Showing 69001 words to 72000 words out of 112633 words

Chapter 24 - DAURIN GORO COMPLET book 1 by Hafsat Rano.txt

07 Aug 2025

7427

da kukan nata, tissue ya ciro ya mika mata

"Menene matsalar ki?"

Ya tambaya yana dago ta,

"Ya Farouk." Tace cikin muryar kuka. Murmushi yayi mata yana jingina ta jikin kujerar motar

"Karki damu, ki koma karatun ki, zan san yadda zanyi."

"Yaushe? Daddy fa ya gama sanin komai, kuma ya fada wa Dadah."

"Akwai lokaci, akwai lokaci."

Yace yana tada motar.

Shiru tayi tana tuna abubuwan da ya jima yana fada mata, haushin kowa take ji, babu wanda zatayi wa uzuri a cikin su, duk kuwa da sun yi mata sosai a rayuwa amma ba kamar mahaifin daya kawo ta duniya ba. Idan bata tsaya masa ba bayan kowa ya juya masa baya wa zai taimaka masa? Ita kenan daya mallaka a duniya dolen tane ta share masa hawayen sa.


***Tsawon makwanni biyu ya dauka a garin kafin ya tattara ya koma inda ya fito, itama Amal sai ta koma can Abuja don karatun ta ta cigaba da rayuwar ta kamar babu komai. Duk da lokaci zuwa lokaci sukan yi waya amma babu wanda ya san da hakan sai Mama kawai, shiyasa ma bata da matsalar komai dan kanta tsaye take abubuwan ta tun da sau tari ma a wayar Maman zai kira bayan sun gama magana sai ta bata.
Alaka ce mai karfi tsakanin su, sai dai ta gaza gane wacce irin alaka ce hakan da har tasan sirrin sa.


***
Dukkan kokarin Daddy na son ganin ya samu wani bayani ta wajen Mummy sam ta ki bashi fuska, rashin sanin yadda zai ɓullo mata ne da yadda yake mata gadara yasa ta kafe itama, zuciyar ta, ta riga ta k'ek'ashe shiyasa bata wani jin shakku ko wani abu game da hakan.

Tun yana tunanin jan aji ne irin na mata har ya gane da gaske take ba zata saurare shi ba, duk baya jin dadin komai, tun bayan rabuwar su da auren da yayi bayan lokacin da kadan bai taba jin wani abu game da ita ba sai yanzu da girma yazo.
Duk da Mama na kokari sosai wajen kula dashi amma ya kasa yakice ta daga ransa. Mai yasa ya kasa mata uzuri a wancan lokacin? Ya kasa gane dalilin sa na yin hakan, gashi yanzu ya fada kogin nadama da dana sani mara amfani.

****
*Farouk*

Aiki yake sosai babu kama hannun yaro, sosai yake jin dadin aiki da Mr Johnson shiyasa bashi da wata matsala da kasar.
Zuwa lokacin da ya fara karatun sa ya riga ya tara kudade masu yawan gaske, duk da haka duk weekend yana zuwa ya zauna a wajen hakan kuwa ba karamin dad'i yake ma Mr John ba dan shi a rayuwa yana son mutum mai kwazon aiki.
Da gangan Farouk ya zamar da kansa agogo baya bada lokacin sa a komai sai neman halal dan yayi wa kansa alkawarin ko zai koma gida ba zai taba bari ya rabi da kowa ba balle har ayi masa wata alfarma.
Batun mutumin nan kuwa, tun ranar bai sake haduwa dashi ba, sai ya tattara shi ya watsar ya rungumi sana'ar sa da karatun sa.

***A gurguje ya sauko kasan shagon tun bayan daya samu sakon supervisor din sa akan yana son ganin sa, dole ya tattare aikin da yake waje daya ya nufi makarantar.
A daidai gate din shiga ya hange shi, da motar sa ya fara gane shi, sai dai yau ba shi kadai bane hadda mace da yara, da sauri ya tsallaka bangaren su yana tsaida su, kamar ba zai tsaya ba sai kuma yaga yaja ya tsaya dage gefe, karasawa yayi cikin sassarfa yana kokarin ganin fuskar sa.

