Showing 48001 words to 51000 words out of 112633 words

Chapter 17 - DAURIN GORO COMPLET book 1 by Hafsat Rano.txt

07 Aug 2025

7418

Ja'afar birki dan shine babban banza, idan ba haka ba ace duk cikin su basu san abinda ya dace ba,yadda zamanin nan ya sauya, yan uwan da suke uwa daya uba daya ma shaidan na iya tasiri akan su, ballantana ita da take ba muharramar su ba, ya lura kanta na rawa sosai da yadda suke shige wa juna tsakanin su. Dole yayi wa tufkar hanci ba zai yarda su kara masa wani ciwon kan aakan wanda yake fama dashi ba.
A kufule yayi hanyar daki wanda tun kafin ya kai ga yi musu magana duk kowa ya dare ya kama gaban sa.
    

★★★
Idan nace ina da matsala ta zamantakewa ta da wadannan bayin Allah nayi karya, duk wani abu da zamu bukata nida Iman sai dai mu ganshi.
  Sai dai har yanzu zuciya ta ta gaza daukar nauyin abubuwan da ke cunkushe a cikin ta, duk da ina kokarin dauke damuwa ta ko dan yawan fadan Hajiya a gareni, Amma Tabbas ba karamin abu bane a gareni, mutanen da ka sani a matsayin dangin ka, rana daya a tabbatar maka da babu wata alaƙa tsakanin ku, mesa tun da ta kasa daukar haske a kan hakan duba da yadda Inno take mata, sai a yanzu wata maganar da Babarsu Harira ta taɓa fada mata ke dawo mata, Inno bata taɓa shayar da ita ba, a lokacin ta dauki hakan a matsayin wata lalura kila data hana hakan, sai gashi yanzu ta gane babban dalilin ta nayin haka, ba zata ce ta cuce ta ba, amma tabbas bata kyauta mata ba, bata yi mata adalci da d'an data haifa ba.
   Bata da wata hanya ta neman mutanen dake da muhimmanci a rayuwar ta, Farouk, Dadah, da mahaifanta. Yaushe zata gansu? Ta riga tayi ma manta alƙawarin ba zata sake komawa garin na Shagari ba har sai sanda ta tabbatar wa kanta shine daidai lokacin daya kamata ta koma din.
  Turo kofar akayi aka shigo hade da sallama, dan gyarawa tayi tana kallon sa, a saman kujerar dakin yayi wa kansa masauki cikin kamala yace

"Ya jikin naki?"

"Alhamdulillah." Na maida nasa

"Allah ya saka da Alkhairi." Na dora, nasan abinda yazo gani, tsam na mike na dauki Iman na isa gareshi, hannu ya mika da nufin daukar ta hannayen mu suka hadu waje daya, da sauri na janye nawa ina sauke kaina kasa, kallo na yayi na yan dakiku kafin yayi murmushi yana maida hankalin sa wajen ta, hanyar fita nayi daga dakin bakin daya saboda ba zan iya zama ni dashi kadai ba, yau ne ma rana ta farko daya taddani a dakin ni kadai, ban kai ga fitar ba ya dakatar dani da maganar sa

"Dawo magana zamuyi."

Da baya na dawo na koma inda na tashi na zauna, shiru ne ya biyo baya, ya cigaba da rikon Iman ba tare da yace komai ba, duk sai naji na takura, dagowa nayi da niyyar ganin abinda ya hana shi maganar, idanun sa a kaina suna yawo, da sauri nayi kasa da kan ina ji na a matukar takure.

"Akwai abinda kike bukata ne?"

Kai tsaye nace

"A'ah..." Sai kuma na tuno da maganar kudin nan, tashi nayi na bude inda na ajiye su, na dauko na dire a gaban sa.

"Dama... Dama idan ba damuwa ina so ko zaka ajiye min kudin nan, idan yaso duk abinda za'a bukata sai ayi a ciki."

Da wani irin kallo ya bini

"Kamar me za'a yi dashi?" Ya tambaya yana kallo na, kin yarda nayi mu hada ido nace

"Amm.. ko za'a siya ragon da za'a yi mata hakika wai dama."

