Showing 45001 words to 48000 words out of 112633 words
Chapter 16 - DAURIN GORO COMPLET book 1 by Hafsat Rano.txt
ina yar hamma,
Altine ce ta shigo dauke da Kaskon wuta, ta ajiye ta koma ta kawo kayan wanka, komai sabo hatta bawon wankan da dangin su sabulu, daukar ta tayi, tayi mata wanka hade da gashin cibiya, kafin ta gama dakin ya dau dumi, turaren wuta Ramlah tasa mana ta zauna tana cin abinci tana yi min hira.
★★★
Harira na zaune rike da d'an karamin mudubi tana duba fuskarta, shirya take tsaf daga gani fita zatayi, ajiye komai tayi a gefe ta yafa sabon mayafin ta, tana yan wak'e wakenta cikin farin ciki ta fito, turus tayi ganin yan sanda a tsakiyar gidan nasu, kowa ganin abinda ya kawo su, bata kawo komai akanta ba tayi wajen su, cikin son nuna ita din wayayyace tace
"Lafiya dai?"
Maganar da tayi yasa Farouk juyowa, da sauri yace
"Arrest her."
Babu wani bata lokaci suka damke ta, tana ihu tana komai suka tusa ta cikin bayan motar, sai a sannan ta lura da Inno kanta a sunkuye ta rufe fuskar ta da mayafin kanta. Wani irin amsawa kirjin Harira yayi, cikin tsananin tashin hankali tace
"Innaro?"
"Ko ba ita bace?" Ta maimaita jin ta mata banza, bata amsa mata ba, har suka isa charge office, fito dasu akayi aka watsa su cikin wani ɗan karamin cell kafin ya tura Garbati a cikin nasa shi kadai.
"Zan dawo, kar kuma ku bawa uban kowa belin su har sai sun bqyyana inda suka kai min matata da jariri na.
Da sauri suka amsa ya juya ya bar wajen, Ja'afar na bin sa haka suka koma gida, be kula takan maganar da Ja'afar din yake ta masa ba ya fada daki da sauri ya saka key, misscals ɗin Dadah ya tarar, sai yaji zuciyar sa ta karye, yasan yadda ta damu da Aminatu idan taji labarin nan hankalin ta ba karamin tashi zai ba, fasa kiran ta yayi ya ma kashe wayar baki daya yana bin dakin nasu da kallo, dakin da sukayi rayuwa a ciki, rayuwar da yake ganin ta cikin wasu muhimman lokutan da yayi masa matukar muhimmanci a rayuwar sa. Ji yayi zuciyar ta ta bushe, ta k'ek'ashe, ba zai taba kyale duk wanda yake da hannu ba, ko da kuwa mutanen dake da kusanci mafi rinjaye dashi. So yake yayi kuka da idanun sa, ko yaji dadi a zuciyar sa, sai dai yasan abu ne me matukar wuya a yanzu, lallai zubar da hawaye idan kana cikin damuwa ma Rahma ne.
Sai yamma likis ya tashi daga inda yake, istigfari yayi hade da dauro alwala ya gabatar da sallar azahar da la'asar. Jawo wayar sa yayi ya kuna, ya danna kiran wayar Dadah don yasan tabbas tana cikin son jin abinda yake faruwa. Bugu daya ta daga, da sauri tace
"Babana me yake faruwa? Kun barni cikin tashin hankali."
Share zufar kanshi yayi, murya a ciki-ciki ya soma mata magana, salati kawai take har ya kai karshe, zuwa lokacin gaba daya komai ya fara tsaya mai, yunwa, tashin hankali da wani abu daya tokare masa makoshi ne suke barazanar kaishi kasa, kiran sunan shi take sai dai baya jin komai sai chan a saman kanss, ya gaza amsawa, a hankali idanun sa ke rufewa, kadan-kadan kafin su rufe baki daya yana sakin wayar wadda karar faduwar ta, ta saka Ja'afar tasowa da gudu ya hau dukan kofar. Jin shiru yasa shi firgicewa yayi dakin Dadah da gudu ya nemo spare keys, a gaggauce yazo ya bude shi, da sauri ya k'arasa wajen sa yana jijjigashi, ganin da gaske baya hayyacin sa yayi saurin dauko ruwa ya shafa masa a fuska, ajiyar zuciya ya sauke da karfi yana bude idon sa da suka rine sosai, taimaka masa yayi ya dora shi saman gadon kafin ya fita don dauko wayar sa. Daddy ya fara kira no answer, sai ya kira Mummy ita din ma babu amsa, shiru yayi yana tunanin wanda zai kira kuma, daga karshe ya yanke shawarar kiran Dadah, a rikice ta daga kiran nasa dan dama suna magana da Farouk din ne taji shiru.
