Showing 165001 words to 168000 words out of 178062 words

Chapter 56 - MAR ADAMS BOOK 3 COMPLETE BY AYSHA BAGUDU.txt

don duk lokacin da zaka shiga damuwa ka sanar min kasacewar nasan baka da wani danuwa namiji da zai maye maka gurbin danuwa da kuma mahaifi” ta qarasa mgnr tana tura masa plet din hadin salad gabansa “wai ma me ya kaika gidansu maryama ne kaje ka sanar mata kana sonta ne ko ya !”tmabayar tazo masa wani iri wai me yasa mahaifiyarsa tasan zahirinsa da badinsa?”mami tasan mamakin maganrta yake tace “nasan zakayi mamaki Jin abinda nace amman karka manta nice na kawowa duniya ,yaakayi maryama taki amincewa ko“?yayi shiru kawai yana kallonta yana jin faduwar gaba mai tsanani aranshi “.






“ka fad’a min idan bata amince bane sai na baka shawar yadda zakayi ka shawo kanta cikin sauki ko kuma mu dini zuga muyi gidansu qawwnya tayi maganar cikin tsigar zolaya “bai san sanda murmushin dole ya bayyana Akan fuskashi ba yana cewa “kai sweetheart wallahi kin bari nayi dariyar da ban shirya ba” gyaran murya yayi yace “ba wannan bane wani abu ne ya tsaya min arai har yasa kika ga yanayina haka tace ”meye shi !”?ta tambayesa adaidai lokacin daya fara ci salad tun kafin lokaci ya kure masa sai dai idanunshi na kanta yace “sweetheart yau naga mai irin yatsun qafafunki a gidansu maryama koma nace miki mahaifiyar maryama wallahi yatsunta na hannu dana qafa exactly irin naki ..”




mami tayi shiru tana dubansa cike da mamaki sannan tana duban yatsun hannunta yayinda mr ata ya cigaba da cin hadin salad dinsa dake gabansa “kuma kinsan wani abun sweet Herat “?ta girgiza masa Kai “sai kinganta wallahi sai kinyi mamaki yadda yanayinta yake Kama da aunty nu..”tun kafin ya qarasa kiran sunan ringin din wayarsa ya katse masa maganarsa ya d’auki wayar yana duba wanda ya kirasa ,ganin abokin halkal kasuwancinsa ne yasa ya nemi izini daga wajen mami kanta ta gyad’a masa alamun ya d’aga .”
Ahankali ya soma magana yana cigaba da cin salad ganin wayar tashi mai tsawo ce yasa mami ta yunkura ta mike ta bar parlour’n .”Mr ata ya jima yana tautaunawa da mutumin har kusan sha d’aya da wani Abu sannan sukai sallama ya tashi da kyar ya shiga bedroom dinsa kai tsaye bothroom ya shiga yayi pest yayi alwala ya fito ya zare Jallabiyar jikinsa ya saura daga shi sai gajeren wondo iya cinya ya qara qarfin ac d’akin yayi addua ya kwanta akan katifa yana lullube rabin jikinsa tare da kallon saman d’akin idanunshi ya saisaita kana ya lumshesu ya fara tunanin ko maryama zata bi umarninsa ko kuwa zata masa taurin kan kin zuwa .”






a daddafe yayi weekend dinsa Allah Allah yake Monday tayi .”Ranar monday da wuri ya shirya ya bar gidan dan ko breakfast bai tsaya yayi ba cikin shigar manya kaya yadi ne blue black mai shegen tsaida ,wanda akayiwa dinkin zamani sai dai gaban aljihunsa anyi masa desing da logon din ATA company ,goma daidai a AGC tayi masa sakamakon abu biyu ,abu na farko maryamarsa abu na biyu kuma hira da yan jarida suke so suyi dashi.”
ahankali manya ma’akatansa suka dinga shige da fice a office dinsa wasu magana ce mai mahimmanci wasu kuma saka hannunsa suke bukata har zuwa lokacin da 12:00 dot ta buga yan jarida suka qaraso suka yi abinda ya kawosu suka wuce amman babu alamun maryama tazo aiki ya Kira some bayan ta shigo yace “maryama fa !”?
”maryama kuma sir?ya kalleta a d’age yana karta saman table din gabansa “irin kallon da taga yana mata ne yasa da sauri tace “ai ta kwana biyu rabonta da zuwa aiki kamar yadda kasani .”