"Aka ce miki ban siya ba? Bana bukatar kudin ki, nayi niyya ne ba wai dan wani dalili ba, nayi ne saboda Allah da ya halicce mu, kuma ya umarce mu da mu taimaka wa wanda yake bukatar taimakon."

Daga kaina sama nayi, sai naga kamar ransa ya ɓaci, ajiye Iman din yayi a saman gadon ya juya zai bar dakin, sai kuma yaja ya tsaya yana juyowa

"Idan kina bukatar inda zaki ajiye ne, zaki iya bude account sai kisa a ciki duk abinda kike bukata sai kiyi a ciki."

Daga haka yasa kai ya fice, shiru nayi ina tunani, ni banga abin fushi a magana ta ba, sai dai dukkan alamun sa sun nuna haushi yaji, ya zanyi toh ni? Me laifin abinda nace?
  Ko da Hajiya ta shigo, sai ta hau min fada, kar na sake maganar duk abinda za'a yi wa Iman din, dan shi mutum ne mai saurin harzuk'a, na bata hakuri tace ya wuce. Tun daga lokacin bana taba cewa komai har idan bashi ne ya yanke ba, sati ya zagayo  aka yanka mata abin yanka kamar yadda addini yace.
   Sosai muke zaman mu lafiya da Ramlah, kasancewar ta mutum me faran faran da son mutane, Iman kuwa dukkan dawainiyar ta a wajen su take, idan tana makaranta Hajiya amma da zarar ta dawo shikenan ita zata dora.
Slip dina na ciro na post Utme d'ina na duba, date da komai, Ramlah na bawa ta gani kafin tace zata je ta kaiwa Ya Anas, har ta tafi kai masan ina tunanin amincewar sa, ina zaune ta dawo da fara'ar ta,

"Ya kukayi?"

"Yace kije da kanki wallahi, dama nasan haka zai ce wallahi."

"Na shiga uku, wallahi kunyar sa nake ji Allah."

"Toh kuwa sai ki hakura wallahi."

Tsaki naja na tashi ina daukar mayafi na, baki daya sun kasa gane yanayin da zuciya ta take ciki, kokarin su na son ganin lallai sai na sake dasu, bani da yadda zanyi, haka na fito falon ina wara ido, a hakimce yake a saman kujera ya ajiye laptop a gaban sa yana aiki, be dago ba duk da yaji sallamar danayi masa, a ciki ya amsa yana cigaba da danne dannen sa hankali kwance, rasa ta ina zan fara masa magana, sai dana juya iya kalmomin da zan iya fada masa sannan na soma magana a hankali, har na kai aya be fasa abinda yake ba, be kuma kalle ni ba, sai kawai ya ture laptop din yana daukar slip ɗin nawa, dubawa yayi ya ajiye, ya sake jawo laptop din sa ya cigaba da aikin gaban sa. Mik'ewa nayi tsam nayi hanyar dakin zan koma naji yace

"Allah ya kaimu, best of luck."

Cigaba da tafiya ta kawai nayi ba tare da na tsaya ba, nayi shigewa ta ina turo kofar, Ramlah na riƙe da Iman tana jijjigen ta, ba laifi akwai rigima idan ta fara kuka har sai kan mutum yayi ciwo, karbar ta nayi na yi mata abinda nasan zai sata shiru, da haka na dora sabon tunanin mutum daya tamkar da dubu wanda ya zama min kamar wata al'adah ta yau da kullum.