Dakin Ja'afar ya komo bayan sun gama wayar, har lokacin idanun sa na bude ya kura wa saman dakin ido.
"Ya Farouk!" Ya kira sunan shi,
"Dadah tace karka sa damuwa a ranka, da cewa tayi ma xatazo nace a'ah zamu taho ma gobe."
"Waye aka ce ya kawo takardar nan?" Ya jeho masa tambaya still idanun sa na kallon sama
"Wacce kenan?"
"Takardar dake rubuce da sakin, waye ya kaiwa Aminatu?"
"Ban sani ba gaskiya, a yadda naji,makaranta aka je aka kai mata."
Shiru yayi cikin dogon nazari kafin yace
"Shikenan, koma waye zan gano ai."
"Kabi komai a sannu Please."
"Karka damu, zaka iya wucewa kawai, zan dan zauna anan ko na sati daya ne."
"Babu matsala idan na Barka? Baka jin dadi naga."
Girgiza masa kai yayi kafin yace
"Idan ka fita ka jamin kofar Please ina son zama ni kadai."
Juyawa dayan barin yana sake gyara kwanciyar sa, dan jim Ja'afar din yayi kafin ya ja masa kofar kamar yadda ya bukata
Dare ya tsala sosai, yayi zurfi a cikin tunanin sa,duk kokarin sa nason ganin ya samu ko da wani haske ne a binciken sa abun ya faskara, juyi kawai yake yana tuna halin da Aminatun ke ciki.
Da safe ya shirya sukayi sallama da Ja'afar ya tafi, duk da baya jin dadin jikin sa da zuciyar sa, amma haka ya danne ya nufi station din don yana son magana da Inno. Fito da ita akayi yayi mata yan tambayoyin da suka shige masa duhu, game da wanda ya kawo takardar sakin. Yadda ta sanar masa yasa kansa ya k'ara daurewa, wacece wannan da zatayi masa haka? Menene tsakaninsu? Mutun daya ya ke tunanin zata aikata hakan, Mummy, sai dai ya kara shiga matukar damuwa daya nuna mata hoton Mummyn amma tace ba ita bace.
Gidan Maigari ya nufa, sai dai shima bayanin d'aya ne mata ne su biyu suka zo wajen sa, sai dai shi be nuna masa hoton na Mummy ba ya daiyi godiya kawai ya tafi.
Duk inda yake tunanin zai kai ga neman ta, yayi, ya sare sosai yana jin kamar rayuwar sa zata k'are. Gidajen Radio da talabijin duk ya kai musu cikiya hade da hoton ta, dan baya taba tunanin zatayi nisa da Katsina, duk binciken nasa a iyakar nan din ne.
Tsawon sati guda kenan yana bincike akai hade da neman ta, duk inda yake tunanin zai same ta har gidan principal yaje, gaba daya ya rame ya lalace kamar bashi ba.
Yana zaune kiran Daddy ya riske shi, a kasalance ya daga yana karawa a kunnen sa gami da sallama
"Farouk, me kaje ka aikata a gidan su yarinyar nan, maigari ya kirani akan kaje har gida kasa an kama mahaifiyar yarinya tsawon sati daya kenan, wai kai yaushe zakayi hankali ne ehe?"
"Daddy ba abinda kake tunani bane..."
"Kai kullum abinda zaka sani magana shi kake yi, ya kamat kasan kai ba yaro bane yanzu."
"Ba haka bane... Ayi hakuri dan Allah."
"Awa uku na baka, kaje ka fitar dasu sannan ka baro garin, kayi abu ya dame ka shine zaka je ka huce akan bayin Allah, Awa uku ka bar garin nan ka dai ji na fada ma."