shiru yayi kawai yana sauke numfashi tare da hura hanci cike da ‘bacin rai ya kai hannunsa saman goshinsa yana murzawa ahankali ahankali yana tunanin abinda ya kamata yayi mata a qarshe dai wayarsa ya d’auka ya soma qoqarin neman layinta inda madam some ta juya ta koma bakin aikinta kira biyu yayi mata sannan ta d’aga tare da yin sallama “bai tsaya amsa sallamar datai masa ba yace “maryama kina wasa dani ko ?”tai saurin girgiza masa kai alamun a’a tamkar tana gabansa “Ina ganin baki san waye adam ba shi yasa har kike taka masa doka “shiru tayi tana sauke masa hucin numfashin Wanda dole tasa ya d’an lumshe idanunshi yana cewa “na fuskanci maryam kina son ganin iyakar taurin kaina ko“?”kayi hakuri amman ai na fad’a maka bazan ci..”oh my god wai me na fad’a miki ?”banace lallai kizo yau ba “kayi hakuri sir ni aikin ne gbdy ya fice min arai kar na dawo ayita samun matsala dani “da sauri ya mike tsaye tare da dunkule hannunsa ya naushi iska sannan ya dinga Kai kawo a filin office din inda idanun madam some da hankalinta yake kanshi sosai taga ya shiga damuwa maryama kuwa tana can rike da waya tana zance zuci “dokar daya kamata yayi akan matarsa ko damuwar daya kamata yayi akan matarsa ya tsaya yana yin abinda bai shafesa ba on expecting taji saukar muryarsa “karki ga na damu akanki ki d’auka wani dalili ne amman kisani zuwanki aiki gobe shine kwanciyar hankalinki wallahi muddin kuma kika yarda na tako gidanku zan miki abinda zai miki illa.”








Mmn sudais
[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗


BOOK 3


*AYSHA A BAGUDO*


WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim


Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.




47




“karki ga na damu akanki ki d'auka wani dalili ne amman kisani zuwanki aiki gobe shine kwanciyar hankalinki wallahi muddin kuma kika yarda na tako gidanku zan miki abinda zai miki illa."ta maimaitawa kanta furucinsa tana jin wani irin mummunar fad’uwar gaba from know where dan zuwa yanzu tasan halin mr ata kamar yunwar cikinta bashi da kyau ta kowane fanni kuma duk abinda yace zai aikata zai aikata shi babu wanda ya isa yasashi kuma babu wanda ya isa ya hanashi ,zai iya aikata fiyye da abinda yace zai mata“.to ma akan me ye zai nemi ya dinga takurawa rayuwarta alhalin ita din ba matarsa bace ba kuma kowa nasa bace ?”.ahankali ta sauke naunauyen ajiyar zuciya batare data sake cewa komai ba.”
“maryama….”!




ya kira sunanta cikin wata irin kasalalliyar muryarsa mai tsananin kashe sansar jiki da tsuma zuciya wanda yasa taji gabad’aya komai ya tsaya mata cak, yayinda ahankali ahankali tsigar jikinta suka dinga mikewa sai dai daga sunanta daya kira bai qara cewa komai ba yayi shiru ya koma ya zagaye table dinsa ya tsaya ya d’aura hannunsa d’aya,jikinsa yayi mugu mugun sanyi dan ya fara Jin alamun bazata zo ba dan haka ya wani dawo kamar wani abun tausayi muryarta a sanyaye tace “sir ka kira sunana kuma kayi shiru ?”tsaki yaja yana fesar da iska mai zafi daga bakinsa .”“please sir kayi hakuri “zaki zo goben ko zaki tsaya yi min taurin kai?”wani irin mugun tsoronsa ne taji ya shigeta wanda yasa tai saurin cewa”shikenan naji zanzo!”yana gama jin abinda ta fad’a ya katse kiran tare da lumshe tsumammun idanunshi yana jin wani irin farinciki na shigarsa with an unreadable expression akan fuskarsa.”






