Showing 51001 words to 54000 words out of 112633 words

Chapter 18 - DAURIN GORO COMPLET book 1 by Hafsat Rano.txt

07 Aug 2025

7442

ta, har ta isa bangaren nasu babu kowa,tura kofar tayi ta jita a bude, ta tura kanta kai tsaye, yana kwance akan cusion ya daga kansa sama sanye da farar singlet da dogon wando fari, wajen sa ta nufa yasa hannu ya dakatar da ita

"Zauna a saman kujerar nan magana zamuyi."

Jikin ta ne yayi sanyi ta zauna tana mamakin yadda yayi mata, tashi yayi zaune , idon sa sun kada sunyi ja sosai, gaban ta ya fadi da suka hada ido.
  Takawa ya shiga yi yana kai komo tsakanin farkon falon da karshen shi ya gaza furta kalma daya, duk in da yayi sai ta bishi da kallo, har ya isa gaban system ɗin dake ajiye tana fitar da sautin suratul munafikun cikin kira'ar Ghamid'i. Kashe karatun yayi ya dauko d'an karamin Flash ya jona a jiki, hoton bidiyon da aka turo masa ne ya bayyana a saman screen din, dan zabura tayi, har ya iso gaban ta ya tsaya kusa da ita daf, ya kura wa videon ido yana masa kallon ssoai, hadiye yawu tayi cikin wani irin yanayi ta kalli fuskar sa, hankalin sa kachokam ya tafi kan kallon video, pause ya saka ya juyo yana hade hannayen sa suka bada sauti me dan karfi. Cikin shakakkiyar murya yace

"Ina kika samu Flash ɗin nan?"

"Ni... Ni? Na'am!"

"Kinji me nace, bazan sake maimaitawa ba."

"Ni ba nawa bane, bansan nawa ye ba."

Wani irin kallo yayi mata shakeke, kafin ya tashi yana matsawa baya

"Tun ranar da abin ya faru, ban taba hutawa daga binciken wanda zai min haka ba, I tried very hard na gano ranar da ni da kaina na zauna na rubuta takardar, sai dai na kasa."

Dan sunkuyowa yayi daidai fuskar ta

"Kin tuna ranar da kika zo kika kawo min juice Ina aiki, ranar dana fada miki zanyi tafiya ina so kuje wajen ta, kin tuna?"

Daga kai tayi da sauri don har ta fara digar hawaye,

"Bude baki kiyi min magana!" Ya daka mata tsawa

"Na tuna."

"Good, what did you do? I trust you the most, na kula dake na baki dukkan gata, kinsan komai nawa, what did you do?"

Ya fad'a cikin daga murya

"Ya Farouk, dan Allah."

"Shissshhhhhhh..." Yasa hannu a saman leban sa

"Don't say a word, bayan na amince miki, you betrayed me, kika bani juice da akayi mixing da abun da zai dauke min hankali, and you gave me this na rubuta same abinda ke jiki."

Ya dago takardar yana nuna mata a fuskar ta da ita da kanta ta rubuta, karfin kukan ta ya karu sosai, wani irin harbawa jijiyoyin kansa suke, ba zai taba yarda idan aka ce masa Amal zata cuceshi haka ba, me yayi mata da yayi deserving wannan sakamakon? Tabbas abinda ya faru kenan ranar, amma yayi imani ba zata taba aikatawa ita kadai ba, dole sai dai idan da hannu wani babba,amma wa?
Kokarin saita kansa yayi dan yana son jin komai.

"Ki daina kuka, ina son sanin dalilin da yasa kika yi min wannan hukuncin, me nayi miki? Soyayyar dana nuna miki tun kina tsumma? Shine sakamako na?"

"Ya Farouk dan Allah kayi hakuri."

"Amal hakuri, is that all? Kinsan halin da kika samu dukka? Dalilin haka yanzu ba'a san inda take ba, and kice nayi hakuri?"

Girgiza kai kawai take tana kuka sosai, tsugunawa yayi a gaban ta yana jin dama shima ya samu damar yin kuka, hannun sa ya dora a saman bakin sa, da sauri ta hadiye kukan da take tana ajiyar zuciya.

