Showing 36001 words to 39000 words out of 112633 words
Chapter 13 - DAURIN GORO COMPLET book 1 by Hafsat Rano.txt
sai kudi masu yawa, murmushi nayi na ciri wayar na ajiye jakar ina kokarin kunna wayar.
Numbobi biyu na gani akai, daya an saka my number, sai dayar dake rubuce da babban baki, *BABANA* zuba wa number ido nayi ina kallo, babu shakka number Ya Farouk ce, shiru nayi ina tunanin abinda zanyi da ita da Dadah tayi min saving dinta akai, sai dai bani da amsar hakan. Ajiye wa nayi kawai na shiga wata sabgar ina kokarin ganin na manta da damuwa ta.
Kwana uku da tafiyar su Dadah sai ga kiran ta, da murna na daga muka gaisa ta tambayi ni idan akwai matsala, hira muka danyi sannan ta kashe bayan ta kara jaddada min kalmar nan ta hakuri ta na riga na gama haddace ta. Tun daga lokacin muke waya sosai, wani lokacin naga shiru nakan kirata muyi hira sosai. Wata rana muna waya take min maganar Jamb, tabbas nima dama ina son yi ɗin,sai dai idan na duba yanayin da nake ciki sai nace na jira wata shekarar, ko dana fada mata uzuri na bata amince ba, a wannan shekarar take so nayi, babu inda raino ko ciki ke hana karatu. Dole na amince na shiga tunanin yadda komai zai kasance.
***
*Bayan wata biyu*
Ba tare da dogon nazari ba, tabbas yan watannin nan a cikin waha'a nayi su, wahalar rainon karamin ciki zuwa kokarin mantawa da dukkan rayuwa ta ta baya, bani da matsala da Inno, dan babu abun da yake hada ni da ita, iya kar kokari na ina yi ganin na kyautata mata, ita dinma a bangaren ta hakan ne, duk abinda tasan zan nema tana kokarin bani shi. Ranar muna zaune muna hira da Yalwati, wadda yanzu ta zama abokiysr hira ta tun bayan tafiyar Karime, dan Inno ba kasafai take doguwar hira dani ba, kasuwancin ta da ya kusa durk'ushewa ta jajirce ganin ta farfaɗo dashi, dan hakan ya zama ma kowanne lokacin ta me tsada ne a wajen ta.
Nura ne ya shigo, kansa dauke da hular gini, ya zauna daga gefen tabarmar da nake zaune yana jingina da bango cikin matukar gajiya. Cikin tausaya wa nace masa "Sannu." ruwan dake gefe cikin kofi na mika nasa, karba yayi yasha ya ajiye sannan ya ciro takarda daga aljihun sa
"Gashi Aminatu, dukkan bayanin yana ciki tace, ki shirya gobe sai na rakaki ki cike dan tace befi sauran kwana uku a rufe ba, Allah ne ma yasa aka danyi jinkiri wannan karon da sai dai wata shekarar."
Da farin ciki na karba na duba, sannan nace
"Kai amma naji dadi, nagode sosai Yaya Nura, Allah ya kaimu goben ."
"Amin." Yace yana mik'ewa.
"Bari na watsa ruwa a gajiye nake."
"Gaskiya dai, ai da gajiya."
Gyara zama nayi ina juya takardar principal din tamu cike da farin ciki.
Ina shirin kwanciya Inno ta shigo, tsayawa tayi a kaina tace
"Naji kuna waya ina tace miki ki saka?"
Na gane Dadah take nufi, kai tsaye nace mata
"Cewa tayi wai nasa Kano."
Shiru tayi, sai chan kuma tace
"Shikenan Allah taimaka." Daga haka ta fice tana jawo min kofar, ni kuma na gyara na kwanta ina fatan wayewar gari saboda tsananin farin cikin da nake ciki.
Washegari da sassafe na shirya muka dau hanyar zuwa cikin gari dan cike jamb. Bamu sha wuya ba muka gama muka dawo. Ranar jarabawar tazo naje na zana cike da addu'ar samun abinda naje nema. Haka muka dawo gida zaman jiran tsammani. Kwana uku kuwa tsakani sakamakon ya fito, sosai hankali na ya tashi, haka dai na daure nasa aka dubo min. Ban taba zaton zanci haka ba, hamdala nayi ta wa Ubangiji dan nasan ba iyawa ta bace. Dana kira Dadah ma na faɗa mata sai ta hau murna, saura jiran post Utme kuma.