maryama kam numfashi ta sauke da ajiyar zuciya atare tana sake mamakin qarfin halinsa,mutun kamar wani aljani gabad’aya yana son ya canza mata tsarin rayuwarta da tunaninta koma tace ya canzata completely dan a halin yanzu bata da wani aiki sai fama da tunaninsa ,ahankali ta runtse shayayyun idanunta tana sake tariyo komai nashi most especially yadda yake nanike mata a duk sanda zasu kasance tare wasa wasa dai mr ata so yake lallai sai yayi wa rayuwarta karfa karfa da karan tsaye sai ya dasa mata matsanancin son shi ya ruguza mata rayuwa sannan hankalinsa zai tashi , ta jima zaune tana tunanisa kafin ahankali ta zame ta kwanta a gurin still dai tunaninsa bai bar zuciyarta ya huta ba.”




“ maryama me zai hana ki auresa kawai tunda ya amince zai aureki kuma kema alamu sun nuna kin fara jin wani abu akanshi ?”ta yiwa kanta tambayar tana jin wani abu tun daga tsakiyar kanta har zuwa kasan maranta mai kama da shocking din wutan lantarki “maryama matukar kika auri mutun nan wahala zaki sha a hannunsa ki manta dashi kawai ki samu wani ko kuma ki yiwa Oga amar magana ko akwai wanda ya yarda da natsuwarsa kuma wanda bashi da mata ya had’u su aure kamar hakan zai fiye mata zaman lafiya da samun kwanciyar hankali a rayuwarta “yes yes !!gara kiyi hakan dan auren mr ata ba mafuta bane gareki wahala kawai zaki bawa kanta ga matarsa dan dole kin san yana daita ga kuma baud’adden halinsa.”Juyi tayi ta gyara kwanciyar tana tunani da zance zuci tana jin kamar kartaje aikin gobe sai dai zuciyarta na tsananin jin tsoro dan bata san abinda rashin zuwan nata zai haifar ba .”






Washegari


Da misalin karfe shabiyu saura Mr ata yana tsaye a gaban ma’aikatansa a office dinsu maryama kuma har lokacin bata qaraso ba yayi shiru yana zance zuci sai gata ta shigo a natse bakinta d’auke da sallama cikin shiga ta kamala, sai bayan data shigo office din sannan taga mr ata tsaye .”office din ya d’auki shiru tamkar babu wasu halittu dake numfashi acikinsa duk wad’an da ke zaune acikin office din babu wanda bai juyo ya maida hankalinsa kanta ba sakamakon jin sautin muryarta d’aya byn d’aya take kallonsu kmr yadda suke kallonta kowa na zaune a mazauninsa sai dai bata ga alamun yusura ba .”
mr ata kuwa tun da ya d’aura tsumammun idanunshi akanta bai d’auke ba. dan tuni ya fara cire ransa da zuwanta a yau din duba ga lokaci ya fara tafiya dan har ya shaka ya fara jin haushi jira yake biyu ta buga yayi mata diran makiya kallonta ya cigaba da yi koina na jikinta a lullu’be yake tun daga saman qafarta har zuwa kanta da hijab wani irin sanyi ya ratsa shi karon farko yaji asalin shigarta ta baya tayi matuqar burgesa babu abinda ya nuna ajikinta wani zirrr ya dinga ji asansar jikinsa har tsakiyar kanshi kamar ana jona masa shocking ahankali yaji ya fara samu wadatacciyar natsuwa .”






ta kalli inda yake tsaye ganin yadda ya zuba mata ido ko kiftawa ba yayi yasa ta bud’e bakinta da kyar tace “sorry sir good morning “.bai amsa mata ba kuma bai d’auke kwayar idanunshi akanta ba ,sai dai irin kallon da yake mata yafi komai d’aga mata hankali “oh Allah ni mryama wannan kuma wani irin kallo ne haka ?”to ko dan ta ‘bata lokaci ne yasa yake kallonta haka ?”ta fad’a a kasan ranta,dan ita wallahi bata son yadda yake kallonta dan wanan kallon nasa kallo ne mai cike da kwarjini da dagulawa mutun lissafi ne .”






