Showing 39001 words to 42000 words out of 112633 words

Chapter 14 - DAURIN GORO COMPLET book 1 by Hafsat Rano.txt

07 Aug 2025

7451

jakar nan, wani yawu me kauri na hadiye ina tunanin abin yi. Babu inda ta bar ya Farouk, komai nasa ne, hatta yatsun kafarta dana hannun ta nasa ne, hawaye na share a hankali ba tare da na bari sun ganni ba.
Fita Anas yayi ya nufi masallaci, ya bar mu a dakin muka karasa kwana, da safe wajen tara aka sallame mu, mota yaje har tasha ya samo mana, aka zuba kayana muka dauki hanyar Kano a karo na farko a rayuwa ta.


***Isar Inno gida tana kokarin shiga yayi daidai da tsayawar motar, Harira ce ta fito kafin daga bisani matar da suke tare ta fito ita ma. Juyowa tayi tana kallon su, fuskar ta a yanayi me wuyar fassara wa. Karasowa sukayi suka tsaya mata a gaba, Harira tayi dariya sannan tace

"Yau dai ga uwar yarinya nan, sai ki bata ita ta tafi da ita, ki gode wa Allah ma da bata ce zatayi karar ki ba wallahi, dan haka salun alum ba sai kowa yaji ba, shiga ki fito da ita."

Kallon banza tayi masu a tare kafin tace

"Ashe ma ni mahaukaciya ce kamar ke, kina tunanin bayan kinzo kin same ni da maganar banzar ki zan sake amince miki har na sake wani gangancin? Kije duk inda zaki ki tona min asiri, na riga na shirya wannan ranar tun kafin zuwan ta."

"Kina nufin me kenan?"

"Abinda kike tunani."

"Baki yarda da abinda nace ba kenan?"

"Ai yadda dake tun ranar da na gano cuta ta kikayi, a ranar na cire ki daga sahun mutane masu hankali, kuma a ranar na daina yarda da duk wani mutum a doran kasar nan."

"Ina wai yarinyar take?" Matar ta tambayi Harira tana yatsine.

"Kina ji ai ko? Ki shiga ki fito da ita, kinga shiyasa ma muka zo da daddare muyi komai cikin sirri, in Kuma so kike kowa yaji ne toh?"

"Idan kinga dama, ki dauki abin magana ki zagaye duk garin nan ki sanar musu, a nan ne zan gane cewa baki da mutunci."

Daga haka tayi shigewar ta gida, tsaye Harira tayi tana kallon matar, cikin bacin rai ta juya ta nufi mota tana mita

"Kinsan bata min lokaci zakiyi kika kawo ni, bayan kin tabbatar min an gama magana."

"Ja muje kawai aikin banza."

Da sauri Harira tayi wajen motar, kafin ta k'arasa sun ja sun bad'e ta da kura, bin su tayi da gudu tana kwala kiran ta amma basu tsaya ba. Zage zage ta shiga yi cikin bacin rai.

★★★
A gurguje ya hada komai, ya rurrufe ko ina ya fito, baki daya tsawon zaman da yayi a wajen cikin rashin kwanciyar hankali yayi shi, kafatanin tunanin shi na wajen ta, duk da dai yasan ya bar ma mutane biyu amanar komai a hannun su wanda yake tunanin ba zasu taba yi masa ba daidai ba, amma hankalin nasa sam yaki kwanciya, har zuwa yau da suka samu yancin barin wajen, sosai yayi dana sanin shiga aikin soja, aikin da zai raba ka da kowa naka idan ba girma kayi a cikin sa ba, tsawon lokaci ba tare da anji daga gareka ba, babu service balle ka kira wani, idan ma akwai baka da kwanciyar hankalin kiran.
Babbar mota ce sumfurin Hilux suka cika kayan su a ciki, suka dauki hanya. Ife ife ne kawai ke tashi a motar cikin yaren su na sojoji, kowa da abinda ya dame shi wasu ma waka suke bi cikin nishadi da murnar zuwa gida. Kallon su kawai yake ba tare da ya sa musu baki ba, daya gaji da hayaniyar tasu sai ya kwanta kawai ya lumshe idon sa yana jin farin ciki da daukin zuwan nasa gida.
Sanda suka iso Abuja, dare ya soma yi sosai, bashi ya samu isa gida ba sai bayan sha biyu na daren.
Rataye yake da jakar goyo irin babbar nan, sai yar karamar trolly daya riƙe yana jan ta a kasalance, ya ɗan buga gate din, sojan dake tsaye kofar ne ya leko, da sauri ya bude cike da mamaki sa, gaisawa sukayi ya wuce ciki kai tsaye, ganin dare yayi ya sa ya wuce bangaren su, ya tura kofar bakin sa dauke da sallama. Ja'afar na zaune a kan sofa Yana danne dannen waya yaji an turo , dagowa yayi da nufin ganin waye, cikin tsananin tashin hankali wanda yasa saura kadan ya saki wayar hannun sa ya furta

