcy nace .”shiru yayi kawai tare da zuba mata idanunshi yana shafa fuskashi da tafin hannunsa yana tunain maganganun maryama wanda har lokacin zuciyarta tana ga wani ,gabansa ne ya dinga bugawa da qarfi “sweetheart karki damu maryama zatazo ta ganki “
Mmn Sudais
[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
39
Ahankali ATA yake kallonta cike da tsananin shaukin qaunarta yayinda cike da yanayi na tsananin damuwa yaga ta janyo gefen mayafinta tana goge hawayen dake fita daga cikin kwarnin idanunta ganin hawaye take zubarwa hakan ya sake kunno wutar damuwarsa”oh my goodness god !”yanzu menene abun kuka kuma ?” ya furta a fili yana mai runtse tsumammun idanunshi tare da Jin wani irin tausayinta na ratsa tsantsar jikinsa “why zanji tausayinta bayan ni ne abun tausayi? ya furta yana jan tsaki sannan ya Kai hannunsa ya dafe saman goshinsa yana murzawa yana jin wani irin zafi da ciwo yayinda zuciyarsa ta dinga tuttukin bakinciki”why maryama!”? “mai yasa baza ki fahimci irin zunzu runtun qaunar da nake miki ba?”kusan minti shabiyar yana tsaye zuciyarsa na jin rad’adin azabar rashin son data furta masa yanzu, kafin ahankali ya bud’e idanunshi ya tsura mata daga inda yake har lokacin tana zaune tana janyo numfashi da kyar.”yayi shiru tare da tura hannuwansa duka cikin aljihun wondonsa yana taku acikin office din ,wani tunani yayi dan haka nan take ya soma taku ahankali ya qaraso zuwa bakin kofar office dinsu ya tsaya tare da rike kugunsa yayinda kwayar idanunshi ke yawo a sansar jikinta ”
“qamshin turarensa daya kawowa hancinta ziyara ne yasa ta sauke wani naunauyen ajiyar zuciya ,sai dai ta qara sunkuyar da kanta qasa tana kallonsa tsaye a bakin kofar shigowa shi bai shigo ciki ba shi bai juya ya wuce ba, wanda hakan yayi sanadiyyar da gaban ta ya dinga dokawa da qarfi gefe guda kuma ta dinga jin wani sabon tashin hankali from know where yana shigarta.” ahankali take hango tahowarsa zuwa inda take zaune gabanta ne ya cigaba da lugud’en bugu tana zaune har ya iso inda take ya tsaya kyam yana kallonta tamkar ranar ya fara ganinta .”
d’ago kanta tayi tana mai mikewa tsaye da sauri tare da goge hawayen idanunta ,bai ce mata uffan ba illa tsumammun idanunshi daya zuba mata tamkar zai cinyeta wanda yasa nan take numfashinta ya dinga sauka da sauri sauri ta tsarke yatsun hannunta cikin juna tana sake jin mummunar fad’uwar gaba mai tsanani, bata san dalili ba amman kwata kwata bata son ganin yanayinsa haka domin yanayi ne dake matukar d’aga mata hankali da tsorata zuciya da gangar jikinta.”
tsurawa juna ido sukai na second goma kafin ahankali ata ya janye kwayar idanunshi akanta yana mai shafa sumar kanshi ,wani abu yaji yana tsarga masa tun daga tsakiyar kanshi har zuwa yatsun qafafun sa,ganin har loakcin kuka take wanda shi aganinsa shi ya kamaci yayi mata kuka saka makon mahaukacin soyayyarta dake huda duk wani sansar na jikinsa .”cikin wani irin sauri zuciyarsa yake bugawa kamar zata fito daga cikin qirjinsa nan take tausayin kanshi ya kama shi bai san sanda ya buga mata wani razanannen tsawa tare da furta “enough maryama !” nan take kukan da take ya tsaya cak sai shesheka “bana son jin sautin sheshekar kukan !”nan take shima ta had’iye jikinta na wani irin rawa, yanayinsa ya qara mata jin tsorasa “. matsota yayi sosai sukai mugun daf da juna da sauri ta d’auke numfa shi ,da zai qara taku guda tak to lallai zasu had’e cikin juna “maryama !”ya kira sunanta cikin wata irin kasalalliyar murya mai matuqar ratsa zuciya “kasa amsawa tayi ila ta kame jikinta waje d’aya tana mai sake sunkuyar da kanta had’e da tattaro jarumta ta sanyawa jikinta“I don’t want to see your tears .”da sauri ta d’ago kanta ,a natse ta zuba masa shayayyun idanunta still akwai ruwan hawaye acikinsu “ki goge hawayen nan ki kuma saki fuskarki .” ido cikin ido take kallonta ko kifta idanunta batayi,shima bangaresna kallonta yake yana faman busa mata hucin numfashinsa.”