"Waye ya saki?" Ya zare mata ido sosai yana sake hada ransa

"Yaaahh..."

"Waye ya saki!!!" Ya daka mata tsawa da karfn da ta kusa sakin fitsari a wando, babu bata lokaci ta shiga sanar mishi komai tana kuka sosai.
Kansa ne ya hau juyawa, ya soma ganin dishi-dishi, bayan samun evidence din da yayi a jakar ta da yadda abin ya dawo masa kamar Flash back, duk da ya shiga kaduwa, sai dai bai taba tunanin zasu aikata masa hakan ba, mutane uku masu matukar muhimmanci a rayuwar sa, wanda ya aminta dasu, yake ganin su a matsayin wanda suka fi kowa a wajen sa, su suka taimaka wajen tarwatsewar rayuwar sa, da baya da baya ya shiga takawa har ya dangana da daki, ganin haka yasa ta fita da gudu tana kuka sosai kamar ranta zai fita.
Daki ya fada ya saka kuka, kukan da ya jima yana neman sa, sai a yau ya samu damar yin sa, lallai ya chanchanci yayi kuka. Ya jima yana yi, sai da yaji kamar zai fita hayyacin sa, sannan ya tashi ya dauro alwala ya shiga gaya wa Allah kukan sa, yana sallar yana hawaye sosai, hawayen zallar bakin ciki yadda suka ci amanar sa.
Asubar fari ya tattara komai nasa yayi wa gidan kallon karshe, ya dau hanya ba tare da tunanin zai sake waiwayo wa ba har abadah.
Ranar data kasance ranar da za'a daura auren, a rana yayi bankwana da kowa nasa da dukkan memory d'insa da yayi tare dasu.
Karfe sha daya kamar yadda aka tsara, dubunnan mutane suka shaida daurin auren Amal Adam Shagari, Da Farouk Kabir Shagari. A daidai lokacin yana kwance a dakin hotel din daya sauka, ya rasa inda zai saka kansa yaji dadi,ya san daga lokacin da Daddy zai gane yayi nisa, duk da yasan zai yi fada ssoai, zai kuma yi fushi dashi me tsanani, amma ba zai iya ba, ba zai iya zama ba, zai bi abinda zuciyar sa ta riga ta saka masa, ko da hakan na nufin zare shi daga cikin ahalinsa ne.


Rano😍

Manage 🙋🚴
:      DG
   22

★★★
Kuka take sosai ta kudundune kanta cikin katon bargo, tana jin lokacin da aka sanar da daurin auren, amma bata da katabus, tana ji suka shigo baki dayan su, kowa na kokarin tsokanar ta, da sauri duk suka yo kanta ganin yadda jikinta ke faman rawa, suka shiga tambayar abinda yake damunta, kayan jikin ta ne tun na jiya, idanun ta sun kumbura sosai alamun kwana tayi bata runtsa ba, da sauri daya daga cikin su ta fita dan kiran Mama. A tare suka dawo dakin, ta dago ta tana karata jikin ta

"Baki da lafiya ne dama aamal?"

Kasa magana tayi, sai wani iri da take kamar zata shid'e, riko ta sosai Maman tayi suka fita daga dakin, dakin ta ta kaita babu kowa ciki, ta kwantar da ita tana kokarin kiran ko Ja'afar ne tun da tasan Daddy na cikin Jama'a. Be d'aga ba shi din ma, alamun shi ma ya shiga busy. Jawo mata kofar tayi ta dawo falon, daidai lokacin da Uncle Buhari ya shigo yana gyara zaman Babbar rigar sa.

"Ina Amal?" Ya tambaya bayan ya amsa gaisuwar matan dake falon

"Tana daki na, bata jin dadi ne."

"Ok Ina son ganin ta. "

"Lafiya dai ko?"

"Eh kalou, magana zamuyi."

Ganin da mutane wajen yasa tace ya biyo ta dakin nata,suna shiga ya matsa jikin gadon, ya duba ta kadan kafin yace

"Kunyi magana da Farouk daga jiya zuwa yau?"