Ahankali ta juya ta soma taku acikin Office din yayinda mr ata bai daina kallonta ba har ta qarasa inda empty chairs suke ta samu waje tayi wa kanta matsugunni ta had’e hannuwanta waje d’aya tana kallon wani gefe dabam .” a natse ya dawo kusa daita ya tsaya ta d’an saci kallonsa sai kuma ta d’auke shayayyun idanunta da sauri ganin ta bar kallon wanan bangaren da yake ya dawo d’ayan bangaren da ta maida fuskarta ya tsaya ya soma mgn“ guys abinda nake son nace shine nan da sati biyu masu zuwa zamu bar kamfanin nan zamu koma sabon kamfani wanda acan zamu cigaba da aiwatar da ayyukan creation dinmu” ahankali ya cigaba da yi masu bayanin irin cigaba da yake son su kawowa kamfani kuma har zuwa wannan lokacin da yake masu bayani bai fad’a masu inda zasu koma da aikin ba
kuma duk yawo su babu wanda yayi qoqarin tambayarsa inda zasu koma din yadda sukai shiru haka mryama tayi tare da tsura masa idanun tana kallon sa tana nazarinsa har sanda ya dasa aya ya qara da cewa “ ina fatan kun fahimceni “.




“yes sir !” suka had’a baki wajen fad’ar haka still babu wanda yayi tunanin tambayesa wanda maryama bata raba dayan biyu tsoro ne “.
“sir mai yasa zamu bar nan din ?kawai ta tsinci bakinta da cewa haka ,shiru yayi mata batare da yace mata uffan ba “naga nan din kamar ..” “keep queit…”ya katseta ta hanyar fad’ar haka yana hura hanci shiru tayi kamar yadda ya bukata yana hukuntata da kwayar idanunshi “maryama what’s this nonsense?”what’s every time if am talking you most disobey me “? nasan kinsan bana son haka but why ?am sorry sir! but nayi tambayar ne saboda musan..”
”maryama ki min shiru banason ki sake cewa komai” tace “okay sir “.!
ta fad’a sai dai tayi kasa da kanta muryarta can kasan makoshi tace “ko me yasa zai daddakemu daga nan ya maidamu wani waje kamar wasu tsuntsaye ?”me kike ce ?ya tambayeta da sauri ta d’ago kanta gabanta na fad’uwa ta zuba masa shayayyun idanunta tare da sanya kwayar idanunta cikin nashi “ba kallona nace Kiyi ba what did you say ?”bance komai ba sir, kawai dai kunnenuwanka ne suka ji kamar nace wani abu.”




“Maryama nasan kince wani abu” tai shiru kawai” ina jinki! “nifa babu abinda nace kawai dan dai kana jin haushina ne yasa kunnuwanka suka jiyo maka kamar nace wani abu “keep quiet bansan me yasa kika rainani over ba ,kisani na d’auki aikina da mahimmanci ban d’aukesa shirme ba sannan idan kinga zaki bimu fine idan kuma zaki cigaba da zama anan gud ya rage naki.” dumm taji gabanta ya fad’i “daman yace tazo aiki ne dan kawai ya samu damar wulakantata kome ?”tayi mugun zuba masa ido tana dubansa ya juya a natse ya fuskanci ma’akatan sa “guys ina fatan zakuyi aiki dani kuma zaku bini duk inda na bukata?”.sure sir okay back to work ”yana gama fad’ar haka ya wuce ya fita ko kallon inda take bai yi ba dan har lokacin haushinta yake ji kamar yadda ta fahimta Itama ko kallonsa batai ba sai dai abinda yayi mata ya dameta matuka idan tai bleming kanta akan saka bakinta cikin maganarsa ko zuwanta aiki sai kuma ta dawo ta bashi laifi wulakancin da yayi mata .”




