Showing 81001 words to 84000 words out of 112633 words

Chapter 28 - DAURIN GORO COMPLET book 1 by Hafsat Rano.txt

07 Aug 2025

7420

daga ba, kai tsaye ya shiga gidan bakin sa dauke da sallama, shiru gidan lokacin Baba Altine ta shiga makota siyo koko, Aminatu na toilet tana wanka saboda haka bata ji shigowar sa ba, sakon da Ya Farouk ya bashi ya ajiye a gefe yana kallon falon, idon sa ne ya sauka akan file din dake yashe a kasa, garin sauri ta manta ta dauke filon bata dauke shi ba, kamar kar ya taba sai kuma yaji yana son ganin date of birth din ta ganin file ne na asibiti.
Kai tsaye yasa hannu ya dauka, sunan asibitin dake rubuce a saman file din dayayi daidai da irin sunan dake jikin birth certificate d'insa shi ya kara jan hankalin sa, murmushi ya saki yana jin dadin ganin ashe ma asibiti daya aka haife su,yana budewa yan kananun passport din dake ciki suka fado be bi takansu burin sa kawai ya ga date ɗin ta dan suna yawan musun ta girme shi sanda suna makaranta.
Mamaki ne ya kamashi ganin hatta date da time na haihuwar su daya ne, be kula da sunan ba yana dariya ya rufe ya tsuguna ya tattaro hotunan guda biyu, cikin tsananin mamaki yake kallon hoton yana sake kalla, hoton Ammi ne da Daddy, duk da dadewar da akayi da daukar hoton wanda idan ba sanin su kayi sosai ba ba lallai ka gane su ba, a birkice ya sake bude file din ya shiga bin sunan ta dake rubuce cikin babban harafi

"AMINATU MD"

Sakin file din yayi ya fadi a wajen daidai lokacin da Aminatu ta fito daga dakin a shirye tana kiran Baba Altine, ganin shi tsaye cikin wani irin yanayi yasa ta ƙaraso da sauri tana tambayar sa menene, be tsaya bata amsa ba ya juya da sauri ya fice daga gidan zuciyar sa na wani irin harbawa.



Masha Allah...

Duk naga bayanan ku, kuma zanzo insha Allah da hukuncin hakan a musulunce, Nagode kwarai Allah saka da Alkhairi. Allah ya taimaka ya bamu Sa'a baki daya.


Rano DG*

               *35*

★★★★★

Tsaye tayi cikin tarardadin abinda ya faru, sai kuma ta bi file din nata dake yashe kasa da kallo kafin ta tsuguna ta tattara komai tana sake dubawa.
Ledar daya ajiye gefe me tambarin Shoprite ta dauka ta bubbbude breakfast ne me rai da lafiya sai yar karamar red rose me kyau sosai, dan karamin note din dake ciki ya fado, murmushi ta saka

"I love you"

Aka rubuta da wani irin rubuth me matukar birgewa, wato ya zama baturen karfi da yaji kenan, wani iri ta dinga ji kamar tana tafiya akan gajimare.


***Yana fita ya shiga motar sa ya kifa kansa saman sitiyari, fuskar Aminatu da bata da maraba da ta Ammin sa ta shiga yi masa yawo a saman ƙwaƙwalwar sa, tsawon wannan lokaci ashe da Ammi take masa kama ya kasa ganewa sai yanzu, hoton fuskokin iyayen nasa ya dinga kokarin haɗawa da nasa dana Aminatu sai dai ko kusa babu digon kama da sukayi dashi, sau tari yakan tambaya kansa da wa yake kama cikin iyayen nasa ganin babu yasa ya bawa kansa amsar kila wasu ya biyo a cikin dangin nasu tunda dama hakan na faruwa.
Tunanin sa ne ya tsaya chak, idan har Aminatu diyar Daddy da Ammin sa ce, shi kuma fa da yake da shekaru da komai irin nata ballantana yace ko kanwar sa ce, ji yayi zuciyr shi ta sake karaya da kyar ya lallaba ya bar kofar gidan ba tare da sanin kowa ba ya bar garin domin yana da bukatar sanin komai.