A hankali cika na yana girma, ina kara tunanin yadda zata kasance min idan na haifi abinda yake ciki na, duk da yanzu bana shan wuya sosai sai dan abinda ba'a rasa ba.
Ranar dana gaji da zaman nayi gidan Karime, chan na wuni sai wajen magriba na dawo gida, washegari kuma nayi gidan Hanne. Sosai suke bani sha'awa, yadda suke zaune a dakin su, da dadi babu dadi, suna tare da mazajen su, hakan ba karamin sani tunawa da Ya Farouk yake ba. Haka dai nake bawa kaina k'warin guiwar komai zai wuce.
***
BAYAN WATA SHIDA
Haka rayuwa ta cigaba da garawa cikin hukuncin Ubangiji Ranar wata talata Inno ta fita sayo kaya,tun safe ta fita sai wajen Magriba ta dawo, yanayin ta kawai na kalla na tabbatar babu lafiya, a gefe kawai ta ajiye kayan ta fada banɗaki, ta jima ciki sannan ta fito, dakin ta ta wuce ta kwanta, ina ganin haka na mike na bita dakin, tayi nisa a tunanin ta na shigo, tana gani na ta tashi tana kokarin fita daga dakin,
"Inna bak'ya jin dadi ne?"
"Gajiya ce kawai, sai dan ciwon kai."
"Allah ya sauwake, bari na dauko miki paracetamol kisha."
Nace ina barin dakin, biyo baya na tayi, ni kuma na shiga daki dan dauko mata, a bakin rijiya na ganta tana alwala, tsayawa nayi ta gama sannan na bata maganin, balla tayi tasha ta wuce daki zuwa lokacin an fara kiraye kirayen sallah. Alwalar nima nayi na wuce daki dan yin sallah.
Tsawon sati guda kenan Inno na cikin zulumi, tun ina tambayar ta har na hakura na zura mata ido kawai ina alakanta hakan da yanayin jikin Baban.
Muna zazzaune a tsakar gidan ana yar hira, Baba na daga kofar dakin sa saboda yanayin da ake na zafi akan fito dashi shima yana shan iska. Shigowar bakuwar dauke da sallama ya saka Inno kusan sakin fitilar k'wan dake hannun ta.
"Harira!" Ta furta cikin tsananin mamaki
"Nice nan Innaro, kinga bakuwar daree ko?" Tayi maganar cikin wani irin salo dauke da yar karamar dariya.
"Muje ciki." Inno tace tana saurin fadawa dakin ta, bin bayanta tayi, a hankali naji an turo kofar dakin alamun an rufo ta, mamaki ne ya kamani, na dan muskuta kadan ina tunanin abinda ya kawo matar, a yanayin Inno kawai ya nuna batayi maraba da zuwan nata ba. Tsawon lokaci suka dauka sai tashin magana k'asa k'asa, chan suka fito tare, Inno sanye da hijabi suka fita tare. Har wajen tara shiru bata dawo ba, ina ta sake-saken abinda yake faruwa sai gata ta shigo. Bata yi wa kowa magana ba ta wuce ciki, har zan bi bayan ta sai kuma na fasa ina kunna Radio cikin wayata. Washegari na tashi bani jin dadin jiki na kwata-kwata. Tun bayan dana shiga wata na takwas nake jin wani iri, haka dai na lallaba na d'anyi abinda zanyi, na koma na kwanta. Shigowar Inno dakin yasa na tashi da kyar ina kallon ta, zama tayi a gefen yar katifar tawa, hankalin ta sam baya jikin ta. Kallon idon ta nayi naga yayi ja, sai duk naji babu dadi.
"Dan Allah menene yake faruwa inna? Kullum baki da nutsuwa kamar ma baki daa lafiya ne."
Gyara zaman ta tayi, ta dube ni a nutse tace
"Abubuwa ne da yawa suka tarar min Aminatu, sakamakon abinda na aikata ne yake bibiyata, dan Allah dan Annabi ki yafe min, na zalunce ki ban miki adalci ba, saboda son zuciya irin tawa, ki yafe min dan Allah..."
