Showing 75001 words to 78000 words out of 112633 words
Chapter 26 - DAURIN GORO COMPLET book 1 by Hafsat Rano.txt
da ta bata... Menene alakar ki da ita?"
" 'Yata ce!"
Na amsa kai tsaye ina sake sakin wani sabon kukan, tashi yayi yana zagaye dakin hankalin sa a matukar tashi, kenan da gaske bayan rabuwar su Da Farouk ta haifi abinda ke cikin ta har ma ta girma, idan haka ne yarinya ce wani tsani na warwarar wasu daurukan da har yanzu ya gaza warware su.
Da wani irin sauri ya mika hannu ya karbi wayar dake hannun Alhaji Marwan, kai tsaye ya shiga jerin sakonni ya fara dubawa, a kan sakon ya tsaya yana sake dubawa duban tsanaki, "abin da sukayi tarayya akai, ba tare da sanin su ba..."
"MD!" Ya kira shi da d'an karfi
"Yarinyar Farouk ce, ita ce ake magana a wannan text message ɗin, waye shi? Me mukayi masa da yake son ganin bayan mu?"
"Kana nufin abinda text ɗin ke nufi kenan?"
"Eh duba kaga, ya zama dole mu nemo shi ko waye, shine yake da amsar dukkannin tambayoyin mu."
Shiru nayi lokaci daya naji kukan ya dauke min, nauyin dake lullube a zuciya ta naji ya soma raguwa a hankali, sai dai ido na daya ke min wani irin zugi kamar na zuba masa yaji, su kadai yanzu suke maganar su sai Kamal daya zuba ido baya fuskantar komai, ni ɗin ma ba wani fuskanta nake ba, sai dai tabbas akwai wata kullaliya da ta saka aka sace min yata, kenan akwai me bibiyar rayuwa ta har bayan barin kauyanmu. Amal ce ta fado min, da ita kadai na taba haduwa har ta nuna min babu wata alaƙa tsakanin mu, ance zato zunubi sai dai a take zuciya ta ta shiga ayyana min ko tana da hannu a cikin batan Iman?
***
A kofar gidan Driver ya ajiye ta, fuskar ta sanye da bakin glass, ta sakala earpiece a kunnenta da alama waya take amsawa, sai data gama amsa wayar sannan taja jakar kayan ta ta shiga gidan, da mai aikin Dadah suka fara karo, bata ko bi ta kanta ba tayi hanyar falon tana yatsine, da gudu da fada jikin Dadah tayi saurin ture ta tana matsawa gefe
"Yar nema karki karya ni."
"Nayi missing dinki ne Dadah."
"Naji, tare kuke da Baban naku ne? Yayi min waya sun shigo garin tun dazu nake baza ido."
"Wai Daddy, ban masan yana nan ba, sai anjima kila idan ya gama abubuwan da ya kawo shi."
"Haka ne, ya mutanen gidan ya kowa da kowa?"
"Lafiya wallahi, bari n huta nazo naci abinci dan yunwa nake ji."
Ta mike tana jan jakar ta ta nufi daki.
***
Sai da suka gama komai sannan muka fito, Daddy ne ya dubi Farouk yace
"Kasan gidan Dadah ko?"
Soso kai ya hau yi yana kallon Alhaji Marwan, da sauri yace
"Yanzu duk zaman ka garin nan baka taba zuwa ba?"
"I'm sorry Dad." Yace yana matsawa dan yasan sauran bayanin
"Toh sai ku biyo mu a baya, chan zamu wuce Aminatu, ba zan iya bawa Dadah labarin da nake so na bata ba tare da ta ganki ba."
Amsawa nayi da toh muka bi bayansu zuciya ta na wani irin bugawa ina jin tsoron abinda zan tarar.
****
Sanye yake da dogon wando da riga longsleeve ya nade wuyan sa da abu mai kauri, hannun sa rike da Amir karamin dan uncle Aliiyu, bayan sa rataye da Jacket ɗin sa daya zare tun da suka ido Nigeria, cikin kankanin lokaci suka gama komai a airport dib suka tari cab kai tsaye suka nufi gidan Dadah bisa umarnin Uncle Aliiyu.
Kallon ko ina yake babu abinda ya sauya a dan tafiyar da yayi, kai tsaye unguwar suka shigo daidai lokacin da motar su Daddy ta tsaya a kofar gidan, runtse idon sa Farouk yayi yana tuno abinda yasa shi barin kasar gashi ya dawo dashi ba tare da sanin yadda zai tunkari mutanen da suka zama masa wani jigo na rayuwa ba.