Bin wayar yayi da ido, ya rasa me yasa har yanzu Daddyn ya gaza aminta dashi balle ya fahimce shi, har yanzu bashi da ikon kansa. Ba ya taba barin sa ya kare kansa, komai yayi bai iya ba, komai yayi sai fada. Mutum daya ke tsayawa ta saurare shi tun yana yaro har zuwa yau, mahaifiyar sa da ita da babu banbancin su kadan ne, bata san komai ba sai kasuwanci ta, bata da lokacin su tun ma kafin rabuwar su da Daddy balle yanzu da take ganin sun girma.
A gurguje ya shiga hada kayan sa, yana yi yana ayyana hukuncin da zai yanke wa kansa, hakan ne kawai mafita a garesa, baya jin zai iya sake zaman wasu awowin a cikin garin. Duk abinda yasan zai bukata ya tattare su, waya kawai ya daga ya kira sifetan yan sandan wajen yace ya sake su, loda koman sa yayi ya rurrufe ko ina ya damka wa Baba maigadi yan mukullayen gidan ya dauki hanyar Kano.
Shigar dare yayi, Dadah na cin tuwo ya turo kofar ya shigo yana jan kafar sa, da kallo ta bishi cike da tausaya wa, har ya zauna gefen ta yana tankwashe kafarsa
"Babu wani labari ko?"
Tace tana tsame hannun ta, girgiza mata kai yayi bakin sa ya gaza furta kalma daya, tashi tayi ta wanko hannun ta tazo ta zauna gefen sa, da sauri ya dora kansa a saman ƙafar ta. Tun yana yaro haka yake mata, idan baya jin dadi ko kuma ransa ya ɓaci, fasa tambayar sa komai tayi. Sai daya gaji dan kansa sannan ya mike ya nufi daki, bata hana shi ba, tasan lallai yana bukatar kadaici, addu'a ta bishi da ita kawai tana fatan komai ya warware cikin sauki.
Ko da ta tashi da safe tuni ya fita, sai gabannin azhar sannan ya dawo gidan, kwana uku yana jeran fita a rana ta hudu yace mata zai je Lagos, bai sanar da ita abinda zai je yayi ba, haka ya tattara ya tafi, a ranar ne ita kuma ta dauki hanyar Shagari don samun magana da Inno.
***
Satin sa biyu a Lagos ya dawo ya wuce Kaduna gidan Mummyn su, duk ya sake ramewa kamar ba Farouk ba, ita kanta data ganshi sai data ji babu dadi, ta shiga tambayar shi abinda ya same shi. Wanka yayi ya shirya kafin ya same ta a zaune a falon ta na alfarma. Tana zaune kafarta saman tuntu tana hutawa.
Maimakon ya zauna a kujerar data ke nuna masa sai ya zauna a k'asa, cikin yanayin da ta kasa ganewa ya soma mata magana
"Kiyi wa girman Allah Mummy, ki sanar dani gaskiya, ba zargin ki nake ba, sai dai zuciya ta, ta kasa nutsuwa, ina son sanin da hannun ki a duk wani abu daya danganci Aminatu? Dan Allah ki taimaka ki fadan gaskiya, kaina ya kule, na rasa waye zai aikata min hakan? Iya sani na ban sake ta ba, amma me yasa na kasa wanke kaina daga daurin da akayi min?"
Murmushi tayi kafin tace
"Farouk kenan, bani da masaniyar komai, haka zalika ban aikata abinda kake tunani ba, mesa zan boye kaina idan har ni ce na raba ku? Karka manta ni mahaifiyar ka ce, tsarin rayuwa ba zai sa na manta matsayi na ba, idan har ina son na raba ku, kai tsaye zan sa ka sake ta, bisa karfin iko na da matsayi na wajen ka."
"Kiyi hakuri, ba ina zargin ki bane, kiyi hakuri dan ALLAH."