"Inna? Me Kika yi min haka har zaki bani hakuri, ni wallahi bakiyi min komai ba, iyaye ai basa taba laifi a wajen ƴaƴansu, nice ma zan nemi gafararki, watakila na miki wani laifin ne da yasa ki a halin da kike ciki."
"Kayya, Aminatu. Nidai dan Allah ki yafe min, kuma kiyi min alƙawarin zaki karbi hukuncin dana yanke akanki, shine kadai abinda zan miki na ceceki daga hannun azzalumai."
"Ban gane ba inna."
"Karki damu, yau in Sha Allah zakiji komai, banso sanar miki ba, amma ya zama dole idan ina so na samu sauƙin abinda na aikata."
Daga haka ta tashi ta bar dakin. Kasa binta nayi kawai ina tunanin maganganun ta, ban gane komai ba sai ma toshewa danaji ƙwaƙwalwa ta na neman yi. Mik'ewa nayi da nufin binta naji marata ta rik'e. Komawa nayi na zauna ina yarfe hannu. A hankali naji ta fara saki, na yunkura da kyar na fito, dakin dana gani a rufe yasa na gane ta fita, komawa nayi na haye saman katifa ta na cigaba da juyi ina tunanin maganganun.
La'asar likis ta shigo gidan a matukar gajiye, dakin da nake ta nufo, sallama kawai tayi ta shiga hade min yan abubuwa na waje daya, duk da dama ba wasu kaya bane masu yawa, cikin kankanin lokaci ta gama ta ajiye su a gefe sannan ta fita, cigaba nayi da kwanciyar kawai na zuba wa sarautar Allahu ido, chan ta shigo ta dauki kayan ta sake fita, bansan me hakan ke nufi ba. Da kyar na tashi na gabatar da sallah, idarwa ta kenan ko hijabin ban cire ba Inno ta sake shigowa, hannu na naga ta kama.
"Tashi Aminatu, lokaci na kurewa."
Mik'ewa nayi da d'an karfi na ta shiga jan hannun nawa, hanyar waje naga tayi dani, na cigaba da binta, motar dana gani ce yasa gabana faduwa, bude min tayi Na shiga sannan itama ta shigo, tana rufewa me motar yaja muka bar kofar gidan.
Tafiya mukayi sosai babu wanda yayi magana a cikin su har sai da muka fita daga kauyen namu muka isa babbar tasha, gefe ya samu ya faka ya kashe motar ya fita daga ciki ya bar mu. Yana fita Inno ta juyo tana kallo na
"Inna dan Allah me yake faruwa?"
Kasan kafarta ta zura hannu, sai ga jakar da ta jima tana ajiyar ta, akan cinyata ta ajiye min tana kokarin maida kwallar fuskar ta
"Gashi nan Aminatu, tabbas na zalunce ki, ban kyauta miki ba, na raba ki da dukkan farin cikin ki, ta hanyar rabaki da ainihin iyayenki...."