Two hearts are about to reunite🏌️🏌️🏌️🏌️🏌️🏌️🏌️🏌️
idan kun shirya nima na shirya, let the game begins 🏇🏇🏇🚴
Idan na samu chargy zaku jini anjima. Manage dis wayata 3%*DG*
*33*
★★★★★
Tun kafin su k'arasa suka fito, Daddy ne a gaba Alhaji Marwan na biye dashi, sai kuma motar Kamal da ke tsaye a bayan tasu Daddyn, wani irin farin ciki ne ya lullube Uncle Aliiyu ganin mutanen da yake da muradin gani tsawon lokaci.
Rufe ido Farouk yayi ya kwanta sosai a jikin kujerar motar, a daidai lokacin Kamal da Aminatu suka nufi cikin gidan, har suka gama fita daga motar be dago ba sai da Uncle Aliiyu ya tab'a shi, kamar ba zai sauko ba sai kuma ya saki ajiyar zuciya ya fito yana kallon sararin samaniya.
Anty Safiyya ce a gaba yaran na binta sai Uncle Aliiyu da suka jera da Farouk yana mishi bayanin sauye-sauyen da ya gani.
A daidai lokacin Dadah na tsaye gaban fanfo tana daura alwala, da fara'a ta tarbe su maganar da take kokarin yi ta makale ganin wadda bata taba tunanin gani ba.
"Wa nake gani kamar Aminatu?"
Tace a dan kideme, tana matsowa inda nake tsaye kamar an dasa, tsananin farin cikin da nake ciki bazai misaltu ba.
Murmushi Daddy yayi
"Yau sai a bani tukwuici na ga Aminatu na kawo miki har gida."
Kukan farin ciki ta saka ta rungume ni jikin ta, kukan da nake kokarin rikewa ya kwace min muka shiga yi a tare, a yau na kara tabbatar da kaunar da matar take min, kenan sun koma nema na bayan na bar kauyanmu, wannan shine soyayya ta gaskiya ba tare da wani abu ba.
Sallamar Anty Safiyya ta katse dukkan me shirin magana, duk suka zuba mata ido cike da tsantsar mamaki, takawa take kamar wadda take tsoron yadda zasu karbe ta. Har ta tsaya a gaban Dadah babu wanda ya iya furta komai, shigowar Uncle Aliyu, Farouk biye dashi kansa a kasa kamar baya son ganin kowa ya kara jefa su cikin rudani, saki na Dadah tayi tayi wajen Anty Safiyya bakin ta a bude, yaran dake gefen ta, ta shiga bi da kallo daya bayan ɗaya tana kallon fuskar mahaifiyar tasu.
"Kabiru me yake faruwa, wa nake gani kamar Aliyu, Safiyya da Babana? Ban gama dawowa daga mamakin ganin Aminatu..."
A rikice Farouk ya dago jin an ambaci Aminatu, a lokaci daya ya dira a gabana, idon sa cikin nawa yake duba na, cikin wani irin yanayi da bazan iya misalta shi ba, rawa bakin sa ya soma kafin da kyar ya samu nasarar furta kalmomin a rarrabe,
"De..s...ti..ny."
Sai ya rike hannu na da sauri ya shiga jana yana kokarin barin gidan, Alhaji Marwan ne ya dakatar dashi ta hanyar rike shi, ya kuma bata rai sosai yana nuna masa ciki, daya bayan daya ya shiga bin mutanen dake tsaye a wajen kowa da kalar kallon da yake mana, sai kuma ya sauke idon sa akan Dadah dake kuka sosai, kukan daya sanyaya jikin kowa har aka rasa wanda zai iya cewa komai.
"Mu shiga ciki."
Alhaji Marwan daya fi kowa karfin hali yace yana nuna masa hanyar falon, mai aikin Dadah ce ta rike ta muka dunguma zuwa cikin falon har lokacin hannun sa sarke yake da nawa, kaina a kasa na gaza kallon sa, wani irin yanayi ne ke shiga ta yana bin kowanne lungu da sako na magudanar jinin jikina.
A kasa muka zube tare yaki saki na kuma, idon sa akaina baya tuna duk mutanen dake falon da matsayin su gareshi.
Kan Uncle Aliiyu na saman cinyar Dadah yana share hawayen dake faman reto a saman fuskar sa, girma da shekarun sa basu hanashi zubar da hawaye a wannnan lokacin ba, domin yana bukatar hakan. Saboda haka babu wanda yayi yunkurin tsaida shi sai daya gaji dan kanshi ya zauna sosai yana duban dukkan yan falon.