***
Ammi na zaune tana kallon talabijin cikin daya daga cikin jerin kujerun alfarmar dake zagaye da babban falon nata, rashin yara na matukar damun ta, tun tana yawon asibiti har ta hakura ta daina, babu wata matsala ta kai tsaye da za'a kira ta dashi daya hanata haihuwa.


Yanayin yadda ya shigo mata a firgice yasa tayi saurin ta tashi zaune tana kallon sa.

"Kamal!" Ta Kira sunan sa, kallon ta yayi sai kuma yayi saurin tattaro nutsuwar, tunowa da yayi bazai bari kowa ya san komai ba har sai ya gano ainihin abinda yake faruwa yasa shi sakin fuskar sa sosai ya zauna kusa da ita yana dora kansa a saman kafadar ta

"Ammi nah."

"Karka cemin dogon tuki kayi, ina Daddyn ya na ganka kai kadai?"

"Ammi ji nayi ina so nazo gida, ga Old Woman ta matsa shisa kawai na gudo gida Daddy ma be san na taho ba."

"Maganar yarinyar ce har yanzu Kamal?"

"Ki taya mu da addu'a Ammi, komai zai daidaita."

"Shikenan, amma gaskiya na soma gajiya da zaryar da kake tsakanin nan da chan, hanyar nan da babu kyau akwai risky."

"Babu abinda zai faru In Sha Allah."

"Allah yasa." Ta amsa ba don taso ba.

Bedroom d'inta ya shiga, ya dubo dukkan takardun sa masu muhimmanci, ciki har da birth certificate d'insa original din, da address din asibitin da aka haife shi ya wuce dasu dakin sa.
Be zauna ba ya tafi wajen Hajiya Turai, har dare yana chan suna hirar su gwanin sha'awa sai dai rabi da kwatan hankalin sa baya wajen yana tunanin yadda zai soma binciken kansa ba tare da sanin kowa ba.



***
Sai data fara sauya shigar jikin ta sannan tayi masa text message gata nan ta fito, handbag dinta dake ajiye saman drawaer tayi nufin dauka bata ganta ba, dubawa ta hau yi kafin da kyar ta gano ta, ta kusa shigewa karkashin gado, ba tare da tunanin abinda ya kai jakar wajen ba ta tura wayar ta fito, duk basa falon hakan yasa tayi ficewar ta kai tsaye, bata bi takan driver dake gidan ba ta fita titi ta tari abin hawa ta fada masa inda zai kaita.

Motoci biyu ne masu tsaron lafiyar Daddy sai motar da suke ciki su hudu wadda Farouk yake tukawa sai Uncle Aliiyu a gefen sa, Daddy da Alhaji Marwan na baya, tracker da Farouk ya sa mata a jikin jakar ta suke bi har zuwa sanda ta isa gaban building din da yake incomplete, saukowa tayi ta sallami me napep ɗin kai tsaye ta kutsa kanta ciki tana kokarin kiran number tasa.

A daidai lokacin ya saka Iman a gaba ta ƙatuwar wayar charger, ko ina na jikin ta duka ne beyi la'akari da kankantar shekarun ta ba, duk da yana bata abinci amma idan tayi mishi kuka dukan ta yake kamar ya samu babba, shigowar Amal wajen ya saki wayar hannun nasa yana dora hannun sa a saman bakin sa

"Shissh." Da sauri ta hadiye kukan ta saka dukkan hannayen ta biyu ta rike saman bakin ta

"Daddy, yarinya ce fa." Amal tace tana matsowa kusa da su

"Bani da time na tabbata by now Ali ya sanar dasu ina raye, ina so ki bawa Hajara wannan sakon, zata san yadda zatayi dashi."

"Toh yarinyar fa?"

"Itace makamin da zan yi amfani na yaki Kabir da MD, ina bukatar dukiya ta, ina so komai ya dawo waje na, na maida su abin kwatance kamar yadda suka zalunce ni."

"Idan har kana da damar hakan ba?"

Farouk ya shigo kai tsaye fuskar sa babu digon Rahma ko sassauci,kallon Amal gyatumin nata yayi cikin yanayi na tuhuma,

"Amal yaudara ta kikayi? Duk abinda nake ba saboda ke nake ba?"