"Ya Farouk!"

Murmushi yayi,

"Kana mamaki ne? Ko ka dauka na mutu ne?"

"Wai yanzu kazo? Yanzu yanzu zuwan kenan?"

"Ga zahiri ka gani, malam karbi kayan ka kaimin daki mana ka tsare ni da tambaya."

"Auw." Yayi saurin karbar kayan yayi hanyar dakin dasu, shi kuma ya fada saman kujerar yana sakin ajiyar zuciya.

"Home sweet home." Ya furzar da iska me dadi kafin ya tashi ya nufi fridge, ruwa ya dauka ya koma ya zauna yasha, sannan ya ɗan mike kafar sa. Jin shiru shiru Ja'afar be fito ba yasa shi kwala masa kira, a zabure ya fito kamar mara gaskiya.

"Kai kuma daga ajiye jaka sai ka zauna, bayan kasan dole zan tambaye ka."

"Bacci ne ya soma dauka ta, afwan, ya hanya ya komai?"

"Normal."

Dan zamowa yayi daga kujerar kadan yana fuskantar shi

"Allah yasa dai abinda na saku kaida Amal kunyi min shi babu shirme ciki, nasan ma dai babu abinda zai sa kuyi min hauka, dan zan iya komai akai wallahi."

"Na'am..?" Ya zaro ido

"Yadda kaji, yanzu dai bari na kwanta, da safe ka shirya da wuri mu wuce, kasan i can't wait any longer."

Tashi yayi wuce daki, a hankali Ja'afar ya zame a wajen yana jin wani mugun tashin hankali. Da sauri ya jawo wayar sa ya hau kiran Amal, har ta katse bata daga ba, haka yayi ta jera mata kiran duk kuwa da yasan ba dole ne ta daga ba, duba da dare yayi.
A falon ya kwana, ba tare da ya runtsa ba, duk kuwa da yasan dole zai dawo dama, amma beyi tunanin dawowar shi a wannan lokacin ba. Lallai akwai matsala babba, matsalar da zata iya haifar da komai.


Manage pls🙏 Yau ruwa yayi mun duka jama'a 😣😣🙄 Saura naji wata tayi min dariya🤫😬
8a:             Daurin Goro*

             *17*

© Hafsat Rano

ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER*

07067124863

*Ko kuma*

09032345899

*ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sababbi,karku manta ku dannan SUBSCRIBE kuyi LIKE sannan kuyi SHARING*🙏🏽

https://youtu.be/Zyl7_eSgXuo
               

17

★★★★★★
Cikin yanayin da ke bayyana tsantsar farin cikin sa ya tashi, mika yayi hade da salati, kafin ya fada toilet a gaugauce. Be dau lokaci ba ya fito, ya hau shiryawa cikin kaya mafi tsada da kyau, yana yi yana kallon kansa a mirror, murmushi ya saki da ya tuna inda zashi, shigar manyan kaya ce a jikin sa, wadda suka fito da zahirin kyawunsa na bakattsinen asali. Lekowa yayi falon da nufin kira Ja'afar, wayam babu kowa sai kalacin dake zube a saman centre carpet din dake ajiye a tsakiyar falon, tsaki yaja ya fito, ya nufi main part din gidan yana karewa ko ina kallo. Kicibis sukayi da Amal dake shirin fita a yanayi me wahalar fada, da sauri taja baya, cikin yanayin rashin gaskiya tace

"Yahh..."

Murmushi ya sakar mata kafin yace

"Suprice!"

"Saukar yaushe?"