Gaban ta ne ya fadi, tayi saurin girgiza kanta tana fatan ba wani abu yace ba, d'an jim Uncle Buhari yayi kamin yace

"Farouk fa ya tafi, ya ajiye letter a dakin su, yanzu haka Yaya bai san inda zai sa kansa ba, matsalar ma ba'a ga letter tasa ba sai bayan aure ya dauro.

"Innalillah wa inna ilaihi raji'un, mun shiga uku."

Mama tace tana sallallami, karfin kukan Amal din ne ya karu, ta mike zaune tana sake bude muryar ta sosai, girgiza kai Uncle B yayi yace

"Kinga yi shiru kar ki ankarar da mutane halin da ake ciki."

Da sauri ta rage kukan nata, sai dai bata daina ba, dan ita kadai tasan dalilin faruwar komai, a yau da tana da iko da kanta, data sanar wa kowa komai, sai dai bata da wannan damar, kenan a haka zata kare rayuwar ta? Ko akwai sauyin da zai zo bayan nan? Kiyayyar Aminatu ce ta shiga ninkuwa a zuciyar ta, duk itace dalilin komai, ta raba ta da Ya Farouk dinta, mai sonta da kaunar ta tun bata san kanta ba.

Cigaba da bayani Uncle B yayi, bata dauki komai a maganar tasa ba, sai data dawo daga tunanin da ta tafi taji yana yiwa Maman bayani

"Abinda nake tunani ko menene akayi wa yaron nan me girma ne, da zai sa shi yanke wannan danyen hukuncin, idan akwai abinda ya haɗa ku ki sanar mana, idan yaso sai asan yadda za'a bullo wa al'amarin."

Ya kalle ta yana sake tambayar ta a karo na biyu, sake girgiza masa kai tayi tana goge hawayen fuskarta

"Bansan komai ba Uncle B, ni jiya ma tun bayan la'asar rabo na dashi."

"Shikenan, ku kwantar da hankalin ku, kar a bari mutane su sani, idan kowa ya watse sai musan ta ina zamu ɓullo wa al'amarin."

Fita yayi ya koma Falon da su Daddyn suke, waya ce a hannun sa yana ta making calls, babu wani information akai, yanke hukuncin kiran Dadah yayi duk da baya son d'aga mata hankali, amma yana tunanin xata iya sanin wani abu.
   Yana gama mata bayani ta saki salati, sai kawai tasa kuka sosai, ta gaji da wannan abubuwan dake ta tasowa, ace daga wannan sai wannan? Idan fa wani ciwon ya kamashi? Ba taga ta zama ba.
   Sosai maganar ta firgitata, iya sanin ta Farouk ba zai taba aikata abinda zai wargaza ahalin nasu ba, shiri ta soma yi, a yau bayan shekaru masu yawan gaske, zata sake taka garin na Abuja, garin da tayi wa kanta iyaka dashi saboda babban dalilin ta, tana shiryawa tana addu'ar komai yazo musu cikin sauki, dan ba zata juri wani abu ya sake bullowa a ahalin nata ba.
   Driver ne ya iso, ya dauke ta da dukkan abubuwan bukatar ta, suka dauki hanyar birnin na abuja.
   Tasbah ne ya hannun ta tana ja, bata jin dadin jikin ta kwana biyu, haka dai take daurewa tana yin komai, sai dai a yanzu yadda take jin jikin nata na neman rinjayar ta, addu'a take tayi tana rokon Allah ya daidaita al'amarin ya kare su daga sharrin masu sharri.

****
Mummy na zaune suna meeting da clients dinta kiran Ja'afar ya risketa, message ta tura masa tana meeting ta kashe wayar baki daya.
  A gajiye ta fito bayan sun gama, takardu ne masu yawa a hannun messenger ta,  hannun ta rike da yar karamar jakar hannun ta suka nufi motarta, sai data zauna a ciki gami da cilla jakar tata gefe sannan ta daga wayar ta kira shi tana kishingida a bayan motar.

"Mummy, akwai matsala wallahi, Ya Farouk ya tafi, babu wanda yasan ina yake, bayan an gama daura auren shi da Amal na shiga daki duboshi na tarar da letter daya ajiye, dan Allah Mummy ko ya fada miki ina zaije? Hankalin kowa ya tashi."