"Bansan zai zo ba ai." Tace tana matsawa gefe gami da riƙe hannun Iman

"Idan bake kika fada musu ba, ya akayi suka san nan?"

"Duk yadda kake kafkaf tsawon wannan lokaci baka taba tunani wannan ranar ba?"

Zai yi magana sai kuma hankalin sa ya kai kan jakar hannun ta

"You are good as nothing Amal."

Yace ganin abinda ke jiki ba tare da ta sani ba.

Sosai hankalin sa ya tafi kan yar karamar kyakkyawar yarinyar dake tsaye tana raba ido, fuskar ta har dan tashi tayi saboda marin da take sha wajen Adam, babu tantama itace yar sa, yar da bata san mahaifin ta ba, very cute and innocent soul kamar Aminatun sa, takowa ya shiga yi yana zaro bindigar dake jikin gefen wandon sa daya karba wajen Daddy, kafin ya karasa Adam ya ciro tasa cikin zafin nama yayi kokarin riko hannun Iman, da sauri Amal ta hankad'a ta wajen Farouk yayi saurin riƙe ta yana sake dagowa.

"Amal!"

Ya ambaci sunan ta da dan karfi ganin abinda tayi masa, cikin zafin nama ya fizgota ya saita bindigar sosai a kanta

"Karka kuskura ka matso, idan ka matso zan saka bindiga na harbe ta har lahira."

Kuka Amal ta saka cike da mamakin abinda mahaifin nata ke shirin aikatawa. Dariyar rainin hankali Farouk ya saka kafin yace

"Wa zakayi fooling? Yar ka ce fa. Idan ka ga dama ka kashe ta yanzu waya damu?"

"Ok." Yace yana saita bindigar sosai yana kokarin jan kunamar bindigar Daddy ya dakatar dashi.

"Me kake bukata? Me kake so damu Adam? Me muka yi maka haka?"

"Ita tsohuwar bata fada muku abinda tayi min ba?"

"Yanzu me kake so?"

"Duk abinda kuka dade kuna tarawa, ina nufin dukiyar ka baki daya data MD, shine kadai zai fanshi duk abinda kukayi min ."

"Kazo muje gida a zauna sai a san yadda za'a bullo wa al'amarin, hannun ka baya rubewa ka yanke ka yar Adam."

"Ni na dade da sa gatari na yanke nawa, bani da alakar komai daku, babu abinda nake so fiye dana ga kun wulakanta, wulakanta mafi kaskanci."

"Daddy wanda yayi nisa baya jin kira, koma me akayi masa ya kamata ya zama mai yafiya, ka daina lallaba shi ba zai taba fahimta ba."

"Farouk kai yaro ne, Adam zaka karbi tayina kazo muje gida mu yi sulhu?"

"Har abadah." Yace yana sake riƙe bindigar sa sosai akan Amal dake kuka sosai har da majina.

"Well then, bani da zabi face na yake ka."

Yace yana nuna wa yaran sa hannu, kafin kace me sun zagaye Adam sun saka tsakiya,

"Retreat or die!"

Dariya ya saka

"Ka zata bani da cover, baka taba mamakin yadda na iya surviving this long years ba tare da na taba haduwa da wani ba, while I'm leaving right under ur noses? Ba kayi tunanin hakan ba? Adam bazai taba kamuwa cikin sauki ba, hatsibibine ni fiye da yadda kake tunani, sannan yanzu zamu fara wasa, best of luck Gen!"

Daga sama aka rufe su da kasa, nan da nan idon su ya rufe ruf kowa ya hau kici-kicin yadda zai ya kare idon sa, a lokacin ya samu ya gudu ba tare da sun ankara ba, sai da komai ya lafa suka neme shi suka rasa ya gudu.

***
A mota Farouk be iya tuki ba dole daya daga cikin sojojin suka karbi tukin ya rike Iman da ta galabaita sosai, Amal na gefen sa ta cusa kanta tsakiyar kafar ta tana faman shassheka, haushi da bacin rai kukan nata ke kara masa,ji yake kamar ya ce su tsaya a sauke ta.