Jiki a sanyaye ta bude littafi tana duba zane tana zance zuci “ya ma bari mutun yayi magana yaji me mutun zai ce amman yaki ya hau mutun da matsefa ,masefaffe kawai abinda ya kamata yace min me nake qoqarin cewa .?”Ko me yasa zai daddakemu daga nan zuwa wani guri da alamun inda zai maidasu din akwai nisa sosai may be shiyasa yayi masu kyautar mota amman ita ya hanata ko ita uwar wa ta kashe masa da zai bawa kowa ya hanata ?”tayi maganar tana jan tsaki a fili ita dai gasky zata samesa taji inda zasu koma matuqar akwai nisa daga unguwarsu bazataje ba ,gara ta hakura da aikin gabad’aya ta huta tunda daman akwai sharad’i akanta.”
ahankali ta soma qoqarin mikewa tsaye tana gyara zaman hijab dinta sai ga madam some ta shigo “yauwa maryama latest desing na royal palace zaki zana “okay ma ,zuwa yaushe ake bukata ?”eh to ko zuwa gobe da safe haka “okay ma zanyi qoqari in sha allahu .”




Madam some ta juya ta fita ta shiga wani office din ita kuma ta nufi office din mr ata bata tsaya neman izini ba ta fad’a kanshi na sunkuye yana duba wani file din zane sai dai nan take ya fahimci Itace ta shigo masa office babu neman izini,a natse ta qaraso ta tsaya a gabansa tare da goya hannuwanta duka abaya tace “sir !”ya d’ago kanshi ya had’e hannuwansa waje d’aya ya dafe ha’barsa tare da zuba mata ido .”amm daman nazo ne nasan inda zamu koma aiki idan wajen yayi min zan biku .”
“Idan kuma wajen bai miki ba fa ?”zan ajiye aikin gabad’aya”.ta bashi amsa kai tsaye batare da wani shayi ko ‘bata lokacin ba “okay lekki zamu koma”. “lekki!?ta furta a fili tana d’an ware idanunta ya gyad’a mata kai yana lumshe mata ido “ammm gaskiya Ina ganin zan ajiye aiki dan …”sai kuma tayi shiru ta kasa cigaba da magana “uhm Ina jikin dan me ?”dan na samu wanda zan aura mgnarta ta daki kunnuwansa ta wuce har cikin zuciyarsa tamkar ta soka masa mashi haka yaji maganartata a kahon zuciyarsa “yayi shiru kawai yana kallonta wanda kallon nasa yasa ta sunkuyar da kanta kasa dan bata son wannan kallon nasa mai firgitarwa .”






ahankali ya motsa lip’s dinsa yace “daga yaushe zuwa yau she ne har kika samu wanda zaki aura ?yayi mata tambayar kamar zai yi kuka ta d’ago kanta a natse har lokacin ita yake kallo fuskarsa a had’e “daga sunday wani d’an uwa zan aura”ta fad’a masa tana son tabbatar da abinda yake boye wa aransa,ya lamgwabar da kai gefe kamar abun tausayi “me yasa ni bazaki aure ne ba ?”yayi mgnr acikin ransa yana jin wani irin tuttukin bakinciki mara misaltuwa ahankali ya sauke hannunsa ya mike tsaye ya dawo inda take tsaye ya tsaya a gabanta yana lissafin abinda zai yi kamar bazai yi magana ba sai kuma ya motsa lip’s dinsa “ni me yasa bazaki aure ni ba sai wani dabam “.?






“Saboda baka sona!”.
“Saboda bana sonki ?” yes of course baka sona shi kuma yana sona kai kuma kace taimakona zakayi kaga gara na auri mai sona ba mai taimkona ba ,dan Kai daman kafi qarfin aurena bare km tun kafin aje koina ka fara da taimakona zakayi “naji but shi da yace yana sonki ke kuma kinji aranki kina son shi ko kawai zaki auresa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login