"Jiya kina ta bacci, nasan lokacin kin kai Australia ma dan nasan ki da shegen bacci."

"Waye nake gani kamar Farouk?"

Ta katse su tana fitowa daga kitchen rik'e da babban tea flask me dauke da kunun tsamiya.

"Nine wallahi Mama, ina kwana?"

"Ah laillai maraba da manyan sojoji, sannu da zuwa ya hanyar?"

"Alhamdulillah walalhi ,sai kewar gida, sam aikin nan ba dadi wallahi."

"Toh ya za'a yi, ka gaisa da Daddyn naku dai ko? dan yanzu yake shirin fita."

"Aiko yanzu nake shirin shiga bangaren nasa, bari nayi sauri dan nima Kano zan tafi."

"Za'a je a gano Hajiya kenan, toh karbi flask din nan ka tafi masa dashi, bari na dauko sauran kayan."

"Ko da yake ma..." Ta kalli Amal dake tsaye kamar munafuka tana sauraron su tace

"Daughter zo ki dau sauran kayan ki kai masa na karasa wani aiki anan."

***Tare suka jera yana tambayar ta bayan tafiyar sa, amsawa take har suka karasa part din Daddy, wayar ta dake cigaba da k'ara ta sake katse wa a karo na ba adadi, dariya Farouk yayi

"Sirikin nawa ake wulakantawa ne?"

Sai ta kalle shi da sauri, girgiza kai tayi suka shiga falon a tare, Daddy na zaune ya shirya cikin shigar sa kamar ko yaushe, da tsananin mamaki yake kallon Farouk din har suka ƙaraso ciki, ajiye kayan sukayi akan food mat din da ake jera masa kayan abincin kafin kowannen su ya zame ya zauna, Amal ce ta fara gaishe shi, kana ta mike kamar wadda ake mintsina ta fice da sauri, tana ji Ya Farouk yana bata sakon ta kira masa Ja'afar tayi gaba kawai ba tare da ta amsa ba.

"Barka da Safiya."

Ya furta cike da karsashi ba tare da ya gama karantar yanayin Daddyn ba. Be amsa ba, sai ma wurgo masa da tambaya yayi cikin dakewa yace

"Sai yanzu kake nuna fuskar ka anan ko?"

Kai tsaye yace

"Ayi hakuri Daddy, wallahi tafiya ce ta taso a ranar, na sanar da Ja'afar amma ya fada maka, bayan na kirkira wayar ka ban samu ba, tun da muka shiga jejin nan babu service wallahi, sai jiya da Allah yayi muka fito lafiya."

"Toh... Tafiyar ce ta saka ka yanke d'anyen hukuncin daka yanke kenan? Bayan haka ka nuna min kaine ka haife ni, ka watsa min k'asa a idon duniya ko? Ka kyauta.."

Cikin rashin fahimta yace

"Allah ya baka hakuri Daddy, amma sam ban gane abinda ake magana akai ba, ka gafarce ni dan Allah."

"Rainin wayon naka har ya kai haka? Lallai wuyan ka ya isa yanka."

Kasa yayi da kansa, yana ji Daddyn ya mike, ya shige bedroom d'insa, kasak'e yayi yana tunanin inda maganganun suka saka gaba, sai dai ya kasa gano ko daya. Fitowar Daddyn yasa ya dago, a fuskar sa ya jefa masa takardun guda biyu, kana yace

"Idan kai kana shaye-shaye toh ni garau nake, kuma da hankali na idan kai mahaukaci ne, idan baka gane maganar fatar baki ba, ai zaka gane rubutu ko?"

Da sauri ya dauki takardar ya hau budewa, bakin sa na karanto duk addu'ar da tazo masa, takardar shaidar cikin dake dauke jikin ta ya fara budewa, a take wani matsanancin farin ciki ya lullubeshi, wanda ba zai iya kwatanta shi ba, da k'warin guiwar sa ya bude dayar yana cike da yakinin abinda yace karo dashi a ta farkon na da alaƙa da ta biyu, a wani irin yanayi ya dago hade da mik'ewa tsaye.

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Ya furta da karfi yana nuna wa Daddy hannu ba tare da ya iya furta kalma daya ba

"Sannan bayan ka cimin mutunci ta hanyar sakin ta, ka kuma ƙaryata cikin dake jikin ta, shine har kake da gut din takowa inda nake, bansan kuma me kake so ka sanar dani ba."