Kai tsaye asibiti suka wuce da ita, domin tana bukatar a duba lafiyar ta. Sosai ta galabaita da yawan kukan da take sai rashin abinci ne suka haɗar mata, gashi da alama sauro yayi mata mugun cizo da har ya saukar mata da zazzaɓi me zafin gaske. Drip aka daura mata da allurai sannan aka gyara mata wajen da duk taji ciwo. A gefe Amal ta rakube bayan su Daddy sun tafi, Farouk be sake bin ta kanta ba ya shige dakin da aka kwantar da Iman din yaja kujera ya zauna ya zuba mata ido, babu abu daya daya raba ta dashi har duhun fatar shi dauka, idanun ta ne kawai irin na Aminatu da dan karamin bakin da zakayi tunanin karamin chokalin tea ne kaɗai zai iya samun sukuni shiga ciki.

Sosai ya shagala da kallon ta yana jin farin ciki mara misaltuwa, da zarar ta dawo daidai zai kwashe su su bar kasar ba zai iya zama ba, dan ya lura fadan na su Daddy me karfi ne dan haka bazai yarda a kara involving rayuwar aaminatu ko Iman ba.
Wayar sa ya ciro ya lalubo number ta, tana bukatar sanin halin da ake ciki ko dan lafiyar ta ita ma.
A lokacin zaune Aminatu take ta kunna karatun suratul Bagra tana saurara, sau uku kenan tana kiran Kamal baya picking sai ta hakura ta bari ta sake gwadawa anjima, saboda haka data ji karatun ya tsaya alamun shigowar kira ta zata shine. Number data gani a saman screen din ta sakata komawa ta lafe sosai a jikin katitar kafin ta daga

"Ina miki albishir da na cika alkawari, gani ga Iman."

A zabure ta mike

"Dan Aallah!"

"Allah." Yace cike da gamsarwa

Sai ta saka kuka

"Kukan me? Ke da zaki gode wa Allah."

Da sauri ta kai goshin ta k'asa cike da farin ciki tayi wa Allah godiya kafin tace

"Kuna ina yanzu? Lafiyar ta kalou? Me ya sameta?

"Duk wannan tambayoyin? Muna nan premier clinic an sa mata ruwa."

"Owk gani nan." Tace da sauri tana kashe wayar.

"Baba!" Ta kwala Kira

"An ga Iman."

"Alhamdulillah, Alhamdulillah."

"Dauko hijabin ki muje suna asibiti."

"Ina jiran ku a mota." Yace yana juyawa.

"Yaushe Ya Anas yazo?"

"Sanda kika fara waya, yana tsaye nace ma ya shigo falon yaki yace na miki magana."

"Ok." Tace tana yin gaba.

****
Da kallo yabi motar kafin ya kada kansa yana kara waya a kunnen sa

"Itace?"

"Ok done!"

Yaja motar ya bar layin.

***Kamar kurame babu wanda yayi wa wani magana har suka isa Asibitin, tambaya sukayi aka nuna musu dakin, da Amal suka fara gamuwa tana daga kofar dakin akan wani benci ta kasa shiga ciki, sallama sukayi mata ta dago tana kallon su, amsawa tayi ta maida kanta gefe.

Idon sa akan kofa yaji an turo, idanun su ne suka hadu waje daya, tayi saurin janye nata ta isa gaban gadon da sassarfa, kuka ne ya taso mata tayi kokarin tsaida shi sai dai duk da haka sai da ya zobo, Baba Altine ce ta karasa cike da jimami take kallon Iman din

"Allah sarki."

Cikin takun kasaita ya shiga takowa har ya iso gaban su, kallon kallo sukayi wa juna kafin Farouk ya dauke kansa yana jan karamin tsaki, hannu Anas yasa ya dafa kan Iman din akayi saa kuwa ta bude idon ta,tana ganin shi ta saka kuka tana kiran Abba tana mika masa hannu.

"Yi shiru kinji my angel." Yace yana shafa kanta

Riko hannun Aminatu tayi dana Anas tace

"Karku tafi ku barni kai da Ummi, kullum sai nayi kuka yayi ta min masifa kuka ki zuwa ku tafi dani."

"Karki damu kinji? Ba zamu kuma barin ki ba."

