Showing 84001 words to 87000 words out of 112633 words
Chapter 29 - DAURIN GORO COMPLET book 1 by Hafsat Rano.txt
kafin ya isa gaban dispenser ya tsiyayi ruwa ya sha sosai, sannan ya koma ya zauna yana jawo wayar tasa domin suba sakonni. Karon farko daya ji zuciyar sa tayi wani irin bugawa da karfin gaske, yasa hannu ya dafe ta yana kara bude idaon sa sosai akan sakon.
_"50million na dan ka dake amsa sunan ka KAMAL MARWAN DIKKO , 100million kuma na yar da baka san tana rayuwa ba, wadda jinin ka ke yawo a cikin jijiyoyin jikin ta, bata san kanta ba, bata san wacece ita ba,tayi rayuwar kunci da bakin ciki duk ta sanadi na."_
_"Dukkan wannan zabi ne ya rage naka ka zaba, idan kuma ba zaka iya sadaukar da million 150 ga yayanka ba, ina fatan zaka iya sadaukar da matar ka ba tare da sisin ka tayi kuka ba. Zabi ya rage ga shiga rijiya!"_ Adam
Rano 😍😍💯DG*
*36*
★★★★★
Number ya kira da sauri, ringing d'aya aka daga
"Adam, kana jina?" Yace jikin sa na rawa
"Ina jinka." Ya amsa a gadarance
"Yawwa, me kake nufi da sakon nan? Ban gane komai ba, me hakan ke nufi."
"Ina da tabbacin kai cikakken bahaushe ne ko? Lokacin boye boye ya kare ina so kaje kayi bitar abinda ka karanta da kyau zaka gane inda maganganun suka dosa, sai dai ka sani rayuwar Kamal na cikin hatsari, haka ma rayuwar yar ka da ni kadai zan iya tabbatar da hakan."
"Ya..." Katse kiran yayi ba tare da ya jira abinda zai ce ba, hanyar fita daga office din Alhaji Marwan yayi yana kokarin neman number Kamal, a kashe take cikin tsananin tashin hankali ya juya akalar kiran zuwa ga Ammi, fitowar ta kenan daga banɗaki taji wayar ta dake saman mirror na neman agaji, karasa wa tayi ta dauka
"Ina Kamal?" Yace a kid'ime
"Be dade da tafiya ba ai, na zata kunyi magana dashi kafin ya tafi, wani aiki ka bashi?."
"Ina ya tafi? Ban aike shi ko ina ba, be kuma fada min inda zashi ba, subhanallah!"
"Me ya faru?"
"Ina zuwa." Yayi saurin katse kiran yana neman layin Daddy
Hankalin ta ne ya tashi ta hau kiran layin Kamal din sai dai duk a kashe, tunanin Aminatu ne ya fado mata, bata raba daya biyu yarinyar ce tasa shi tafiya ba tare da izinin mahaifin shi ba, sannan yayi mata karya akan aikin Daddy xai je yayi, take tsanar yarinyar ya shiga zuciyar ta, ta hau zagaye a dakin tana tunanin mafita, alk'awari tayi ma kanta idan wani abu ya samu danta ba zata taba barin ta ba.
Gaba daya Alhaji Marwan ya birkice wa Daddy, tunanin sa kar wani abu ya samu Kamal d'insa, dan be san yadda zai iya dauka ba, a gefe guda kuma tunanin wacce yar tashi Adam yake nufi, iya sanin sa bashi da wata 'ya kawai Adam naso yayi wasa da hankalin sa ne tunda ya riga yasan tun bayan haihuwar Kamal din Ammi bata sake ko da batan wata bane, shiyasa kawai ya share maganar fatan sa kawai ya samu Kamal a waya yaji inda yake dan kwarai ya fara tsorata da lamarin Adam,ya soma tunanin komene akayi masa haka toh me girma ne a wajen sa.
****
Isar su Katsina ana ta kiraye kirayen sallar isha'i, hotel ya samu ya sauka da nufin da safe ya karasa garin na Shagari, baya jin dadin komai burin sa ya gano wani abu da yake da alaka dashi da Aminatu.
Be wani iya baccin kirki ba da sassafe ya shirya ya fita, asibitin ya fara zuwa da yake shi ba a cikin garin yake ba, ya tarar da wani mutum a reception, sallama yayi masa gami da mika masa hannu sukayi musabiha kafin yace
"Wani muhimmin abu ne ya kawo ni, takanas daga Abuja, ina fatan zan samu information din da nazo nema."