Da sauri ya dire akan ƙafarsa, yace

"Ban aikata ba, ban aikata daya daga cikin abinda ake tuhuma ta dashi ba a karo na biyu wallahi ban aikata ba, bani da masaniyar komai.."

"Rubutun jiki fa? Ko shima zaka ce min ba naka bane?"

Ya watso masa tambayar yana masa kallon banza, sake kalla yayi da kyau, tabbas rubutun sa ne, me hakan ke nufi? Kira ne ya shigo wayar Daddyn, ya daga yana amsawa kafin yayi hanyar waje kawai ba tare da ya kalli jerin abinci da aka ajiye masa.
  Kamar mahaukacin zaki haka ya fito daga shashen, da sassarfa ya isa bangaren su yana kwala wa Ja'afar kira. A zaune ya tarar dashi yana karin kumallo cikin kwanciyar hankali. Watsa masa takardun yayi a hargitse yace

"Kayi min bayanin me ya faru, bayan tafiya ta, ina amanar dana bar maka?"

"Ya Farouk calm down, nayi maka bayani."

"Wanne irin calm down, kasan me kake fada kuwa?" Ya fada a hargitse

"Owk, bayan tafiyar ka, ranar da ka fada min zasu gama exams, muka dau hanya, mun yi nisa sosai har mun wuce Kano ma amma da kadan, motar mu ta samu matsala, abinda yayi delay dinmu kenan gashi yamma tayi and wajen da muke babu abin hawa balle me gyara, da kyar muka sami wani bawan Allah ya juyo damu Kano, muka bar motar a can, washegari Daddy yazo da maganar sakin, bansan me ya faru ba naji dai suna magana da Dadah, the following day muka tafi Shagari tare da Dadah."

Dafe kansa yayi cikin tsananin tashin hankali yace

"Ja'afar, Saki ni? Na sake ta? When, how? Mesa bana tuna komai? Ka yarda zan sake ta kaima kamar Daddy?"

Girgiza masa kai yayi

"Ban yarda ba Ya Farouk, sai dai rubutun da ya zama naka, shi yafi bani mamaki, ya akayi hakan ta faru?"

"Someone is behind this, WallAhi sharri aka kulla min, wani ke son ganin bayana."

"Amma Ya Farouk..."

Ƙarar shigowar messages wayar yasa yayi saurin kallon ta, ta saman notification bar ya ga alamun video aka turo masa ta whatspp, whatspp ɗin ma da ya manta rabon sa dashi, hankalin sa ne ya tafi zuwa son ganin abinda video din ya kunsa, a gaggauce ya danna load, ya zuba wa wayar ido yana jin kamar zuciyar shi zata fashe, cikin kankanin lokaci ya gama loading, videon ya bude. Shine zaune, gaban sa ɗan karamin centre table din dake falon su, rike da papper da biro, rubutun ya kura wa ido, take abinda ke rubuce a takardar hannun sa ya bayyana a faifan video ɗin, shine zaune yana rubuta wa Aminatun sa saki, cikin kwanciyar hankali, jefar da wayar yayi saman kujera yana sakin numfashi da karfi.

"It's a trap Ja'afar, na shiga uku."

Da sauri Ja'afar ya isa wajen wayar ya dauka yana kallo, rubutun tar hade da fuskar Farouk din sanda yake yinshi a cikin falon nan nasu, girgiza kai yayi yana shirin ajiye wayar sakon audio ya shigo, kunna wa yayi muryar Farouk din ta karade ko ina a lokacin da aka kira shi. Sanda yake ƙaryata maganar cikin, zabura yayi ya fisge wayar yana sake saurara, tabbas shine yake magana, amma yaushe hakan ta faru? Ya kasa tuna daya daga cikin ranakun da hakan ta faru. Da sauri ya fada dakin su, ya hau birkice komai na dakin, babu komai sai tarin kayayyakin su da takardun su na makaranta, a hargitse ya sake fitowa, rike da mukullin motar sa dake hannun Ja'afar tun tafiyar sa, da sauri ya tare shi ganin kamar ba a hayyacin sa yake ba

"Barni Ja'afar, Kano zan tafi, daga can na dau Dadah mu tafi wajen ta, ba zan iya zama ba, idan har lissafin cikin jikinta da date ɗin da akayi daidai ne, toh tabbas ta haihu, ko kuma tana kusa da haihuwa, ya kake tunanin zata iya daukar wannan tension din da ciki."