****
Daddy be sake neman sa ba, kamar ma ya bar maganar gaba daya, har aka soma kiran sa na gaggawa a wajen aiki, ranar yana hanyar Kano kiran ya riskeshi, ba tare da sanin madafa ba ya isa gidan na Dadah. Sai daya ci abinci ya huta sannan ya sanar da ita halin da ake ciki, ta jinjina lamarin duk da ta fara cire rai akan ganin Aminatu nan kusa, sai dai ba zata taba hanashi auren Amal ba, da shi da ita dukkannin su nata ne, babu wanda zata zaba sama da wani, dadin dadawar maraicin yarinyar, duk da babu laifi Maman na kokarin kula dasu, sai dai rashin uwa tun kana d'an karami ba abu bane me sauki.
Abu daya ta dogara dashi a halin yanzu shine Exams d'in da Aminatun zatayi wanda tabbas tasan idan har tana da rai da lafiya ba zata kasa zuwa ba, idan kuwa haka ne zatayi amfani da wannan damar wajen ganin ko za'a dace.
Sanda ta sanar masa da kudurin ta, murna ya hau yi, kamar ance an ga Aminatun ne an gama, duk da babu sanin takamaimai ranar da zata je ɗin, sai dai a hakan zasu duba ko Allah zai sa a dace d'in.
Bincikowa yayi ya samu date ɗin da za'a yi dukka Exams din da venue, ya had'a komai intact yana jiran ranar.

★★★
Ranar labari shine ranar da zatayi ta ta Exams din, tun ranar Monday suka fara jelar zuwa makarantar, daga nan suyi nan har la'asar babu alamun ta, haka suka koma gida washegari ya komo shi kadai ba tare da Dadan ba, nan ma haka ya gama zagayen sa daga nan zuwa nan har aka gama baki daya, ya sha wuya matuka sosai haka ya hakura babu komai a cikin sa ya koma gida yana fatan samun dacewa.

Karfe 9 zamu shiga hall saboda haka da wuri na shirya, Ramlah ma ta shirya don dama sunyi hutun makaranta, shirya Iman akayi saboda zamu biya ta banki daga makarantar, tare muka fito suna zaune da Hajiya yana shan tea, kallo daya yayi mana ya maida hankalin sa kan abinda yake yi, zama mukayi ya karasa Hajiya na dan jana da hira, tashi yayi yana mika min kofin kafin yayi hanyar fita

"Sai mun dawo Hajiya."

"Allah ya bada sa'a, sai kun dawo."

Kitchen na nufa na ajiye kofin na dawo mukayi mata sallama Ramlah na rungume da Iman muka fita.
Yana zaune cikin mota ya kunna ta,muka shiga ya ja muka bar gidan. Karo na farko dana fito kenan tun bayan zuwa na, kallon unguwar nake babu hayaniya, layi ne Babba me dauke da shinfidaddiyar kwalta, daidai kofar wani madadaicin gida me kyau da tsari gate din gidan ya bude a hankali, wata bakar mota me bakin glass ta fito, da wani irin gudu ya hau kan dan karamin titin ba tare da ya kula da motar mu ba. Tsaki naji Anas yaja cikin kuluwa yace

"Sojan nan yazo kenan!"

Ramlah ce tayi tsagal tace

"Jiya ma da Hajiya ta aike ni naga motar tasa, ba yau yazo ba."

"Na tambaye ki?" Yace yana zare mata ido

"Bana son gulma da sa ido kinji, ni da nake da grudges dashi daban, mind ur bussiness."

K'us tayi tana turo baki, ya sake jan tsakin yana kallon mirror din dake saman motar, hada ido mukayi ya harare ni nayi saurin sauke kaina k'asa. Zuciya ta na tsananta bugu jin ambatar sojan da yayi, tunanin Farouk d'ina ne ya dawo min, shi kadai na sani da hakan. Tun daga lokacin na daina sauraron komai, na fada kundin tunanin sa.