Ta dinga jin kamar ta barshi ta kama gabanta amman kuma Tana tsananin jin tsoron abinda zai biyo baya dan a kallon da take masa zai iya aikata komai “smile !” ta jiyo fitowar sautin daga bakinsa.a d’an rikice take kallonsa batare da tayi abinda ya bukata ba “nace kiyi dariya”! Dan banason ganin wannan yanayin akan fuskarki “gaba daya maryama ta rud’e ta gigice tana kallonsa da sabon mamaki akan fuskarta “nace kiyi dariya !”wannan karon a fusace yayi maganar batasan sanda ta soma murmushin yake ba wanda ya bayyana d’an murmushin a saman lebbansa yayinda idanunshi ke kanta .”
Ganin irin kallon da yake mata yasa ta janye jikinta tana cigaba da murmushin data saka masa sunah “gashi karka kasheni a natse tabi gefensa ta wuce tana taku a natse ,ya tsura ma bayanta ido yana kallonta tana taku ahankali ,wani naunauyen ajiyar zuciya ya sauke kai tsaye office dinsa ta nufa ta duka ta d’auki jakarta ta fito ta nufi hanyar fita, tafiya kad’an tayi ya juyo taga ita yake kallo ido cikin ido suke kallon juna sannan ta
Sake juyawa” mai yasa nasa tayi dariya ?”nasa tayi dariya dan na daina jin damuwa acikin raina amman har yanzu ban daina jin abinda nake ji ba mai kuma zanyi na samu natsuwar zuciya? Ina son naji farinciki amman kuma na rasa samun wannan farinciki what do I want?”ya furta a fili yana Jan tsaki Allah yasa kar yarinyar ta kasheni !ta kasheka ko dai ka kashe kanka da kanka,haka kawai ka zauna kana cutar da kanka a banza numfashi ya sauke da qarfi ya samu waje ya akan kujera ya zauna yana kallon hanyar data bi.”
Ahankali aunty hassana ta fito daga cikin d’akin umma hannunta rike da takardar gidan biredi,adaidai lokacin umma ta shigo dan dama ba fita tayi ba d’akin yaya sadam ta shiga da sauri aunty hasana ta zauna akan kujera tana tura takarda qarqashinta tasa hannunta ta dafe goshinta ,umma ta tsaya tana kallonta kafin ahankali ta qaraso tana cewa“lafiya hasana meke damunki ?wallahi kaina ke min wani irin ciwo shigowa nayi ko zan samu magani a wajenki “okay bari na duba miki ko zaa samu magani wayyo allah kaina kamar zai cire ,umma ta nufi d’akinta da d’an saurinta cikin kankanin lokaci umma ta fito ta tsaya gabanta tana cewa”kar’bi ki sha .” aunty hassana tasa hannun ta amsa tana sauke numfashi da kyar tace “na gode aunty tana qoqarin kai magani bakinta taji umma tace “ki sha maganin idan kin gama sha ki tashi na d’auki takardar da kika saka qarqashinnki.” a matukar tsorace aunty hasana ta tsurawa Umma ido tana kallonta gabanta na faduwa “ki sha maganin ba kanki ke ciwo ba ?
Aunty hassana tai shiru cikin tsananin tashin hankali “idan bazaki sha ba ki mike na d’auki takardar” jikinta a sanyaye ta mike tsaye sai ga takardun gidan biredinsu ,umma tasa hannu ta d’auka “yanzu dake za’a had’a baki a cuceni na yarda na amince dake amman da irin abinda zaki saka min kenan ? kije ke da allah amman karki sake shigowa zuwa inda nake na rantse da ..”da sauri aunty hasaana ta zube kasa tana kuka tun kafin umma ta ida maganarta “dan girman Allah aunty Kiyi hakuri wallahi ba halina bane yaya gali ne ya turo ne ,ki yafe min wallahi bazan sake ba ,ai baki ta’ba kamani da irin wannan halin ba ko tunda muke dake kin ta’ba neman wani abu naki kin rasa?”wannan ma sausauyi ne ,ki yafe min idan kika sake kamani da laifi makamancinsa na yarda ki dauki duk matakin da kika ga dama numfashi umma ta sauke batare da tace komai inda aunty hassana tayita mata kuka tana mata magiya da kyar dai ta samu umma tace ta tashi taje zatai tunani jiki a sanyayye aunty hassana ta mike tsaye ta nufi kofar fita zuciyarta cike da nadamar abinda ta aikata.”
