Showing 15001 words to 18000 words out of 104857 words

Chapter 6 - UWATACE SANADI Book Complete by Maimuna Tijjani Iyam.txt

Advertisement

22 Feb 2025

7335

sai annemota?Allah yasa ya dawo bai same ta ba komai ya mata ita ta jawa kanta".




Tana rufe bakinta Baffa ya shigo riƙe da bokatin dana fita ɗebo ruwa dashi.




Hamdala inna tayi tana faɗin"Adamu yana ganka da bokatin ita kuma hibban ina ka baro ta?".
"Inna a kofar gida fa,naga bokatin na shigo dashi ita hibban ina taje?". Cewar Baffa
Cike da jimami Inna tace"Tun safe ta fita ɗebo ruwa har yanzu ba ita ba labarinta".


A harsale Baffa yace "uban wa yabata iznin fita?".
" Inna ce sai danayi nayi,a bari sai ka dawo ka nema mai ɗebo ruwan amma ta dage akan zataje".Hajara ta faɗa tana cillawa Inna wata hararan.




Tsaki Baffa ya sake tare da ficewa daga gidan.Bai Daɗe ba ya dawo inna da duk ta gama rikicewa tace"Adamu aganta?".
Ajiyan zuciya ya saka kafin yace "inna Hibba butulu ce,Hibba ba ƴar mutumci bane a yau nayi mamakin kasancewar ta ƴar yaya Sule domin ko kaɗan bata gado halinsa ba".
"Adamu meya faru yimin yanda zangane meye Hibban tayi?".






Sai da Baffa ya numfasa sannan yace,"Inna Hibba guduwa tayi yanzu dana fita wani yake shaida,min ya ganta a tasha kuma yaga shigarta mota".
Salati inna ta saka tana kuka tana faɗin"Adamu kagani ko sai dana gaya maka ka haƙura da maganar auren da yarinyar nan amma kaƙi,to yanzu ga abinda kajawo mana marainiyar Allah ta'ala".
Cike dajin haushin maganar inna hajara tace"Haba!inna ya zaki daura masa laifin daba nasaba taje ai duniya ce tafi gabaruwa iya jima".








*********************************




Tunda na sauƙa a tasha dana gama kuka na,na tashi na hau tafiya.
Har aka ƙira sallan la'asar mai tallan pure water na tsayar na saya domin nayi alwala nayi salla,gefen zani na na since zan bata kuɗin ruwanta.
Naga babu kuɗi salati nasaka tare da sake dubawa amma babu kuɗin ba alamar sa.
Miƙa mata ruwan nayi ina cewa,"Kiyi haƙuri banga kuɗin nawa ba".
"La ki riƙe kawai ba komai ki bar kuɗin",nace "nagode".




Tafiya na cigaba dayi ina tinanin a ina na jefar da kuɗin nan,ga wata masifaffiyar yunwa dake nuƙurƙusa na.
Hawaye ne suka fara tsiyayowa daga idona saura kiris wani Mai keke ya bugeni,sai daya rurrugamin ashar kafin ya wuce.
Hawayen danake yi ne,suka tsananta gefen wani shago saloon na zauna nayi alwala sannan na shimfiɗa ɗan kwalina nayi salla akai.




Na kuma cigaba da tafiya bansan inda zan nufa ba.Yunwa nakeji tamkar zan mutu ga wani masifaffen ciwon kai daya dameni ina tafiya ina haɗa hanya kamar bugaggiya,ina zuwa dai-dai wani gidan cin abinci na faɗi na suma.




Nan jama'a suka cika a kaina aka shiga dani cikin gidan abincin,aka bani abinci naci sannan na soma dawowa cikin hayyacina.




Wata matace Mai gidan abincin tace"Baiwar Allah ya kikejin jikin yanzu?"


"Alhamdulillahi nagode da taimakon ki amma naso ace kin barni na mutu".






Cikin sauri tace,"Subhanallahi! baiwar Allah meya miki zafi cikin dunyia har kike wannan fatan akanki?".




Hakanan kawai naji zuciya ta bata nutsu da in samar da ita labarin rayuwa ta ba.




Shiru nayi tare Sunkuyar da kaina ƙasa,ta dafa kafaɗa tare da faɗin"Ƙanwata ki sanar dani abinda ke damunki ƴar-uwar ki ce ni mace".