"Assalamu alaikum."

Yayi sallama kai tsaye, a tare suka amsa dukkan su, kafin namijin ya juyo da dukkan fuskar sa yana duban shi, duba na tsanaki.

A wani irin yanayi suka hada baki a tare kamar wanda maganar tazo wa a lokaci daya cikin yanayin dake kama da an fuzgota suka ce

"Farouk!"

Ware idanun sa yayi, duk da karancin shekarun sa ba zai taba mantawa dasu ba, mutane biyu masu kusanci dashi, daya kani ne ga mahaifin sa, daya kuwa kanwa ce ga mahaifiyar sa. Mai suke anan? Me yasa babu wanda yake tunawa dasu? Babu wanda yake maganar su. Bayan har da d'an da suka tafi suka bari. Ja'afar! Mai yasa suka manta da kowa suka zo nan suka kafa sabuwar rayuwa. Bashi da amsar ko daya daga cikin wadannan tambayoyin, shaf ya manta da abinda ya kawo shi makarantar, da sauri ya fada motar yana kallon yaran guda uku dake zaune a bayan motar suma suna kallon sa.
Sautin kukan Anty Safiyya ne ya sake dagula masa lissafi, kuka take sosai sai dai babu wanda yace uffan har suka isa gida. Daga kai yayi yana karewa gidan kallo, tsawon wannan shekarun suna rayuwar su su kadai ba tare da dangi ba. Mai yasa?




★★★★
Rayuwa ta cigaba da garawa cikin hukuncin Ubangiji, idan baku manta kuduri na ba, ba zai wuce na cikar buri na ba, karatu na nasa a gaba babu wani abu daya sauya na daga yadda rayuwar tawa take
  Yadda komai yake wanzuwa cikin hukuncin Allah, zaka tabbatar da babu mai tsara bawa ƙaddarar sa face Allah SWA.
Hakan ce ta kasance dani, a yau na rubuta jarabawar karshe ta makarantar horar da lauyoyi dake garin bagauda (law school). Idan na tuna matsayin karatun da nayi a daya daga cikin manyan jami'oin Nijeriya (BUK), na kan ji wani nishadi mara misaltuwa, ban taba hasashen hakan ba, sai gashi Allah ya hukunta min cikin manyan kaddarorin rayuwa ta.

Anas ya zama wani babban jigo a karatu da rayuwa ta, sannan Kamal daya zama mafi kusanci dani da yarinyata
Tun ina tunani ko hasashen zan hadu da wani daga cikin ahalin su Farouk har na daina sai dai har lokacin yana makale a kahon zuciya ta. Duk sanda na kalli Iman na kan tuna dashi da komai nashi.

**Sanda sakamakon jarabawar ya fito sai dana yi kuka, kukan farin ciki saboda yadda result din yayi kyau ainun, wai yau nice rike da shaidar zama cikakkiyar lawyer, Anas yaso yafi ni farin ciki saboda a daidai lokacin ne Hajiya ta amince masa da aure na, duk da abin yazo min a wani irin yanayi amma nayi kokarin boyewa na biye masa wajen nuna farin ciki na, y'an kwarya kwaryar walima ya shirya min daga ni sai shi sai Iman, Baba Altine da Ramlah sai kawayen ta biyu, ban gayyaci kowa ba a yan makarantar mu, duk dama babu wata shakuwa tsakanin mu sai abinda ya shafi karatu.
Kamal tun daya koma ban sake saka shi ido na ba sai dai muna waya sosai dashi.
Komai ya sake chanjawa bayan gama karatu na, kai tsaye Anas yake zuwa a matsayin zance. Mutum ne shi da yake bin komai a tsare, dan haka bai taba ketare iyakar sa ba, komai yanayin sa ne a addinance babu jahilci. Hakan na kara birgeni dashi, yadda yake tafiyar da rayuwar sa cikin tsari abin so ne.