Ras gabana ya fadi jin abin tace, wani irin juyi naji cikana yayi, nayi saurin dafe wajen ina zaro ido
Bayan hannun ta tasa ta share fuskar ta
"Labari me tsawo Aminatu, sai dai wallahi tallahi yaudara ta sukayi, ba tare da sanin komai ba, na amince musu, nayi dana sani Aminatu, nayi dana sani tun ba yau ba, Allah ne shaida ta. Kiyi hakuri da abinda zan sanar dake, bani na haife ki ba, hasalima bansan iyayenki ba. Rana daya muka haihu da mahaifiyar ki. Sai dai ni haihuwa nayi da kaina ita kuma aiki akayi mata. "
"Watarana naje asibitin ganin likita, a lokacin cikina wata tara har da doriyar yan kwanaki, tare da kawata Harira data rakani, muka hadu da wata Hajiya, kana ganin ta kasan hamshakiyar mata ce, wadda ta jiku da kudi da jin dadi, yadda take ta kallon mu, yasa na dan zargu amma na share. Sanda muka zo tafiya ne ta tsaida mu, ta kira Harira gefe, sun jima suna magana har na gaji na zauna, sannan tazo muka tafi. Kwana biyu tsakani Harira ta bijiro min da maganar data firgita ni, da farko sam ban amince ba, amma yadda ya dinga kwadaita min abubuwan Alkhairin da zamu samu, naji na amince da bukatar su ta indai namiji na haifa zan basu, su kuma su bani tasu indai mace ce. Sai dai na kafa sharadin ba za'a dau lokaci ba zasu dawo min da d'ana, da farko matar bata amince ba, amma da Harira tayi mata bayani sai ta yarda. Bansan me ya faru ba ranar ina kwance sai ga Harira dauke da magani, ta kawo min wai nasha, ban kawo komai ba nasha, kafin wani lokaci na fara nakuda, da kanta ta dauke ni muka nufi asibiti, muna zuwa aka ce haihuwa ce aka shiga dani. Ban dau tsawon lokaci ba na haifo dana namiji, kukan sa kawai nake iya tunawa da yake min amsa kuwwa Harira ta dauke shi ta fita dashi, jim kadan ta dawo dauke da ke, da wannan jakar wadda ke dauke da manyan kudade masu yawa da tsoratarwa, haka ina ji ina gani aka tafi da d'ana, aka bar min ke. Bansani ba ashe Harira yaudara ta tayi, bata san su ba, bata taba ganin su ba sai ranar da muka hadun nan asibiti. Kiyi hakuri tabbas an zalunce ki, duk da bansan alakar ki da matar data tsara wannan abin ba, amma tabbas mahaifiyar ki bata da masaniyar abinda muka aikata."
Saboda tsananin kukan da nake muryata ko fita batayi, bansan a wanne mazauni zan dauki zancen na ajiye shi ba, ji nake kamar zan haukace saboda tsabar firgice, sama sama numfashi na yake fita. Duk addu'ar data zo baki na na shiga karanto wa, ina kokarin ganin na saita kaina
"Kiyi hakuri, tabbas na zalunce ki, ban kyauta miki ba. Bamu da lokaci Aminatu, ga jakar ki nan, da duk kudin dana karba wajen iyayenki, kiyi amfani dasu, domin sanar wa kanki rayuwa me kyau, Harira ta kulla wani babban abu, da bazan iya barin ta aiwatar wa ba, kuma bani da hujjar da zan ƙaryata ta, ko na nuna wa duniya ainihin wacece ita, rayuwar ki na cikin hatsari idan kika zauna anan, zan sauka na koma daga nan, ki kula da kanki, ki kula da kanki. Allah yayi miki albarka."
Kukan ne yaci karfin ta, ta shiga yin shi babu kakkautawa. So nake nayi magana, so nake nace wani abu, amma na kasa, na kasa samun harafi kwaya daya da zai samu zama akan harshe ne har na iya furta shi. Ina jin ta ta bude kofar ta fita, cikin dakiya tace
"Sai watarana Aminatu."
Sai a sannan naji karfi yazo min, na yunkura da sauri na balle murfin motar na fito.
"Inna..." Na kwala kiran da dukkan karfin muryar ta, chak ta tsaya, da tafiyar da take batare da ta juyo ba, k'asa daga kafa ta nayi, hankali naji wani abu kamar ruwa yana bina. Cigaba tayi da tafiyar ta, ina kallo ta bacewa gani na. A wajen na durkushe ina jin numfashi na yana barazanar barin gangar jikina.
Sama sama naji wani mutum yana min magana, ban iya amsawa ba, sai nuna masa motar nake da hannu na. Barin gurin yayi da sauri, chan ya dawo tare da wata mata.
"Taimaka Hajiya mu sata a motar chan bga kamar." Ina ji suka kamani, suka saka ni a motar, daidai lokacin me motar ya dawo.
"Kaine me motar nan?"
"Eh nina, tafiya zakuyi?"
"Eh, amma ga passenger ka nan babu lafiya ai, ka taimaka a mika ta asibiti kusa."
Lekowa yayi cikin motar, ganin yadda nake murkususu yasa shi firgicewa
"Kuyi hakuri gaskiya ba zan iya ba, sai dai idan kunyi niyyar taimaka mata ne toh."
Cikin bacin rai namijin yace
"Ashe baka da tausayi, baka ga halin data ke ciki bane?"