"Ok me kake bukata?"
"A asibitin nan aka haife ni, ga date nan da komai a jikin birth certificate d'ina, idan babu damuwa ina so ka binciko min file din da mukayi amfani dashi sanda muke zuwa Asibitin."
"Menene file number din?"
"0023."
"Ok ka dan zauna mu binciko shi, an kwana biyu zai danyi wuya."
"Owk." Yace yana samun waje.
Yana zaune mutumin ya dawo, hannun sa ya kalla ganin babu file din yasa shi cewa
"Ba'a samu ba ko?"
"Wallahi ba'a samu ba, abin mamaki duk daadewa ba'a rasa file amma wannan babu shi kwata-kwata."
"Dama nasan ba za'a samu ba. Amma dan Aallah ko zan iya sanin adadin mutanen da aka haifa a asibitin nan ranar da aka haife ni?"
"Da kamar wuya gaskiya, kaga an jima kuma mu ba wai muna da record bane cikin computer, manually ake komai dan haka gaskia ba zai yiwu ba."
"Idris ina aka ajiye file din Samira ne?"
Maganar ta ta riga ta ƙarasowa wajen, babba ce a kalla zatayi kusan sa'ar Ammi, kallon kamal tayi kadan kafin ta maida hankalin ta wajen wanda ta kira da Idris din tana masa magana,
"Wallahi Sister Asibi bansan inda aka sashi ba, ko yana wajen Lawal a tambaye shi."
"Sister Asibi?"
Sunan ya shiga masa yawo aka, idan har be manta ba shine sunan da ya gani akan file din Aminatu, sannan shine same sunan dake jikin nasa takardar, da sauri ya ciro ta ya duba, hakan kuwa ne, murmushi yayi ya bita da sauri ganin har ta kusa shiga wani office
"Dan Allah tambaya ce dani."
Ja tayi ta tsaya tana duban sa
"Ya akayi ɗan saurayi?"
"Am nidai sunana Kamal Marwan Dikko..."
"Anan aka haife ni, ranar 5 ga watan February, 1996."
"Kaga akwai ayyuka da yawa kaina, ina ganin ka nemi wani sai kayi masa bayani."
Tayi gaba da sauri, shan gabanta yayi yana bata rai sosai ganin da gaske so take ta gujewa maganar dan tun sanda ya ambaci sunan sa ta nuna alamun tsoro a idon ta
"Ki tsaya muyi magana ta fahimta kafin na sanar da hukumar asibitin, kece kika karbi haihuwa ta ko? Dan sunan ki ne a rubuce jikin takardar haihuwa ta."
"Shigo ciki."
Tace tana yin gaba, bin bayan ta yayi har wani office, suna shiga ta rufe kofar tana kallon shi
"Me kake so?"
"Ina son sanin waye ni? Me yasa sunana yayi daidai da na wadda aka haife mu rana daya, lokaci daya da ita, me hakan ke nufi?"
"Kai zan tambaya dan ban gane me kake nufi ba." Tace tana juya masa baya, murmushi yayi me ciwo kafin yace
"Ina bukatar sanin gaskiya, karki boye mun komai ki sanar dani, idan kuma ba haka ba..."
"Me kake so ka sani?"
"Waye ni? Wacece Aminatu? Ko ana so ace min mistake akayi wajen rubuta mana sunan mahaifi daya bayan an haife mu a lokaci daya a rana daya kuma asibiti daya? Ko ana so a cemin mu ɗin yan biyu ne, nasan ana iya samun suna iri daya, sai dai ba irin namu ba, hoton Daddy da Ammi dake jikin file dinta fa? Shima kuskure ne? Ba zai taɓa yiwuwav ba."
Hadiye yawu tayi me kauri ganin yadda yaron yake so lallai sai ya tono abinda ya dade da shudewa, abinda ta aikata wanda ta jima tana dana sanin amincewa zuciyar ta da tayi, kwanakin baya Inno da kanta tazo mata da rokon ta sanar da ita ko da address din inda aka kai mata dane, amma ita kanta bata sani ba.