Tuni taji gajiyar da take ciki ta warware, tashi tayi zaune sosai tace ma driver ta ya rage gudn motar,

"Kana jina Ja'afar? Ina yace ya tafi?"

"Be fada ba, yace dai yayi nisa kada a neme shi."

"Dama aure Daddyn naku zai masa? Bani da masaniya akai?"

"Na zata kin sani naga yazo wajen ki before yayi accepting maganar ,shiyasa ma ban sanar miki ba."

"Shikenan, ka kwantar da hankalin ka, bansan ina yake ba amma i ll try my very best naga na same shi, ka kwantar da hankalin ka."

"Ok shikenan, sai anjjima."

Ranta ne ya ɓaci, mamakin girman kiyayyar da Daddy yake mata har ta kai hakan, a karo na biyu ya sake aurar da dan nata ba tare da sanin ta ba, kwafa tayi tana lumshe idon ta, ta gaji da komai, dauriya ce kawai da karfin zuciya, amma wannan karon ya kamata ta nuna masa da gaske ita ta haifi Farouk ba wai shi kadai ɗin bane kamar yadda yake mata iko da gadara akan dukkan abin da ya shafe shi.
   Maimakon ta wuce gida kamar yadda ta saba, sai ta sauya akalar motar zuwa gidan su, dan tabbas ba zata bar komai ba, zata nemo danta ta dawo dashi gaban ta, ta bashi dukkan kulawar da ta kamata. Dauriyar ta ta kare!

∞∞∞
Dadah basu isa Abuja ba sai daf da magriba, lokacin kowa ya watse sai yan tsirarin da suka zama dole, Daddy na zaune a masallacin gidan Aminin sa, tun bayan da aka idar da sallar la'asar suke ciki ba tare da sun fito ba, sosai tafiyar Farouk ta bige shi har yana jin kamar bashi da lafiya, zuciyar shi tayi sanyi,  tabbas yana tsaurara wa a duk abinda ya shafi Farouk din, ya rasa dalilin da yasa baya iya tsayawa ya saurare shi, ko ya bashi damar kare kansa.
    Sai da aka yi magriba da isha'i sannan ya fito, ya nufi cikin gidan nasa yana takawa a hankali, da motar dasu Dadah suka zo ya fara tozali, da dan saurin sa ya nufi shashen nata da zama mallakin ta a dah, Wanda yake a rufe tun bayan tafiyar ta, taron biki yasa aka bude shi saboda mutane, bakin sa dauke da sallama ya shiga, suna zaune dukkan su, Mama na daga kasa wajen kafarta, sai Amal datayi matashin kai da kafarta tana kuka k'asa-k'asa.
   Waje ya nema ya zauna, cike da girmamawa ya gaishe ta, ta amsa masa kafin su fara zamewa daya bayan daya suna barin falon, su biyu sukayi saura, daga ita sai shi, kallon sa tayi a tsanake, da hango tsantsar ramar da yayi, wadda ba zata wuce a wunin yau ta same shi ba, Tabbas ba abu bane mai sauki ba tafiyar Farouk din, sai dai a yau zata nuna ma Daddy kuskuren sa, zata sanar dashi abinda ya gaza fuskanta.

"Kabiru..." Ta kira shi da sunan shi kai tsaye, sai yaji zuciyar sa ta kara karyewa, tabbas ko menene zata fada masa yasan me girma ne, cikin girmamawa yace

"Ina neman gafarar ki Dadah, idan na bata miki dan Allah."

Gyara zaman ta tayi, cikin jan hankali tace

"Idan nace kamin laifi nayi karya, tsakani na dakai, babu abinda zance maka sai Allah yayi maka albarka, ka zama baya goya marayu, ka rike kowa naka, ya'yan yan uwanka ka kula da su da al'amarin su, ba tare da ka duba abinda ya faru a baya ba, sai dai kayi kuskuren wofintar da naka duk da sunan son hukunta mahaifiyar sa, menene laifin sa a ciki abinda bashi da masaniya akai..?"