****
*Waye Shi!*

Hannu na sakale dana Iman muke zagaye supermarket din, Alk'awari nayi mata idan har ta iya wasu surori zan kai ta, ta zabi abinda take so, da kanta ta fada wa Anas aikuwa sai ga kudi ya aiko mana dashi.
Doguwar riga ce bud'addiya a jikina, na yane kaina da madaidaicin mayafi, takalmin kafata irin flat shoe ne, babu yadda za'a yi daga kallo daya ka gane wacece ni ko daga ina na fito, jikina ya murje sosai na zama cikakkiyar mace ta kowanne fanni. Bamu da matsalar komai saboda Anas ya tsaya mana.
Mun bata lokaci sosai kafin mu gama saboda yadda Iman ta tsaya ruwan ido,sai dana gaji nace tafiya zanyi sannan ta hakura, napep muka tara muka nufi gida lokacin duhu ya fara sauka.
Muna cikin tafiya wayata tayi kara, ciro ta nayi ganin Kamal ne yasa na daga.
Magana muke wanda ta dauke hankali na har muka kusa wuce inda zamu sauka, da sauri na tsaida me napep din muka sauko na mika masa kudin har lokacin wayar na makale da kunne na.
Kasancewar har anyi magriba tasa layin babu kowa, da hannu daya na rike wayar da kayan dayan hannu na rike Iman dake min mitar na bata wayar su gaisa, tafiya muke a kafa ina cigaba da amsa wayata ban bi ta kanta ba.
Kamar walkiya haka naji an fizge hannu na dake hade da nata, kafin nayi wani yunkuri an watsa min wani abu mai matukar yaji da radadi a idanuwa na, bansan lokacin dana saki kara mai karfi ba cikin tsananin azaba na durkushe a wajen.
Ina jin sahun digadigan su, ina jin ihun Iman mai haɗe da kiran sunana, a birkice na tashi ina laluben ta, tsananin duhun daya mamaye ido naa yasa na kasa aiwatar da komai.
Ƙarar tashin motar su kawai naji, na sake yunkura wa da dukkan karfi na, sai dai ban yi ko da taku daya ba naji an shaka min wani abu da yasa na daina gane komai.


Rano

Manage 🚴🚴🚴🚴🚴🏇🏇🏇

Dukkan masu kwamplain an daure su, kuyi hakuri za'a kunce ku a hankali, zaku gane kan komai. *DG*

                       *31*

★★★★★
Kukan da nake ya dawo hankalin mutane wajen, da sauri wani makocin mu daya shaida ni ya karasa gida ya kira Baba Altine, a kideme ta fito babu ko mayafi, tana gani na ta hau salati tana kuka. Zuwa lokacin radadin da nake ji ba kadan bane a idanuwa na, kama ni aka yi da taimakon wani Alhaji ya bada aron motar sa aka dauke ni zuwa asibitin.
  
Kamal a rude ya fito daga dakin sa, part din Iyayen sa ya nufa riga a hannu yana kokarin sakawa, Ammi na zaune ta tallafe fuskarta da hannun ta ya shigo a kid'ime.

"Ammi ina Daddy?" Yace a rude yana kallon ta.

"Menene?" Tace tana tashi tunanin ta wani abun ne ya faru.

"Kano zan tafi, akwai matsala."

Yayi hanyar fita daga falon, da sauri ta riko shi, tana kallon yanayin sa

"Kana da hankali kuwa? A daren nan? Wai menene ma ya faru?"

"Ban sani ba wallahi, kawai muna magana da Aminatun,  naji ihu sai kuma na daina jin komai, ina ta kira kuma wayar bata shiga."

"Yarinyar da ka bani labari? Har yanzu kuna tare kenan."

"Ammi pleaseeeeee, suna bukatar taimako wallahi, bari kawai naje wajen Old Woman nasan ita zata fuskance ni."

"Tsaya." Tace tana daukar wayar ta, Alhaji Marwan ta kira, bai dauka ba har ta katse, ta sake kira sai ya biyo ta da text message suna wani meeting ne zai kira. Ajiye wayar tayi tana kallon dan nata

"Ka yi hakuri mahaifin ka ya dawo kamal, yanzu dare yayi."

"Amma..."