Idon sa ne yayi ja sosai, ya sake duban ta a karo na ba adadi
"Shirun ki na nufin wani mummunan al'amari ya faru a ranar da aka haife mu, shirun ki ya tabbatar min da..."
"Tabbas nayi kuskure wajen amincewa zuciya ta, nayi dana sani mara amfani, ban taba tunanin wannan ranar zata zo ba."
"Kayi hakuri Kamal, tabbas mun zalunce ka zalunci me yawa, sai dai akan Aminatu kai gata mukayi maka, tun bayan lokacin ban sake haduwa dasu ba, sai dai har zuwa yanzu ina rayuwa ne da tunanin makomata."
"Me kike nufi?" Yace cike da dauriya dan zuwa lokacin zuciyar sa ta fara shiga mawuyacin hali
"Nice na chanja ka da Aminatu, nice sanadiyyar zaman ka duk abinda ka zama a yanzu, kuma nice sanadiyyar saka Aminatu a cikin mawuyacin hali, ba tare da sanin mahaifanta ba,son zuciyar mahaifiyar ka shine mafarin komai, da bata amince ba babu yadda zatayi hakan ta yiwu tunda ita lafiya lau ta haife ka tasan me ta haifa."
Dip ya daina ji kwata kwata, tsawon dakika biyar tana cigaba da jera masa bayanin da baya iya jin komai, a hankali jin sa ya soma dawowa, jiri ne ya kwashe shi yayi saurin dafa bangon office din, da sauri ta sa hannu zata tare shi ta dakatar da ita
"Menene kwatancen gidan?"
"Idan kaje ka tambayi gidan Inno babu wanda be santa ba."
"Waye ya saki aikata mana wannan mummunan aiki?"
"Bansan shi ba, sai dai na san sunan sa a lokacin da naji matar ta fada masa, Adam idan har ban manta ba, shi ya bamu kudi domin mu yi masa wannan aiki, ni, harira da mahaifiyar ka sai mace daya da suka zo tare, wadda ta zama wakiliyar sa dan ita muka sani bashi ba ."
Girgiza kansa yayi cikin sarkewar murya wanda yake jin numfashin shi na kokawa da gangar jikin shi ya soma magana
"Allah ya isa tsakanin mu daku, bazamu taba yafe muku abinda kukayi mana ba, ina rokon Allah ya wulakanta ku tun a duniya, ya bi mana hakkin zaluncin da kukayi mana."
Kofa ya nufa yana layi, kafin ya juyo yace
"Ki jira abinda zai biyo baya dan ba zan yafe miki ba, Shari'a ce zata raba mu."
"Dan girman Allah ka tsaya ka saurare ni."
Bugo kofar yayi da karfi, ta zauna dabas a kasa tana rike kanta, ina zata kama? Shari'a da Marwan Dikko ba abu ne me sauki ba tasan tabbas zai iya sakawa a rufe kaf dangin ta. Da sauri ta mike ta zari jakar ta ta fita da kofar baya.
***Da taimakon wani direbab mota daya dauka shata suka isa cikin garin, duk da dauriya kawai yake yi amma bashi da karfi da kuzarin tunkarar abinda yake tunkaro shi din. Tambaya sukayi aka nuna musu gidan, da ido ya shiga duban gidan da ya sake lalacewa ainun, yanzu mutane ne ke rayuwa a ciki? Ya tambayi zuciyar sa, a take ta bashi amsa da mutanen ma iyayen da suka kawo ka duniya, chije bakin sa ya yi ya fitar da iska mai zafi yana tuna girma da kyawun gidan su na Abuja, tabbas Aminatu ita aka cuta, aka sata rayuwa a muhallin da har ta bar duniya ba zata taba rayuwa a cikin sa ba, kwalla ce ta zubo masa yasa hannu ya goge.
"Sannu da zuwa."
Nura yace yana fitowa daga cikin gidan, saurin daidai ta kansa yayi ya mika masa hannu,tunanin Abinda zai ce mishi yake, sai yaji yace
"Wa ake nema?"
"Nan ne gidan su Aminatu?" Yace
"Nan ne, kana da labarin inda take ne dan Allah?" Ya amsa cike da zumudi,
"Zan iya ganin mahaifiyar ta?" Yace yana dauke wanchan maganar
"Bismillah shigo ciki." Yayi gaba da sauri, dan jim yayi kadan kafin ya kutsa kansa cikin makeken zauren gidan daya cika da yana.