A matuqar gajiye maryama ta shigo bangaren umma bakinta d’auke da sallama sai dai falon shiru babu alamun kowa dan ta shiga d’akin umma bata ganta ba ,sai dai jin alamun saukar ruwa abayi ta fahimci tana ciki ta fito ta shige d’akinta tai wanka tare da yin sallah bayan ta idan ta d’auki wani littafi tana dubawa sai dai ta kasa fahimtar komai ,dan madadin ta fahimci abinda ke cikin littafi sai ma ta shiga nazarin maganar madam some da kuma mganar mr ata da yayi mata a shekanjiya da kuma abinda ya faru a wannin da suka gabata “uhm !ta sauke numfashi da karfi tana cewa “madam some kenan gsky tunaninki akaina sam bai yi ba ta ina zan fara kai kaina cikin halaka ,ni ko sona mr ata yake koni na kamu da sonshi ai sai nasa wuka na raba tsakaninmu bare babu dayan biyu ta fad’a tana sauke numfashi tana zaune ta jiyo sautin muryar umma tana kiran sunanta “maryama! na’am umma ta amsa tare da fitowa ta sameta zaune a natse ta gaishe da umma yayinda umma ta riko hannun maryama tana dubanta kafin ahankali ta mike tsaye tare daita suka shige dakin umma , maryama ta zauna a bakin gado tana duban fuskar umma yayinda umman ta dawo kusa daita tana kallonta tare da dafata tana cewa “ya mai gidanki “yana lafiya da matsalo linsa , umma ban fad’a miki bane ya bawa kowa kyautar mota amman ni ya hanani amman ni bai dameni ba ina neman taimkon Allah ne umma tai shiru tana sauraron maryma har sanda ta dasa aya sannan tace “ amman dai gsky bai kyauta ba ,uhm umma manta da wannan mutumin kullmu maganrsa I don’t like bad behavior in this company ga tarin wulakantani da yake “.
“kawai fa taimako yayi min nayi qoqarin yi masa godiya amamn umma kinga uban wulakancin da mutumin nan yayi min sai kin tausaya min umma tai murmu shi irin nasu na manya kana tace “ai tunda yana iya taimako ai yana da kirki kad’an maryama ta yatsina fuska “ shifa abinda na fahimta yana da miskilanci tare da tarin wulaqanci kuma baya bukatar yayi maka abu kayi masa godiya”banda abunsa to meye acikin kayi ma mutun abu yayi maka godiya .”ni dai abinda zan fad’a miki shine kibi komai ahankali karki zake daywa ,idan mutun yana da irin wannan dabiar kana sanin yadda zaka tafiyar dashi ne,ki kula sosai kiyi duk abinda yake so kinji maryamata” naji umma in sha allahu na gode sosai yauwa diyar albarka allah yayi miki albarka ta amsa da “Ameen.
Mami ce zaune tare da yaranta mata uku aunty shahida,khadija da kuma zabiba yayinda mryam da nana hauwa’u ke zaune a d’akin sun kulle kansu suna zantawa,ahankali aunty shahida tace “alkubus fa kikace mami bayan tsawon shekaru “wallahi shahida ,ni kaina abu yayi matukar bani mamaki tun bayan rasuwar mahaifinku bai sake cinsa ba wanda hakan ya zamo silar da kowa ya daina cinsa acikin gidan nan kawai jiya bayan ya shigo yace shi zai ci nayi matukar mamaki .”gaskiya ne mami dole kiyi mamaki shekarun da yawa fa mami ta numfasa irin nasu na manya tace “kunsan wani abu ?”duk suka tsura mata ido suna sauraronta “ba kuyi tunanin wani abu akansa ba ?”atare suka girgiza mata kai me kike tunani akansa mami ?”inji cewar aunty khadija mami ta bud’e baki da zumar cigaba da magana sai ga ATA ya shigo yana qoqarin wucesu mami tace “yauwa ga adamcy din ma ya shigo ,ahankali ya tsaya yana dubansu “adamcy ka qaraso mana “yau ma nayi maka alkubus kuma nasan zakaji dadinsa fiyye dana jiya dan na jiya anyi aikinsa cikin sauri yau kam a natse akayisa .”
shiru yayi yana kallon fuskar mami dake kwance da tsananin farinciki “adamcy mami ka qaraso ka zauna mana” inji cewar aunty shahida still dai shiru yayi yana sauke numfashi gabad’aya suka tsura masa ido suna jin tsananin qaunar d’an uwansu, jiki a sanyaye ya soma taku sai dai hankalinsa da natsuwarsa baya gurinsu yana ga maryamarsa ahankali har ya qaraso zuwa inda suke inda aunty shahida ta kamo hannunsa ta zaunar dashi a kusa daita “wai kaci alkubus jiya ?”ka tuna da poverty din dady kenan khadija ko kin tuna lokacin da dady yake raye mami kusan kullum sai tai masa alkubus har compotetion ake gurin ci “murmushi aunty khadija tayi tana dubansa inda shi kam hankalinsa baya garesu cigaba da zantawa sukai cikin tsananin farinciki shi kam kasa cigaba da zama yayi acikinsu ya soma qoqarin mikewa adaidai lokacin da aunty shahida tace “a zubo mana muci tare dashi