Da sauri ta dakatar dashi
"Anas karka dau zafi, ina ganin haihuwa ce, ya kamata muyi sauri taimaka sai a biya ka malam." Tace tana kokarin shiga motar.
"Muje toh tunda biya zakuyi."
Kwafa Anas yayi a bude motar a fusace ya shiga.
Ignore any error
#Rayuwar Aminatu. 💔💔🙏
Nagode sosai da addu'oin ku gareni, kunsan matsalar ido sai a hankali, yau tun safe nake typing ɗin nan ina yi ina ajiye a hankali saboda idon. Please bear with me Dan Allah 🙏
Ranoa: ©Hafsat Rano
(16)
★★★★★
Tsaki kawai yake har suka isa asibitin, zuwa lokacin na bana gane komai, tsananin azabar da nake ji tafi gaban a bayyana ta. Tun kafin motar ta gama tsayawa yayi saurin balle murfin motar ya fito yana kwala kira nurses din, da sauri daya ta ƙaraso wajen motar, suka taimaka aka fito dani, kujerar da ake dora mara lafiya aka saka ni akai, aka nufi labor room dani. Fitowa nurse din tayi ta bashi list ɗin abinda ake bukata, da sauri yaje ya siyo a cikin asibitin ya kawo.
Tsawon lokaci aka dauka ina fama, nasha matukar wuya kafin na haihu, ina haihuwa na suma cikin tsananin wahala. A wannan lokacin suka gyara min jikina ba tare da nasan me ya faru ba.
Sama sama naji suna kiran sunana, a hankali na fara dawowa, ido na ya sauka akan jaririyar dake kwance bisa kirjina, babu ko kaya a jikin ta, kura mata ido nayi, kuka take sosai da dukkan karfin ta.
"Ga tana tabarakallah, lafiyayya kuwa."
Naji nurse din na fad'a wa abokiyar aikin ta. Rasa a wannan matsuguni zan ajiye wannan ranar, ranar da nake gudun zuwan ta, duk kuwa da na hakura na barwa Allah ikon sa, sai gashi tazo min a bai bai, cikin yanayin da ni kaina ba zan iya tantance shi ba, bani da kowa yanzu kenan? Sai wannan jaririyar da bata san komai ba, yanzu ne ma zata fara sanin abinda ke kunshe cikin duniyar nan. Hawayen da bazan iya banbance na farin ciki ne ko na bakin ciki ba suka shiga bin fuskata, ina ji suka cire ta daga jikina, suka shiga gyara ta. Dakin hutu aka maida mu, suka shigo a tare, kallon su nake har suka ƙaraso inda nake, Hajiya ta dauki yarinyar cikin farin ciki, ta shiga jera min sannu.
"Masha Allah, Allah ya raya ta."
"Matso ciki mana ka ga jaririyar." Tace tana kallon sa, yana tsaye jikin kofar yana kallon ciki, a hankali ya tako, ya ƙaraso gaban ta ya leka cikin shawul ɗin da aka rufe ta, murmushi naga yayi, a hankali ya furta
"Tabarakallah Hajiya, kinga baby me kyau kamar a bani."
Dariya ta saka
"Kai fa Anas na manta son yara ne dakai."
"Wallahi Hajiya. Ina son yara."
"Allah ya baka masu albarka."
Da sauri ya amsa
"Amin Hajiya ta."
"Ja'iri." Tace tana dariya. Kallo na tayi
"Baiwar Allah ya kamata ki kira yan uwanki, kinga mu akan hanya muke, idan yaso ko zuwa gobe ne sai mu wuce, nasan ma dai goben zasu sallame ki tun da kalou kike ai."
Ido na ne ya cicciko jin abinda tace, wa zan kira? Bayan bani da kowa a yanzu, wayar ma ko dauko ta banyi ba, ganin yadda duk suka kafa min ido yasa na wayance nace
"Ba anan suke ba, a Kano suke."
"Kano? Toh ai muna yan chan ɗin ne, idan kin yarda damu sai mu tafi tare gobe da safen, idan yaso sai dai su ganki da babyn ki."
"Allah ya kaimu goben." Nace ina kokarin boye damuwa ta. Ido na ne ya sauka akan