"Inna, inna fito ga wani yazo ganin ki kuma da alama yasan inda Aminatu take."
"Yana ina?"
Ta tashi a zabure, tsaye yayi a bakin kofar ya kasa karasowa ciki, wannan itace mahaifiyar sa data zabi kudi akan sa, mahaifiyar data raini Aminatu a cikin kaskanci da tozarci bayan nata dan na cikin gata da jin dadi
Sararo tayi tana kallon sa, cikin sakannin da basu gaza biyar ba, ta kare masa kallo, kallon daya tabbatar mata da zargin ta, da sauri tayi kansa tana duban damtsen hannun sa dake bude cikin riga me gajeren hannun daya sa, katon tabon da aka haife shi dashi wanda shine abu na farko data fara gani sanda yazo duniya ta shiga bi da kallo, da hannu ta shiga nuna shi sai dai ta gaza furta kalma daya, tana kokarin riko hannun nasa yaja baya da sauri
"Kamal MD kamar yadda kike hasashe! Ina fatan kina cikin koshin lafiya bayan abinda kika aikata."
"Na shiga uku Nura, wallahi tallahi dana ne, shine dana wallahi shine, wallahi shine."
"Inno me kike fad'a, ni ban fahimci komai ba fa."
Cigaba da matsowa tayi tana kokarin riko shi yayi saurin ja baya yana bata fuska sosai
"Karki taba ni, karki fara! Ba abinda ya kawo ni kenan ba, ina so naga kalar rayuwar da kike yi, alhamdulillah na gani, yanzu zan koma inda na fito."
Yana kaiwa nan yayi waje da sauri, biyo bayan shi tayi tana kwala kiran sunan shi amma ko waiwayowa bai yi ba, motar ya fada da sauri ya umarci me motar su tafi.
"Na shiga uku Nura, wallahi tallahi dana ne, kana gani ya tafi amma baka tsayar dashi ba."
"Idan har da gaske shine, kina zaune zai dawo da kafafun sa, waye ya kawo shi yanzu? Ra'ayin kansa ko? Toh shi zai dawo dashi kiyi shiru karki tara mutane."
"Shikenan nayi shiru."
Tace tana kama bakin ta kamar yarinya karama. Ciki suka koma duk ta kasa komai data rufe idon ta hoton fuskar sa kawai take gani, ta girma sosai ya zama babban saurayi me ji da kyau da gayu, shigar sa kadai ta tabbatar mata da shi din waye, anya zai karbe ta a matsayin mahaifiyar sa kuwa? Yanzu da bata da maraba da mahaukaciya duba da yadda duk ta lalace ta koma kamar wadda tayi jinya ga babu suturar arziki.
***
Ganin an kwana babu labarin Kamal yasa Alhaji Marwan baza jami'an tsaro sosai aka shiga neman sa, banda kuka babu abinda Ammi take, hakan ya karawa mishi damuwa sosai dan ba Hajiya Turai bata san wainar da ake toyawa ba.
Dakin sa ta shiga ta tarar dashi yana waya, zama tayi a gefen sa idon ta duk ya ɓaci saboda kukan dataa sha, ajiye wayar yayi bayan ya gama ya dube ta cikin kulawa yace
"Ki kwantar da hankalin ki in Sha Allah za'a ganshi."
"An kira yarinyar da yake zuwa gani a Kano? Ina zargin ta dama ni chan hankali na be kwanta da ita ba."
"Sirikar Aminini ce ashe, yarinyar da muke ta fafutukar nema ashe jikarmu ce, dan haka bani da matsala da yarinyar, idan kika ganta ma nasan kema irin ta Kamal din zakiyi, ki ji ta kwanta miki."
"Bana son ta gaskiya, karo na farko dana fara jin mijina yana yabon wata bani ba."
"Kishi?" Yace yana murmushi, gefe ta kawar da kanta tana bata fuska.
"Kinsan Adam yana raye?" Yace yana duban ta, duburburce wa tayi tace
"Ban gane ba?"