"Karka damu, bani da masaniya akan ba kaine ka sake ta ba, bayan na samu labarin a wajen Ja'afar, ban yi niyyar zuwa ba, sai dai text message dana samu ne yasa ni zuwa dole, tun da sakon na nuna cewa ka saki yarinyar sannan Daddyn ku yaje domin ya maida auren, bayan kuma kace kai bakaa so, hakan yasa na tafi, a ganina hakan zai sa na hana abinda yake shirin aikata maka karo na biyu."
"Text?Waye ya aiko shi?"
"Ban sani ba, dan nima tun a ranar na kirkira number ba,tq shiga."
"Zan iya ganin number."
"Ok bari na duba, ina tunanin ban goge message ɗin ba ai."
Gyara zaman sa yayi ta dubo masa number, da sauri ya dauki Number ya kira, ringing daya biyu aka daga, sai dai muryar data bayyana a wayar ta sake sashi a wani rudanin, bayerabe ne ya daga, cikin harshen sa na yarabawa, dole ya kashe yana jingina da kujerar dakin.
Kwana ɗaya yayi mata yace zai tafi, taso ya d'an kara zama sai dai yace mata zai dawo nan kusa, haka ya tattara ya wuce Kano, nan dinma kwanan sa biyu, ya komo abuja.
Jiran Daddy yayi har ya dawo ya same shi a falon sa, gaishe shi yayi a mutunce ya amsa kafin ya nemi izinin sanar dashi abinda ya kawo shi.
"Na yanke shawarar ajiye aikina, zan koma karatu a karo na biyu, na nemi izinin ajiye aike, sai dai sam shugaban mu ya ki amince wa, shine nake rokon ka saka baki dan Allah."
"A wanne dalilin zaka ajiye aikin ka?"
"Akwai matsi da takura sosai, sannan ina son chanja akalar rayuwa ta ne, zuwa mutumin da zaka yi alfahari dashi a gaba."
Da sauri ya kalle shi, sai kuma yayi murmushi
"Kana tunanin yanzu bana alfahari da kai?"
Be ce komai ba, ya sunkuyar da kansa kasa,
"Shikenan, zan yi magana, duk abinda ka zaba wa rayuwar ka, ina fatan hakan ya zamo Alkhairi a gareka."
Sosai yaji dakin maganar, da sauri ya amsa da amin yana jaddada kansa a k'asa cikin tsananin farin ciki
"Sai dai akwai sharadi guda daya..."
"Ina so ka amince da auren kanwar ka Amal, hakan shine kadai buri na akan ka yanzu, idan kayi min shi nasan ka cika d'a nagari."
Da wani irin shock Farouk din yake kallon shi, daga mishi kai yayi cikin gasgata abinda yace ya dora
"Idan har kana son ka samu damar barin aikin ka, ka tafi duk inda kake son tafiya tun da nasan kudurin ka na barin k'asar ne, toh tabbas sai ka auri Amal, idan yaso sai ku tafi tare, daga nan har karshen duniya bani da matsala da kai."
Juyawa kansa ya hau yi, idan har shawarar sa ta kauracewa kowa na nufin auren sa da Amal, da kuwa ya sani be dauki wannan shawarar ba, sai dai ya sani Daddy ba zai taba kyale maganar ba, tun da har ya riga ya furta, idanun sa ne suka shiga dauko masa hoton Amal, duk da yana son ta, yana jin ta sosai a ransa, amma ba hakan na nufin zai iya auren ta ba, aure a irin wannan lokacin da bashi da nutsuwar zuciya, idan yayi haka be wa Aminatu adalci ba.
"Zaka iya zuwa kayi shawara sosai, zuwa nan da lokacin da zuciya ka zata zaba maka abu daya, sai dai ka sani, abu daya tak zan iya yi maka, in ma ka hakura da kudurin ka naa son nisanta kanka damu, ko kuma ka yarda da auren yar uwarka, zabin ya rage naka."
Tirkashi!!!
Shin za'a yi auren nan?
Yaya rayuwar Aminatu zata kasance a gidan data samu kanta?
Sai yaushe zasu hadu da Farouk?
Waye yake ma Farouk makarkashiya?
Ina labarin d'an Inno ne wai?
Yaushe a kuma wanne irin yanayi Aminatu zata hadu da iyayenta?