Sosai ran Farouk ya bci, ya hade girar sama data kasa ya shiga watsa ma Anas harara, ita kanta Aminatu bata bi ta kansa ba kamar ma ta manta dashi a wajen, murya ya shak'e yace

"Ba'a wa yaro hayaniya aka musamman wanda ba lafiya ce dashi ba, tana bukatar hutu an gode da dubiya."

Sarai Anas ya gane dashi yake, be kula shi ba ya sake shafa kan Iman din

"Baby Bari na dauko miki chocolate a mota ?"

"Uhum uhum..Karka ki dawowa."

"Zan dawo yanzu kinji?"

Daga mishi kai tayi tana lumshe ido

"Ina so muyi magana." Yace yana duban Aminatu, kallon Farouk tayi da sauri taga yadda yayi, fuskar nan tasa kamar wuta haka ya tamke ta.

"Baki ji bane Aminatu, yayanki Anas yana so kuyi magana."

Baba Altine tayi tsagal, yaki Aminatu tayi ta tashi da nufin bin sa dan tuni yayi hanyar fita Farouk yasa hannu ya finciko ta da karfi har sai da glass din idon ta ya cire ta fado jikin sa. Da hannu ya nuna ta cikin bacin rai yace

"Karki manta akwai igiyar aure na akan ki, ke idan ma babu ban yarda ki kebe da wani gardi ba wallahi, zan baki mamaki idan kikayi gigin aikata haka."

"Idan kai ne ka haife ta sai ka hana, dame kake takama ne wai?"

Anas ya katse shi a hasale, da hannu Farouk yayi masa nuni da Iman dake kwance

"Kaga abar da nake takama da, ba kuma zaka taba samun irin ta ba har abadah sai dai abi wani sarkin."

Cikin bacin rai Anas ya bar dakin, ko motsi Aminatu batayi ba, ita mamakin yadda Farouk ya zama take, kamar ba Farouk dinta na baya ba me saukin kai da son mutane ba.



***
Duk tsare tsaren da zaiyi ya gama shi, hatta address din asibitin da komai ya gama haɗawa waje guda, baya so Ammi tasan shirinsa saboda haka sai yayi mata karyar Kano zashi akan wasu harkokin Daddy da yake so ya fara duba wa, sosai taji dadi ta bishi da addu'a.
Kai tsaye tasha ya nufa karo na farko a rayuwar sa daya shiga motar haya, kamar akan kaya haka yake jin sa, sai dai bashi da wata hanya sai hakan. Kano suka fara zuwa kafin ya kuma samun wata motar zuwa Katsina.


Madam Inno😂 na zaune ta zabga uban tagumi tunanin rayuwar baki daya take, abubuwa da yawa sun faru, wasu ma nakan faruwa ciki har da yanayin da suke ciki yanzu na matsi da babu, duk jarin nata ya kare, ta dawo ta tsuguna sauran mazan gidan ne ke kokarin taimaka musu wani zubin da abinda zasu ci.
Nan da chan bata iya zuwa saboda yadda abinda ya faru ya gama zagaye ko ina na kauyen hatta ƙananan yara sau tari idan ta fita sai dai taji suna maganar hakan yasa ta tattara fitar baki daya ta watsar ta zauna ta fawwala Allah komai tana cigaba da jinyar Baba da ke cikin mawuyacin hali tsawon wannnan shekarun babu wani sauki sai godiyar Allah.

****
Yinin yau baki daya be duba wayar sa ba, aiki suke sosai akan wani kamfanin man gyada da yake son budewa a Niger, rabon da su hadu da Daddy yau kwana biyu kenan, shima ya zama busy sosai yana shirye shiryen ritaya ma saboda ya tattara hankalin sa waje guda, tun bayan abinda ya faru basu sake maganar Adam ba, sun barshi a matsayin ihu bayan hari ne kawai amma babu abinda zai iya, sun tuntubi Dadah da maganar tace su sake nata lokaci dole suka tattara suka ajiye komai.
Bayan ya gama duba komai ya tattare su waje guda, sakatariyar sa ya kira ya bawa ta kai office din Admin human resources sabida yana so komai ya kankama.
Babbar rigar dake jikin sa ya cire ya rataye ta a saman hanger

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login