Idona fal da hawaye nace,"Ki taimaka min domin Allah badan nasanar dake labarin rayuwa ba ta".
"Wani irin taimako kike so?".


"Wajen dazan zauna shine damuwata a yanzu."na faɗa inajin wasu sabbin hawayen nabiyo kunci na.
Sai datayi Jim kafin tace,"Zan taimaka miki zamuje dake gidana in mijina ya amince ki zauna shikenan".
"Nagode Allah yasaka da alkhari".


"Amin ya sunanki?"


Nace" HIBBA" ita kuma tace "sunan ta Amina".




Haka muka zauna a shagon har yamma sannan muka tafi gidan ta dake unguwan fayamasa.
Tun kafin mu isa ta shaida min tanada abokiyar zama balaraba da ɗanta ɗaya kabir tamin kashedi sosai,akan na kiyayi shiga harkan Balaraba da kuma ɗanta Kabir.
Muna isa gidan muka tarar da mijin anty Amina yana tsakar gida yana alwala saboda ƙiraye-ƙirayen sallan magrib da aka fara.




UWATACE SANADI


Tsarawa/Rubutawa


©Maimunah Tijjani Iyam




______________________________




Page 1⃣2⃣






Da sallama muka shigo ko sallamar bai amsa ba,yace"amina wannan kuma wacece?".


Nan anty amina ta shiga bashi labarin yanda muka haɗu.Miƙewa tsaye yayi tare da ƙwalawa baralaba ƙira yana cewa"fito ki tayani ganin ikon allah".


"Malam meye faru?",ta faɗa tana fitowa daga ɗakin.


" Amina ce ta kwaso mana wata gayyar tsiya dubeta".ya ƙarishe maganar yana mata nuni da inda nake tsaye.


kallona balaraba ta farayi from toes to head.Kafin tace"baiwar allah ina iyayenki?".


A hankali nace"suna nan",


"To maza-maza ki fice daga gidan nan kinada iyaye ki,barosu ki zauna damu.malam wannan yarinyar nan ba mamaki cikin shege tayi iyayen suka koro ta",




Wani zafi naji a raina furcin balaraba sun soki zuciya ta,bansan sanda hawaye suka fara gosilo a fuska na ba.


Roƙon sa anty amina ta shiga yi daya barni na zauna,sai daya kafa mata sharuɗa kan zata ɗauki nauyin ci da Sha na.




Ta yadda itama balaraba kashedi tamin akan,kar nasake na shiga harkan ɗanta KABIR, ɗakin anty Amina muka shiga.
Kallo ni tayi tana cewa" Hibba na roƙe ki dan girman allah ki dubi darajan taimakon dana miki ki kiyaye kanki daga shiga harkan balaraba da ɗanta,har ki zamo silar tarwatsewar aure na".




"In sha allah Anty zan kiyaye haka".




"Yauwa ki tashi kiyi alwala kiyi salla".




Ta nunamin banɗakin dake cikin ɗakin na shiga nayi alwala nafito nayi salla.




Ina zaune a inda nayi sallan nace"Anty Dan allah zanyi ƙira da wayanki inbazaki damu ba?".


Cikin sakin fuska ta miƙomin wayar sannan ta fice daga ɗakin.




Numbern yaya Fawas na saka daman na haddace ta akaina,na shiga dialing numbern.


Inna ƙira caraf!yaɗaga inajin muryansa na fara hawaye to ma mezan faɗa mishi?nace masa na baro gida kenan saboda baffa zai aurar dani?ko kuma ince mishi na shiga duniya?saboda za'amin auren dole ko kuma saboda baffa ya dakatar min da karatuna?.


Kashe wayar nayi ba tare dana mishi magana ba,muryarsa ma kaɗai danaji yasamar min da kwanciyar hankali.


Kaina na kifa akan gwiwowina ina rusar kuka,tare da tinanin rayuwar dazan tsinci kaina anan gaba.






__________________HABIB__________________






Ta bangaren habib kuwa rashin samuna a waya,da kuma rashin dawowata makaranta da bashir ya sanar dashi ban yi ba yasashi cikin tashin hankali.