Leggo🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚵🚵🚵🚵🚵🚵Hansatu R
20
ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER*
07067124863
*Ko kuma*
09032345899
*ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sababbi,karku manta ku dannan SUBSCRIBE kuyi LIKE sannan kuyi SHARING*🙏🏽
https://youtu.be/Zyl7_eSgXuo
★★★★
Kasa tashi yayi har zuwa sanda Mama ta shigo, da kyar ya ja kafafun sa ba tare da yace komai ba ya fito. Amal na tsaye a gaban part din su kunnen ta sakale da waya tana amsawa, tsayawa yayi chak yana kallon ta daga nesan, ya sani sarai Amal bata da matsala, zai iya cewa ma rainon sa ce, amma ya gaza gano dalili d'aya da zai iya bashi damar auren ta, takawa yayi har wajen da take, ya tsaya daga bayan ta yana son ya gano wani abu, cire wayar tayi daga kunnenta cikin farin ciki ta juyo, ganin sa tsaye yasa ta dan yi sak, sai kuma ta fadada fara'ar ta
"Yah Farouk, dama kana tsaye?"
"Umm. Ina tsaye ina jinki kina waya da siriki na."
"Ni?" Ta zaro ido tana dafe kirjin ta
"Da fa Ilham muke magana."
"Ahaap, idan ma dai boye min shi kike shikenan, anyway zo muje ina son magana dake."
Gaba yayi ta bi bayan shi cikin tarardadin abinda zai ce mata ɗin, part dinsu ya shiga, ya zauna saman kujera cikin sanyin jiki ta zauna gefen sa tana kallon sa.
"Kina da wanda kike so?"
Tayi saurin dagowa,
"Yes... Idan har akwai wanda kuke magana dashi, let me know, ni kuma zan yiwa Daddy maganar."
Marairaice wa tayi kamar zatayi kuka tace
"Ni dai babu kowa Allah."
'Dan jim yayi kafin yace
"Kin tabbata?"
Daga mishi kai tayi tana sake kwabe fuskar ta, girgiza kansa yayi ya furta
"Shikenan ba damuwa, kije kawai."
"Ya Farouk!" Ta kira sunan sa ba tare da ta tashin ba, maida kallon sa yayi kanta yana jiran yaji me zata ce, wasa ta soma da hannun ta kafin ta daure tace
"Mamaa tace min zaka aure ni, shiyasa bana kula kowa."
A mamakan ce ya bita da ido har ta bar dakin da sauri, janye hannun rigar sa yayi cikin rashin sanin madafa ya jingina kansa da jikin kujerar yana lumshe idon sa.
Kwana uku a tsakani yana ta tunanin mafita, ya rasa yadda zai ɓullo wa al'amarin, idan har yace ba zai aure ta ba, toh tabbas kamar ya dasa wani babban abu ne tsakanin sa da mahaifinsa, wanda bashi da wani buri sai na ganin ya faranta masan.
Muskutawa yayi yana sake kiran Number a karo na ba adadi,magana d'aya ce babu wani sabon bayani game da neman nata, tsaki yaja yana ajiye wayar, chan ya sake dauka ya danna wa Dadah kira, bata daga ba har ta gama ringing, zamewa yayi a wajen ya mike kafar sa yana fatan komai ya zama masa da sauki.
Yayi nisa cikin tunanin da yake na kokarin ganin ya samu mafita, ganin yana kara bata lokaci yasa shi mik'ewa ya sauya shigar sa zuwa kayan motsa jiki, mota ya fada ya nufi wajen motsa jiki. A chan ya dade ba tare da ya dawo gida ba, sai daya ji ya gaji sosai sannan ya juyo gidan.
Part dinsu ya wuce kai tsaye, Ja'afar ne zaune da sauran yaran gidan suna buga game d'in wot, idanun sa ne suka sauka akan Amal dake zaune cikin su ana yi tare da ita, ransa ne ya ɓaci, ya daka mata tsawar data saka dukkan su firgita, hannu ya nuna mata kofa yana jin kamar ya kikkifa mata mari, gaba daya wannan wani sabon hali ne da be san ta dashi ba, duk da sukan yi hakan a lokacin yarinta, amma yabzu fa? Sam ba zai yarda da wannan shashancin ba, dole ya taka wa