"Let me come with you, ba zaka iya driving ba."

Mika masa car key din yayi ya fada saman kujerar idanun sa sun kada sosai, burin sa daya ya isa gareta, yayi mata bayanin komai. Cikin kankanin lokaci Ja'afar din ya fito bayan ya chanja kaya, suka dauki hanyar Kano.

****
Dadah na zaune hannun ta rike da waya tana sake gwada kiran, karo na biyar kenan tana kira ba'a dagawa, gashi sam hankalin ta yake kwanciyar.  kanwarta Fatsim tayi wadda suke kira da Umma Fatsim, tace

"Yaya wai kiran ne har yanzu?"

"Kinga har yanzu ba'a daga ba, gashi sam hankali na yaki kwanciya wallahi, Allah yasa lafiya."

"Toh amin, amma nake ga ai idan ba lafiya ba zasu kiraki su sanar miki, ki kwantar da hankalin ki babu abinda zai faru sai Alkhairi."

"Allah yasa, anjima sai na k'ara gwadawa."

Hira suka cigaba da yi sama-sama, har zuwa lokacin da aka bude gate din gidan, ta window ta zuge labulen ta leka,

"Ja'afar ne."

Tace tana sakin labulen, da sallama suka shigo, kallo daya zakayi wa Farouk kasan baya hayyacin sa, shine a gaba Ja'afar na take masa baya.

"Babana!"

Da sauri ya karasa gabanta, kamar karamin yaron dake gaban mahaifiyar sa, haka ya dora kansa a saman kafarta yana jujjuya kan kamar wanda ke shirin zaucewa

"Me yake faruwa Ja'afar?"

"Kamar yadda kike tunani ne Dadah."

"Bani nayi ba wallahi Dadah, bani ne ba, sharri aka kulla min, I'm trapped bansan ya zanyi ba."

Dago kanshi tayi

"Mik'e Babana, nasan dama ba zaka taba aikata ba."

"Nasan dama ba zaki yadda ba, ke kadai ce kika yadda dani, amma ni kaina yanzu Dadah ban yarda da kaina ba, na kasa tabbatar wa kaina bani ne na rubuta ba, rubutu na ne, magana tace Dadah, waye zai min wannan? Ko dai ni na aikata ban sani ba? Amma ta yaya? How comes bana iya tuna komai ne?"

"Ba zaka taba aikata abinda zai zama cuta ga Aminatu ba."

Ciro wayar sa yayi, ya mika mata videon yana girgiza kansa

"Nine a videon nan, da hannu na na rubuta sakin Dadah, da hannu na na rubuta, bansan sanda na fara shaye-shaye ba, amma tabbas bana hayyacina sanda na aikata hakan, tabbas yaudara ta akayi, aka sani na rubuta ba tare da na sani ba, sai dai na kasa tuna komai, bana tuna komai Dadah, kaina kamar zai fashe nakeji, zuciya ta namun zafi, idan har akwai mutumin da yake son ganin bayana a duniyar nan, toh tabbas Aminatu tana cikin matsala, zanje na ganta, zan bata hakuri, nasan zata amince dani ko kowa be yarda ba."

"Kaje ka ganta, tana bukatar ka fiye da kowanne lokaci, abinda ke cikin ta na bukatar ka."

Mik'ewa yayi cike da karfin sa, ya juya ya bar falon Ja'afar na take masa baya. Shiru ne ya biyo bayan fitar su, zuciyar Dadah cike da farin cikin dawowar Farouk a lokacin data tabbatar Aminatu na bukatar sa.

★★★★
Tafiya ce mara daɗi musamman gareni, duba da rashin sabo da kuma danyan jegon da nake ciki, kuka yar jaririyar da bansan takamaimai sunan ta ba, ta saka tana wutsul-wutsul da kafarta, dauke kaina nayi daga ɓangaren Hajiyar, ina kallo ta hau jijjigen ta, sai dai bata da alamun yin shiru.

"Aminatu,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login