Kwance yake akan bed ɗinsa a part ɗinsa a gidan uncle suraj,yana dialing numberta kamar kullum yauma switch off aka ce masa,cigaba yayi da dialing numbern har izuwa lokacin da yasira ta shigo ɗakin.ko ƙaran shigowarta baiji balle sallamar data shigo dashi.




Gefenshi ta zauna tana bubbuga pillow daya ɗaura kansa a kai tana cewa"hamma!hamma!!hamma!!!".




Figigi ya tashi ya zauna ya haɗe rai yana cewa" wai ke ban hanaki shigo min ɗakin ba sallama ba".


"Ayya hamma wallahi nayi sallama sai dai inbaka ji dan na shigo na tardaka tanata tinani". Yasira ta faɗa tana ƙoƙarin zaman gefen shi.


Dafe kansa yayi tare da furzar da iska daga bakinsa.


Sosai yasira ta fuskan ta akwai abinda ke damunsa tace" hamma kana cikin damuwa meyake damunka hamma na?".




"Ba komai ƙanwata gajiyace kawai"


A nitse tace" hamma zanfi yadda inkace min bankai inji damuwarka ba akan kace min ba komai".


Cike da ƙosawa da sauraron surutunta yace" yasira nace miki ba komai ko",




Miƙewa tayi tana cewa"okay tinda bazaka faɗa min ba hamma bari naje na faɗawa ummi watakil ita ka iya sanar da ita".


Riƙo hannunta yayi yana cewa" zauna".




Ba musu ta zauna tare da cewa" to inajinka hamma meye damuwarka?".


A hankali ya dogo idanunsa dasu ka rikeɗe suka koma jajir ya zuba mata tare da cewa da ita ba komai.


Ajiyan zuciya ta sauƙe kafin tace "hamma nasan ni bazan iya maka maganin damuwarka ba amma ban iya tayaka da addu'a,please hamma na meke damunka?".


Nan fa ya sanar da ita komai har da yanda ya daina samun na a waya,gashi Dr bashir yace masa ban dawo school ba sannan sun sa Faisal ya ƙira.yaya fawas amma wayarsa shima kullum a rufe.


Ya ƙarishe maganar tare da sassauta muryarsa sannan ya cigaba da cewa.


"Yasira bazan boye miki ba,Innason hibba kuma zuciya bazata iya jure tashin taba duk ban furta mata ba,ina tsoron duk abinda zai sanyan ku tashin hankali mussamman ace nine sanadinsa,ina tsoron na rasa hibba domin muddin hakan ya faru zaku iya rasani".


Tun daya fara maganar ba abinda yasira,take yi illa hawaye tabbas ta tausayawa ɗan-uwan nata matuƙa.




Cikin kulawa tace" hamma kaje gidansu mana".


" Yasira naje sau babu iyaka amma aka ce min sun tashi tun bayan rasuwar babanta".




Riƙo hannunsa tayi tace"hamma bi'izininlahi ta'ala zata bayyana sannan zata amshi soyayyarka".




Ajiyan zuciya sannan yace"allah yasa hakan ƙanwata,Dan ina fargaban saku iya rasani matuƙar na rasa hibba".




Haka tayita kwantar masa da hankali har tasamu ya fito yaci abinci.




Haka abubuwa suka yita tafiya duk weekend habib sai yaje damaturu yayin dashi da Dr bashir zasu garzayo potiskum,amma kullum bacigaba.




Harsu shahida suka tambaya ko muna waya dasu,suka ce tun gaishewar rasuwar Abba dasu min basu sake samuna ko a waya ba.


Ranan habib yana office ya dafe kansa ga tulin files ɗin dasuke gabansa,amma ya kasa dubasu,shigowar PC ɗin sane ya sashi ɗago kansa.


"Sir waɗannan turawan masu company sarrafa alkama a chine ɗinnan sun iso har na shirya meeting ɗin". PC ɗin ya faɗa yana kallon shi.


Miƙewa habib yayi ya nufi ɗakin taron nasu koda yaja ma yakasa tsinana wani abin kirki,a haka suka tashi gida ya nufa.


Yana isowa ya nufa direct part ɗinsa ya shiga ya wuce bedroom kan bed ɗinsa ya faɗa yana sauƙe numfasha a hankali.