Rano😊🙏🏼:     DAURIN GORO       
21

Gudu yake sosai muna biye dashi har makarantar, a wajen shiga suka tsaida shi ba'a barin me tinted glass shiga, kamar zai yi musu dasu sai kuma ya dawo da baya yayi wajen da aka tanadarwa masu irin glass din, shiga mukayi still Anas na ta mita, mitar yasan dokar kawai dan shi force ne zai taka, mu dai babu wanda ya tanka masa har muka isa gaban Hall d'in, fita mukayi ya nemi wajen parking mu kuma mukayi wajen gungun mutanen dake jiran zuwan examinars ɗin, zaman mu da kadan suka iso, nan dana aka soma screening ana shiga hall din, ba'a dau wani dogon lokaci ba aka fara, addu'a kawai nake duk wadda tazo baki na, saboda ba kowacce na sani ba, ba kowacce na iya ba, dama Farouk ne yamin alƙawarin sani a islamiyya da zarar ya dawo, ashe hakan ba mai yiwu wa bane.
   Na gefe na ne muka hada ido dashi, ya bini da wani irin kallo kamar ya ga kashi, mamaki ne ya kamani ganin ba wai sanin sa nayi ba, shigar jikin sa kadai ta nuna waye shi, da inda ya fito. Ban sake kallon sa ba, dan na lura dan zafin kai ne, na shiga abinda ya kawo ni. Har muka gama ban sake kallon ko in da yake ba, hanyar fita nayi ina sauri sauri, ya cimmini yana tsaida ni, kamar bazan tsaya ba sai kuma na tsaya, cikin isa da kasaita ya tsaya a gabana yana min kallon up and down

"Na sanki?" Ya tambaye ni looking as if ya taba gani na

"Kamar ya?"

Wani iri yayi da bakin sa, yana sake ware idanun sa a kaina, sai kuma yce

"May be, may be."

"Ban fa gane ba ."

"Shit!, Kin tab'a attending birthday party haka or kinsan wani a abuja"

Juyawa nayi da nufin barin wajen dan na lura bashi da abun fada sam, sai ya sake biyo ni da sauri,

"I'm Kamal Marwan Dikko by name."

"Baku gama bane?" Muryar Ya Anas ta kawo mana ziyara har inda muke, juyawa nayi na bar wajen da sauri ina tunanin yanayin da fuskar tasa ta nuna, inda na bar Ramlah na sameta, tana rik'e da Iman dake ta faman kuka, tana zagaye a wajen, tausayi ta bani ganin yadda tayi wujiga wujiga.

"Kar dai kuka take tayi miki tun da muka shiga."

Nace ina karbar ta,

"Kuma kinsan batayi kuka ba sai yanzu, wannan da muka gani sojan nan dazu, har nan yazo, da yaji kukan ta har da karbar ta, yana da kirki na rasa me yasa basa shiri da Ya Anas wallahi, kinsan yana zuwa ya ganmu tsaye tare, ya haɗa rai ya karbe ta a hannun shi, dalilin barin wajen nan kenan da yayi, kuma dan mugunta irin ta Ya Anas yana tafiya ya dawo min da ita lokacin ta soma kuka,shine fa take tayi har yanzu, taki shiru."

Dariya kawai na saka muna nufar motar

"Kika san me ya hada su, kinsan ance wasu masu khakhi akwai iya shege, duk da ba dukka ba, Ya Farouk ba haka yake ba sam."

"Toh wannan din ma bashi da damuwa wallahi, zafin rai ne irin na ya Anas."

"Maza ya jiki wallahi, ba ruwana."

Dariya ta saka

"Nima wallahi ba ruwana nayi shiru."

"Atoh, yafi dai."

Jikin motar muka tsaya, tsawon lokaci sannan ya zo ya bude mana muka shiga, rannan nasa a jagule, kamar wanda akayi rigima dashi, banki muka wuce direct ya karbar min Form, na cike komai, wajen sa marital status ne har na zabi wajen Married, naga yayi min wani kallo, da sauri na gyara ina yak'e, na mika masa ya karba yana sake sakarmin harara. Dariya ma ya bani, na dan murmusa kawai, shi sam abin bacin rai baya masa kadan, komai abin ayi fushi ne, sai dai duk inda mutum me nutsuwa da kamala yake ya cika, bashi da hayaniya balle baragada, komai yana yinsa ne gently cikin tsantseni da takatsantsan.
Yana ajiye mu a gida be ko shiga ba ya ja motar ya tafi, Hajiya bata nan taje Barka, Baba Altine ce kawai a gidan ta gama aiki tana kishingid'e tana jin radio, sai a lokacin muka samu muka ci abinci sannan muka zauna muna d'an tayata hira.
   