"Dan Allah, I can't risk loosing u, kasan dai yadda tafiyar dare take, ka bari kaje by flight idan Allah ya kaimu, yanzu ka duba available flight da time."

Kamar zaiyi kuka amma dole ya hakura ya koma dakin sa, tsawon daren kiran wayar ta kawai yake amma bata amsawa, haka dai ya hakura yana ta Allah Allah gari ya waye ya je ya gani, ya rasa dalilin daya sa ya damu da ita sosai da al'amuran ta.

***
Idan nace muku na runtsa tsawon daren toh nayi karya, kafin safiya idanuwan sun haye sunyi suntum, bana ko iya bude su ga bakar azaba, duk da wannan tunani na na wajen yata, waye wannan da zai sace ta, wai me nayi wa mutane ne har haka da ba zasu barni nayi rayuwa ta ba, iya sani ba bani da wani abokin gaba ko fada, amma me yasa hakan ke kasancewa dani.
    Shigowar Anas dakin tare da yan sanda yasa nayi shiru daga kukan da nake na zuci, dan likita ya hanani kuka saboda idon nawa zai kara rikicewa.
  Tambayoyi sukayi min suka fita, kamshin turaren sa daya sake kusantoni yasa na gane ya matso sosai

"Sannu." Yace yana dora hannun shi saman goshi na. Bance komai ba,zuciya ta ta riga ta karye, ina ji kamar numfashi na zai yanke na bar rayuwar baki daya. Shiru ne ya biyo baya, ina jin motsin sa yana taba abu a jikin gadon, kafin yace

"Ina zuwa."

Yana fita Baba Altine ta shigo Kamal na biye da ita, kamar wadda wani dangi ko dan uwanta ne yazo haka naji, duk sai naji komai na sake bijiro min, mantawa nayi da kashe din likita na shiga rera kuka sosai suna bani baki, shigowar likitan ya katse min kukan da nake, tare suke da Anas, ganin Kamal a dakin ya dan sha jinin jikin sa kafin ya basar yana sauraron bayanin likitan.
   Aiki za'a shiga dani na gaggawa, saboda haka aka wuce dakin gwaje gwaje, babu wanda ya matsa nan da can a cikin su har zuwa lokacin da sakamakon ya fito. Daga nan aka wuce dani zuwa dakin theatre domin gudanar da aikin.

****
Daki ta shiga da sauri ta hau harhada kayan ta, har lokacin kuka take, yaran na tsaye bakin kofa kowa yayi shiru jiki a matukar sanyaye suke duban mahaifiyar tasu, idan da sabo sun saba duk lokacin da abin ya motsa sai anyi da gaske take hakura, sai dai yau zuwan wannan bakon ya so saka su a tunani, iya sanin su babu wanda yake zuwa musu da sunan dan uwa ko wani dangi, haka nan suke rayuwar su daga su sai iyayen nasu biyu.
   Shigowar Abban nasu dakin hannun sa rike dana Farouk yasa suka matsa gefe suna jiran suji mai zai faru.
   Anty Safiyya na ganin sun shigo tayi saurin rufe akwatin kayan ta tahau jan ta da sauri tana nufo su, kama hannun Farouk tayi cikin kuka tace

"Wuce mu tafi, ba zan sake zaman ko da awa biyu bane a garin nan na gaji!"

Gam ya rike hannun mata idanun sa na kadawa, duk da har lokacin ya kasa tunanin abubuwan da yadda suke sai dai tsantsar tashin hankalin da yake gani a idanun uncle Aliyu kadai ya isa ya gane akwai gagarumar matsala. Mai yasa tsawon wannan lokacin babu wanda ya nemu su?"

A gefen gadon ya zaunar da ita, ya rike mata hannu yana durkusawa a gaban ta, ganin taki daina kukan yasa hannu ya shiga share mata hawayen kafin yace

"Dan Aallah ki daina kuka, idan kina kuka mu fa? Dukkan mu zaki saka muyi kuka."

"Ina Ja'afar?" Tace tana share hawayen nata

"Ja'afar yana nan cikin koshin lafiya."

Girgiza kanta tayi

"An min adalci kenan? A rabani da d'ana tsawon wannan shekarun ba tare da ya ganni ba Farouk?"