Yakai kusan 30min a haka sannan ya tashi ya shiga bathroom yayi wanka, sannan ya fito ko mai bai shafa ba ya zara doguwar rigar jallabiyarsa fara tas! sannan ya fito ya shiga part ɗin ummi.




Tare da uncle suraj yasame su sai yasira data zubawa makeken tv ƙiran plasma dake manne a cikin wall ɗin parlon, ido tana kallon wani series(hawas Maya)da ake haskawa a mbc Bollywood.


Yana shigo da sallama ɗauke a bakinsa,ummi ta amsa sallamar gefen yasira ya zauna yana yiwa uncle suraj sannu da hutawa.


Sai daya tambaye shi ya companies ɗin?yace" alhamdulillah daddy komai yana tafiya yanda akeso".


"Masha Allah I hope kana shan magungunan ka". Daddy ya tambaya cike da kulawa


Sai da yayi ƙasa da kansa sannan yace" E daddy Ina sha".


Kallon yasira yayi yanda ta zubawa tvn ido ko kiftawa babu,da alama tana enjoying kallon series ɗin.




"Wai ke yanzu kinajin abinda suke faɗa ne kika wani zuba ido haka?".


Dariya tayi sosai sannan tace" hamma ina ganewa mana,kaima inkana kalla yau da gobe zakana fahimtar me suke faɗa".ta ƙarishe maganar tana mai da kallonta ga tvn.


Murmushi yayi kafin yace"Gobe sayyid zai dawo ai munyi waya dashi ɗazu yake faɗamin sun sama hutu zaiyi maganinki inya dawo ai kinsan halinsa sarai".




Sayyid lecturer ne a freedom college of nursing and midwifery kano,ita kuwa yasira tana shekaran ƙarshe a alƙalam university dake cikin katsina nan.inda take karantan biological science.


Zaro idanu yasira tayi tana faɗin "na shiga uku hamma kawai kace mugun zai dawo".


Nan ta miƙe ta nufi upstairs tana ta faman gunaguni.


Dariya habib yayi sosai irin shirmen yasira wasu lokatan sukan mantar dashi damuwar dayake ciki,suma su ummi da daddy dariyar suke kafin ummi tace.


"Zai dawo zaki maimaita a gabansa".


Miƙewa daddy da habib sukayi,saboda ƙiran sallan magriba da'aka farayi,habib na Miƙewa yaji kamar wani Abu ya tukare masa zuciyarsa.


Nan da nan yaji ƙirginsa ya masa nauyi da wani jiri dayake ɗibarsa,tangal-tangal yayi kamar zai faɗi daddy ya riƙi shi da sauri yana faɗin"habib lafiya?".




Wani tari Mai ƙarfine ya sarƙe sa cikin ƙanƙani lokaci Duk yafita hayyacin sa.


Ummi ta kawo masa ruwa,daddy ya basa sannan tarin yaɗan lafa daddy yace.


"Tashi mu tafi asibiti habib". Ya faɗa yana ɗago habib ɗin


"A'a daddy ai naji sauƙi ma".




Badan sun so ba haka suka barshi dan basa son takura masa.



Haka suka tafi masallaci suna dawowa ya wuce part ɗinsa,wanda ya sama rakiyar daddy.


Sam bacci yaki ɗaukar sa har aka kira assalatun asuba,yanda yakejin jikinsa bai jin zai iya tashi balle har ya fita.
A bedroom ɗinsa yayi,salla a zaune ma ya yita sannan ya koma ya kwanta kan bed ɗinsa.
ƙarfe 9:00am dai-dai na safe Sayyid ya dawo cike son ɗan nasu Daddy da Ummi suke amsa gaisuwar dayake musu,ita kuwa Yasira tana maƙale jikin Ummi kamo kunnenta Sayyid yayi yana cewa.


"Wato kin gani shine ko gaisuwa babu?".




Tunin Yasira ta saki ihu tana yarfa hannu,tana faɗin "A'a Hamma Sayyid kayi haƙuri,wayyo Ummi zai tsinkemin kunne".




Saketa yayi yana dariya tare da faɗin" ina hamma fa?".
"Yana part ɗin sa" cewar ulUmmi
Part ɗin Sayyid ya nufa yana tura kofan bedroom ɗin,ya hango shi kwance a ƙasa cikin jini da duk alamu aman jinin yayi.