"Baka taba bashi damar jin ta bakin sa ba, komai yayi laifi ne wajen ka, baka taba damuwa da halin da yake ciki ba, halin da zai shiga, duk da haka yana kokarin yi maka abinda kake so."

"Ina ji a jikina a duk inda yake ba a dadi yake ba, akwai babban dalilin da yasa shi barin mu."

"Nayi kuskure, ban taba jin abinda nake aikata masa laifi bane, sai yau, sai dana samu wanda zai fahimtar dani, tun safe maganar da muke kenan da MD, me yasa na kasa gane haka? Sai da lokaci ya kure min, ya zanyi da auren da ke kan Amal? Na rasa ina zan saka raina naji dadi Dadah, komai ya tsaya min."

"Hakuri zamuyi, mu bar wa Allah komai, mu bashi lokaci muga yadda abubuwan zasu sauya, watakila ya waiwayo mu, idan ransa ya saki."

"Allah yasa, bana son matsala ta sake faruwa, ina son yadda muka binne komai, kada wannan matsalar ta tono shi, zuciya ta ba zata iya daukar maimaituwar abinda ya shud'e ba."

"In Sha Allah hakan ba zata faru ba."

Cigaba sukayi da tattaunawa, a hankali cikin hikima Dadah ke kara nuna wa Daddy laifin sa, sosai jikin sa yayi sanyi, yaji tsoron abinda zai je ya dawo. Duk a dalilin rufe sirrin gidan nasu, ya bata wa d'an sa komai, da hannun sa ba tare da ya ankara ba. Tsaki yaja yana tuna shi,ba zai taba yafe mishi ba, duk kuwa da k'asa ta riga da ta rufe idanun shi a yanzu, amma tabbas ya bar musa tabo babba a zuciyar sa da ba zai taba iya goguwa ba.
   Kwana Dada uku a daddafe ta tabbatar da komai ya lafa, ta hau shirin juyowa, rokon da suka dinga yi akan ta zauna dasu, ki tayi dan hakan shine abu na karshe da ba zata iya ba. Amal ce ta roki alfarmar zata bita, kai tsaye Daddy ya amince , ta haɗa kayan ta ta bita don samun nutsuwar zuciya.

****
Hakimce take saman kujerar ta ta gado, me samfurin karagar mulki, farar tsohuwa wadda a ƙalla ta doshi shekaru tamanin da yan kai, bata da Abu mafi soyuwa a rayuwar ta fiye da jikin nata wanda ya kasance d'a kwaya d'aya tak.
   Hajiya Turai kamar yadda sunan ta yake, wadda tsabar farin ta yasa aka saka mata sunan, gashi har tsufan ta tana nan da farin nata da ya sake haduwa da hutu da jin dadi.
   Sanye yake da rigar sa marar nauyi da gajeren wando da be wuce masa guiwa ba, hannun sa rike da football yana dokata a hankali ya isa falon.
   Fara'ar fuskarta ce ta dadu, ganin abinda yafi komai soyuwa a gareta, dukkan soyayyar da take wa mahaifin sa ce ta dawo kansa, da ya zama da d'aya tilo da ta haifa a duniya, bayan ta cire dai ta fitar da tsammanin samun sa.
   Zama yayi yana cigaba da doka ball ɗin yana kamawa, ransa a bace babu walwala, tasan kwanan zancen,saboda haka ta shiga yi masa kirarin data saba masa a kodayaushe, biris yayi da ita kamar bai san tana yi ba,

"Wanane ya taba min kai wai?"

"Haba Old Woman kinsan fa dalilin fushi na, nace ku fada masa bana son karatun a Nigeriar ma baki daya kunki, ace a rasa ina zanyi University kamar ni sai a Kano, a Kanon ma ba Private Uni ba, chan ta kowa da kowa har da ya'yan talakawa, Allah ya gani an cuceni walalhi."

"Ka kwantar da hankalin ka, ka fara chan ɗin tunda ya kafe, idan yaso a hankali sai na sashi dole ya fitar da kai wajen, amma sai ka fara rage rawar kan naka ya tabbatar ka nutsu sosai."

"Ni wai wacce rawar kai nake, haka kullum Ammi sai faɗa take min, ke kadai ke sona sai Anty, ni na gaji da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login