"Kiyi hakuri."

Uncle Aliyu ne ya matso jikin gadon yana rike mata hannu

"Safiyya... Nasan kina dauka ta a cikin mutane mara sa adalci da son kansu ko? Kina tunanin na rabo ki da kowa naki na kawo ki nan, ki sani bani da zaɓi da ya wuce hakan, ba'a son raina hakan ta faru ba."

"Kullum magana daya kake, baka da zaɓi, baka taba zaunar dani ka sanar dani abinda ya kamata na sani ba, taya kake tunanin zan yadda da kai?"

"Bani da ikon sanar dake ne, sai dai a yanzu komai ya wuce, ni kaina ina bukatar ganin dangi na, dana kasa kare su na tsaya musu sanda suke da bukata ta, musamman Anty Abidah."

Cikin zumudi tace

"Kana nufin zamu koma gida?"

Daga mata kai yayi

"Tsawon lokacin nan ina jiran wannan ranar ne, duk yayi min ikirarin ba zan taba ganin ranar ba, sai dai ban fitar da rai ba, ina ta addu'a Allah ya kawo min karshen halin da nake ciki, Safiyya ba haka kawai na zauna anan ba, akwai babban dalilin da ya rike ni har wannan lokacin."

Juyawa yayi yana duban Farouk

"Ya akayi kazo nan, ga dukkan alamu ba yanzu kazo ba,yanayin ka ya nuna ka jima a kasar, menene ya faru?"

Ajiyar zuciya Farouk ya sauke yana jin an tabo masa tsohon mikin zuciyarsa, sai dai dole zai sanar musu komai saboda ga dukkan alamu Uncle Aliyu ya san wani abu dasu basu sani ba , sai dai kafin nan yana bukatar amsar tambayar dake nukurkusar zuciyar sa

"Ina da dalili babba na barin kowa na dawo nan da zama, sai dai na kasa auna fahimta ta a sanda na ganka, tun zuwa na farko kasar nan na fara haduwa dakai Allah be sa zamuyi magana ba, me yasa tun bayan tafiyar ku, babu wanda ya kuma neman ku, yasan inda kuke ko yayi maganar ku?"

Murmushi Uncle Aliiyu yayi ba tare da ya amsa ba ya jeho masa wata tambayar

"Tun tasowar ku ka taba ji ance maka yau ga Kawun ka Adam yazo?"

"Ina tunanin Uncle Adam ya rasu tun muna yara ai ko?"

"Eh ya rasu a idon duniya sai dai be rasu a idanun Aliyu ba, yana nan da rai yana yawo a doran kasa."

Zaro ido sukayi a tare da Anty Safiyya, ta tashi tsaye tana kallon mijin nata cikin rawar murya tace

"Ya akayi hakan ta kasance?"

"Babu amsar wannan tambayar taki sai a gaban mutanen da hakkin sanin hakan ya wajaba akan su, dole sai mun tabbatar da hakan ta hanya gamshashiya ba ta fatar baki ba, ƙaryata labarin mutuwar da ya dauki tsawon lokaci da wucewa ba abu bane me sauki. Musamman a wajen mutane irin su Adam wanda babu digo na imani a ransu."

"Tabbas akwai rudani a cikin wannan maganar Uncle Aliiyu, sai dai hakan yasa na fara wani tunani da hasashen wasu abubuwa ciki har da abinda ya faru dani, ina so zan sanar maka da komai da ya faru bayan tafiyar ku, ina nufin abinda ni ɗin zan iya dorarwa akai ba wanda ban sani ba, daga nan zan baka labarin abinda ya sa na dawo nan ɗin, ina fatan hakan ya bani haske a abun da na jima ina tunani da hasashen wanda yake da hannu a ciki."

"Madallah da kai, hakan ne zai taimaka mana kwarai wajen sanin ta ina zamu tabbatarwa da duniya abinda ya jima yana boye."

"Ina fatan haduwar mu ta zama warwawar manyan daurukan da suka dade a daure, ina fatan ya zama silar wanzuwar farin ciki a zukatan mutane da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login