★★★
Daya bayan daya mutanen dake cunkushe a harabar makaranta suka dinga yayewa, har ya zama na babu kowa sai yan tsirarin mutane, ran Farouk babu dadi ganin da gaske har ana neman gama wa babu alamar ta, hakan na nufin ta hakura da duk wasu muhimman abubuwan da suka dace da rayuwar ta kenan ko me? Baya so zuciyar sa tana raya masa wani abu mummuna ya faru da da ita, yana ji a ransa tana nan da ranta, kuma koman daren dadewa zata dawo gareshi. Amma yaushe? Yau? Gobe ko jibi? Babu rana balle wata, a duk sanda ya kira Shagari jikin sa kara mutuwa yake, a tunanin sa zata dawo baya, duk da yasan ba lallai bane tunanin ta ya kawo mata hakan, duba da yadda komai ya zo mata a lokaci daya.
  Da kyar ya bar makaranta zuciyar sa babu dadi, yana zuwa ya rufe kansa a daki ya kwanta kawai, ba zai taba yafe wa Inno ba, da kuma duk wanda yake da hannu a ciki.
   Sakon text message ɗin Ja'afar ne ya iso masa, ya bude yana karantawa

"Daddy na neman ka, idan da hali ka baro komai ka dawo Please."

Ajiye wayar yayi ya koma ya kwanta yana yanke hukuncin amsar tayin na Daddy. Saboda haka yana tashi da safe ya sanar wa da Dadah kudurin sa, addu'a kawai tayi masa tare da sake karfafa masa gwuiwar yayi wa mahaifin sa biyayya.
   Haka ya tattaro koman sa ya dawo, ya kuma jewa da Daddyn da albishir ɗin karbar tayin nasa, tsabar farin ciki a take ya kira waya ya nemi alfarmar barin sa ya tafi karatu na tsawon wasu shekaru ba tare da ya bar aikin nasa ba, babu bata lokaci aka gama komai aka hau shirye-shiryen biki na alfarma.
Shi dai sai ya koma gefe ya zuba musu ido kawai dan bashi da katabus akan komai zasu aiwatar.
Da yake abun na gida ne sati biyu aka saka, tun daga lokacin Mama ta soma aikin gyaran amarya, aka shiga hidima sosai tun da wannan su shine karon farko da za'a yi aure a cikin gidan, auren kuma na mutum biyu.
Wednesday suka fara events, dama sam babu wanda yasa ran Farouk din zai halarci abu ko daya a ciki, a harabar gidan dake manne da nasu da ya zama gidan shikiki kuma aminin Daddyn suke yin komai saboda girman sa.

★★★

Sanye take da takalmi me kamar slipers rigar jikin ta doguwa ce me budewa sosai, sai d'an karami mayafi data dora saman kanta, a hankali cike da farin ciki take taka harabar gidan har ta dangana da part din Mama, yan uwa ne cike kowa na zaune ana hada-hada, cike da karsashi ta karasa garesu, suka hau yi mata kirarin ga amarya ga amarya, bakin ta ya kasa rufuwa saboda tsabar farin cikin da take ciki, kan wata Anty ɗin su ta faɗa tana kunshe fuskar ta.
  Tsokanar ta suka cigaba da yi, ta zame da kyar ta fada bedroom din su, sauran yan uwan su sa'annin ta ne da manyan ma da suka girme mata a zazzaune ana shafta, cikin su ta shige aka cigaba da yi dakin ya kaure da hayaniyar su.
   Wayar tace tayi k'ara, ta daga da sauri, ganin sunan Yah Farouk yasa ta mike tayi saurin fadawa toilet tana saka key, shikiyanci suka hau yi mata tana jinsu ta daga wayar tana karawa a kunnenta

"Kizo side dinmu yanzu ina jiran ki."

Fitowa tayi ta fice tana ji su sake tsokanar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login