A kiɗime ya nufoshi yana kiran sunansa,da ƙarfi"Hamma!Hamma!! Hamma!!!".




Wayarsa ya ɗauka ya kira wayar Daddy yana faɗa masa halin dayazo yasama Hamma Habib ɗin a ciki.




Dukkaninsu suka shigo bedroom ɗin, ɗaukar shi Daddy da Sayyid sukayi suka wuce asibiti dashi.


Emergency aka shiga dashi yayin da Yasira keta shirga kuka hakama uUmmi,sun kai kusan 1 hour suna jira,kafin likitan ya fito yace.


"Daddy da Sayyid su same shi a office".




Ummi da Yasira kuwa ɗakin da'aka shiga dashi suka shiga,yana kwance yana bacci ansa masa robar ruwa.Fuskarsa tayi fayau da ita sai ɗan raman dayayi.




Kallon likitan Daddy yayi yace" doctor meyake damunsa?".


Sai da likitan yayi Jim kafin yace,"Damuwa ce ta masa yawa kuma matuƙar ya cigaba da zama a haka zuciyar sa tana cikin barazana,dan zata iya bugawa ako yaushe".


Sai da likitan ya numfasa sannan ya cigaba" Akwai abinda yake so Wanda bai same shi ba".




Mamaki ne ya cika daddy fal! yana maimata,furcin likitan "wai damuwace ta masa yawa".
Miƙewa yayi ya fice, ba tare daya ƙarisa jin sauran maganan da likitan ya cigaba dayi ba.
Sayyid ma fitowa yayi daya gamajin sauran maganan da likitan ya faɗa musu yabi bayan daddy.


Ɗakin da'aka kwantar da habib suka shiga,har yanzu bai farka ba.




Gefenshi Daddy ya zauna,ya riƙo hannun sa sannan ya shiga faɗin.




"Habib meyeke damunka a cikin wannan duniyan?mena gaza maka Wanda uba yake yiwa ɗansa?Habib ban barka kayi maraicin iyayenka ba domin na maye maka gurbin su?".
"Wai meyake damunsa ne?,meye likitan yace?".uUmmi ta shiga jero tambayoyin a lokaci guda.



Nan Sayyid ya faɗa mata komai.Kuka ta saka mai sauti tana cewa" innalillahi!da wani ido zan kalli Granny na gaza samarwa Habib farin-ciki"


Da ƙarfi ta furta "Habib meke damun zuciyarka?".
Dukkansu kuka sukeyi bamai bawa wani haƙuri.Fita Daddy da Sayyid sukayi masallacin dake cikin asibitin,nan kuwa yasira ta sama damar faɗawa mmi komai game da damuwar Habib ɗin.
Ta tausaya mishi matuƙar,su Daddy suna dawowa kuwa suma ta faɗa musu.
Tunda Sayyid ya sanarwa Granny ta ɗaga hankalin ta sai datazo,




Nan fa Daddy ya dage sai an fitar dashi waje domin sama masa ingantaccen lafiya acewar sa zuciya ba wasa bace.
Likitotin sukace masa ba sai an fitar dashi ba suma zasu bashi kyakykyawan kulawa.
Amma Daddy ya dage sai ya fitar dashi,dan tunda sukazo asibitin yau kwana uku kenan sau ɗaya yayi magana.
Nan ya shirya musu tafiya malesia domin kula da lafiyarsa,tare da Daddy da sayyid aka tafi.
Yasama kyakykyawan kulawa daga likitotin kasar,amma sun shaidawa Daddy cewa zuciyarsa ta taɓo.Dan haka a kiyaye ɓata masa rai.


Kwanan su goma sha shida aka sallame su,tare da kafa musu sharaɗin duk bayan wata uku Habib ɗin zai dinga zuwa ana duba lafiyar zuciyar tashi.


Yasama kulawar ahlin nasa sosai har ya fara dawowa hayyacinsa,ƙoƙarin sa shine ya manta da hibba kodan farin-cikin iyayen nasa.


Daddy kuwa tunda yasira ta faɗa musu nice sanadiyar damuwar Habib ɗin.Ya kira Bashir suka tattauna akan zance,nan Bashir yasake sanar dashi wasu abubuwan daya sani dame dani.