"Hello inspector." Yace yana daga wayar
"What!!!" Ya mike tsaye da sauri
"Gani nan zuwa." Ya katse kiran yayi hanya da sauri
: *DG*
*37*
©Hafsat Rano
★★★
Tafiya yake ba tare da yasan inda yake taka ƙafarsa ba, so yake yayi kuka ko zaiji sauƙin zuciyar shi, sai dai ashe kukan ma samu ne, tsawon shekarun nan yana rayuwa ne da mutanen da bashi da alaƙa takusa ko ma ta nesa dasu, mahaifiyar data kawo shi duniya na rayuwa a wani waje cikin tsananin talauci, da kunci, tabbas ba'a kyauta masa ba, sai dai akan Aminatu kusan shi gata akayi masa, rayuwa ce yayi ta cikin tsananin gata da dadi, ita kuwa aka dora mata rayuwar da bata dace da ko da me aikin gidan ba balle ita, ya ɗaya tilo da take buƙatar dukkan gata, gata mace me rauni.
Tunanin ta yadda zai fara sanar da kowa komai yake, idan har ya cigaba da boye gaskiyar abinda ya sani be kyauta wa Aminatu ba, haka be yi adalci ga iyayen da suke rikeshi bisa amana ba, suna bukatar yar su, itama tana bukatar iyayen da zasu nuna mata gatan data rasa.
Idon sa ya runtse tuno labarin rayuwar ta data bashi, da irin abubuwan data fuskanta, ya tausaya mata kwarai sai dai a yanzu shine abin a tausaya wa, rashin sa'ar iyayen k'warai masu nagarta.
"Baka gaji da tafiyar kasan bane?"
Ya tsinkayi wata murya a saman kansa, juyowa yayi ya kalli mutumin
"Ya kamata ace ka dan huta ai, bayan ka gano komai me ya kamata kayi?"
"Me kake nufi?" Ya katse shi yana duban shi
"Ina biye dakai tun barin ka gida, na kuma san abinda ya kawo ka, ina fatan bayyanar gaskiya be saka ka yanke hukunci da rayuwa ba."
"Me yasa kake bina, ina kuma ruwan ka da rayuwa ta, waye kai ma a takaice.?"
"Wanda ya chanja maka rayuwa daga ta tsantsar talauci zuwa mafi kuloluwar daraja."
"Adam!" Yace yana zaro ido
"Nine, Ina fata haduwar mu ba zata zamar wani babban al'amari ba."
"Me nayi maka? Me yasa ka zabi da kayi wasa da rayuwa ta?"
"Idan kace wasa da rayuwa kana nufin ban kyauta maka ba, dubi suturar jikin ka, ka dubi kanka, kana tunanin ban maka gata ba? Toh ka bude kunnen ka kaji.."
"Ina so abin da ka binciko ya zama tarihi a ranka, wajibi ne ka boye komai ka cigaba da rayuwar dana zaba maka, idan baka sani ba, MD ne ya zabarwa yarsa irin rayuwar da take, shine silar komai, ya rabani da abubuwa guda biyu mafi soyuwa a gareni, shiyasa na zabar wa abinda zai haifa rayuwa mafi kaskanci."
"Karya kake wa Daddy, babu abinda yayi maka karya kake, kuma wallahi sai na tona komai ko da zan dawo rayuwa ta ta asali."
Murmushi yayi gami da cije lebensa na kasa
"Idan har na bar maka damar yin hakan ko? Yaro kenan, sunana kawai kake ji amma na wuce tunanin ka."
"Ta Allah ba taka ba, duk abinda kake kullawa sai ya koma kanka."
Hannu Adam ya harde yana duban shi, tafiya Kamal ya cigaba da sauri da sauri ba tare da ya sake waiwayo wa ba.
A wani irin yanayi iska ta dauki karar motar ta kai masa kunnuwan sa,da sauri ya juyo kafin ya iya tantance komai tayi sama dashi. Ƙarar daya kwalla ita ta jawo hankalin mutanen dake wucewa ta wurin jefi jefi.
*****
A kid'ime yayi waje yana kwala wa Driver sa kira, kuka Ammi tasa tana binsa ganin kamar baya hayyacin sa
"Dan Allah ka sanar min abinda ya faru."
"Kamal ne ya hadu da accident a Katsina."
Abinda kawai ya iya cewa kenan ya fada mota, kuka ta saka me karfi ta fado motar.
Wani irin gudu driver yake kamar zai tashi sama, babu abin da kake ji sai sautin kukan Ammi, ikon Allah ne kawai ya kaisu, direct