Nan fa Daddy ya zubawa gidan TV da radio kuɗi anata cikiyata.dan a nasu zaton tare da Umma da kuma yaya Fawas muka tashi daga gidan.




___________________________________






Ina zaune a tsakar gida ina wanke-wanke,anty Amina kuwa ta tafi shago.


Kabir ya shigo tare da wasu abokansa uku."Ke ki kawomin abincina ɗaki". Ya faɗa da tsan-tsan izza.
Ko kulashi ban yi ba na cigaba da aukina,ya ƙaracewa "bakya jinane?,nace kikawomin abinci ko".



Sai a lokacin na ɗago tare da faɗin,"Amma ai kasan niba yar aikinku bace dazaka sani aiki ko?".


A harsale Kabir yayo kaina "ke ni kike faɗawa haka?",




"An faɗa maka ɗin".na faɗa ina ajiye soson wanke-wanken dake hannu na.




Mari ya shiga sauƙe min hagu da dama yana faɗin" shashasha to ko ita wacce ta kawoki gidan bata isa ina faɗa tana faɗa ba balle ke wawuya kawai,wacce zaman gidan iyayentaya gagare ta".




Yana gama faɗin haka ya shiga ɗakin sa yayin da zugan abokan nasu suka rufa masa baya.


Dafe kuncina nayi ina hawaye, a hankali na maimaita furcin kabir"WACCE ZAMAN GIDAN IYAYENTA YA GAGARE TA".




Share hawaye na nayi cikin sanyin jiki na ƙarisa wanke-wanken sannan na dawo ɗaki nacigaba da sana'ata wato kuka,sai daf da magriba sannan anty amina ta dawo ko kaɗan ban bari ta fahimce wani Abu ba.




Washe gari da wuri anty Amina ta tafi shago,sannan nima na fito na kama aikin dana san ko sharafar mutuwa nakeyi sai nayi wannan aikin.


Share gidan sannan nayi wanke-wanke na wanke banɗaki.


Na koma ɗaki na kwanta,a hankali naji ɗumin hawaye nabin fuskana.Ajiyan zuciya na saka tare da kwantar da kaina akan pillown.


Haƙiƙa kowa da irin tasa ƙaddarar a rayuwa,mutuwa ta rabani da Abba ƙaddara kuma ta rabani da yaya Fawas.


"Ya rabb ka nufeni da cimma abinda na fito nema wato karatu,na cika burin Abba sannan na cimma ƙudurin yaya Fawas". Na faɗa ina share hawayen dake bin fuska ta.


Kamar daga sama naji balaraba na kwaɗa min kira,cikin sauri na miƙe na fito nace" gani".


Ba tare ta kalle inda na keba tace"ke hibba saboda tsabar rashin mutunci shine baki sharewa Kabir ɗakinsa ba?,bayan nasanar miki kullum kina tashi kizo ki share masa ɗaki".




Sanyayyan ajiyan zuciya na saka sannan nace"naga bai tashi daga bacci bane shiyasa ban shiga ba".


Muryan Kabir naji yana cewa yayin dayake fitowa daga ɗakin nasa yana faɗin" munafuka ni tun yaushe na tashi,zaki wani ce wai ban tashi ba".






"Yi shirunka basai ka ɓata bakinka ba ni nasan halinta tsabar munafurcine".




Cikin sanyin murya nace"kabir kaji tsoron Allah yanzu fa ka tash........."


Ban ƙarisa maganar ba Balaraba ta rufe ni da duka tana faɗin"shegiya munafuka acikin mu yawake miki ƙarya?".




Duka na takeyi tamkar tsohuwa ta sama shantu,tun ina bata haƙuri har maganar ma ta gagareni.


Anty Amina ce ta shigo tare da sakin salati,ta dakatar da balaraba daga dukan datake min ta hanyar cewa.


"Haba! Balaraba meye baiwar Allahn nan ta miki a dunyia?,karki manta fa itama ƴace ga wasu sannan ƘADDARA CE(littafina mai zuwa in sha Allah) ta rabota da iyayenta".




Cikin matuƙar ɗaga murya Balaraba take cewa,"To ni ina ruwa nace ina ruwa na.dakike

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login