"Na tabbata duk wanda yake gurin nan yayi mamaki ganin mu, bayan shudewar lokaci da ina kyautata zaton babu wanda ya sake tunawa da Aliyu da matar sa Safiyya, sai dai mu bamu taba kwana ba tare da mun tuna da ku ba, duk da ba wai ina tuhumar ku bane, hakan ya faru ba tare da sanin daya daga cikin ku ba, haduwar mu da Farouk shine silar dawowar mu, wanda dama abinda muke jira kenan tsawon wannan lokaci da muka kasa dawowa din."
"Kamar yadda kuka sani, ni Aliyu na bar gida ba tare da sanin daya daga cikin ku ba, sai dai bani da zabi illa na tafi, dan a lokacin da na tafi bana cikin hayyaci na, ji nayi ba zan iya zama ba dole sai na tafi, da fari jihar fatakwal na fara yada zango duk da ba a bisa son raina ba, so nake kawai na bar kasar a lokacin, daga bisani Allah ya taimake ni na nemi gurbin karatu a jami'ar Cranfield dake birnin London, na samu, hakan ya saka na tattara na bar kasar ba tare da tunanin sake waiwayar kowa ba.
"Tafiyar da nayi da Safiyya ita ta taimaka min wajen tuna wanene ni, sanda na dawo hayyaci na hankali na yayi matukar tashi naji bana son sake kwana a kasar, bayan mun gama shirye shiryen komai ranar da zamu tawo na dan fita ina karasa siyan abinda zamu bukata na hadu da Adam, nayi mamakin ganin sa a kasar kuma ga dukkan alamu ba bakon kasar bane, take abinda ya faru ya dawo min, rai bace na tare shi zan soma magana yace
"Sako nazo baka, ka tabbata kai da barin kasar nan sai bayan cikar buri na, duk ranar da ka hadu da wani cikin mutanen dake da kusanci dakai, a rana zaka iya komai, sai dai ina maka albishir kai da haduwa da wani sai bayan ranka, kamar yadda kaso ka tona min asiri haka zaka kare rayuwar ka cikin kunci da dana sani."
Juyawa yayi ya bar wajen ban iya ce masa komai ba, kiran daya shigo wayata na maida hankali wajen dauka, kukan dana ji Safiyya nayi yasa jikina ya hau rawa, a nan take sanar min da an shigo an kwashe komai da zamu bukata wajen barin kasar, hatta yan kudaden da suka rage mana an kwashe komai, tun daga lokacin bamu sake samun damar barin kasar ba, haka muka cigaba da zama a kasar muna addu'ar Allah ya kawo mana karshen wannan musibar.
Toh kamar yadda kowa ya sani, Adam ya mutu a idon duniya, amma yana nan yana yawo a doran kasa yana aikata mugayen abubuwa, ina fatan wannan bayanin nawa zai saka Dadah ta sanar da kowa wani boyayyen sirri da ta sani, wanda sanin dana yi ya jefa ni a matsala, amma kafin nan ina neman alfarma ya zama a gaban Anty Abidah, domin a lokacin nake so komai ya warware, ina son na cika mata burin alkawarin dana yi mata na wanke ta daga zargin da ake mata."
"Kana nufin Adam yana raye?"
Daddy ya jeho masa tambayar kansa a daure cike da mamakin abinda Aliyun yace,
"Yana nan da ransa." Ya amsa kai tsaye
"Ikon Allah."
Ya dora
"Sai dai nasan yarda da hakan ba mai yiwu wa bane lokaci daya, ina bukatar lokaci dan tabbatar da haka."
"Me akayi masa haka mai zafi da yake kokarin ganin bayan mu?"
Yace yana duban Dadah data sauke kanta kasa, murmushi Uncle Aliiyu yayi, ya kalli Dadah ya kama hannun ta ya rike cikin nasa
"Ki taimaka ki sanar da kowa abinda kika sani, ke ce mahaifiyar mu dukka, ke kika haife mu saboda haka karki ji tsoron komai babu abinda ya isa yayi miki sai abinda Allah ya ƙaddara miki."
Kuka ta saka tana tuna abubuwan da suka faru, wanda take ganin kamar a lokacin suke faruwa ko kuma taso da maganar na iya saka komai ya kara tabarbarewa.
"Zan neme ku, kuyi hakuri yanzu." Tace tana goge fuskar ta
"Shikenan Allah ya kaimu."
Suka hada baki a lokaci daya, kallon Farouk Daddy ke tayi ganin yayi biris da kowa na falon kamar be san da zaman su ba, idanun Dadah na kansa haka ma Uncle Aliiyu na lura dashi tun zuwan su.
"Farouk!" Ya kirashi
Dagowa yayi yana duban sa cikin girmamawa yace
"Na'am."
"Baka gaida kowa a falon nan ba, ina fatan baka manta su waye a zaune a gaban ka ba ko?"
Kwarjini yaji yayi masa, idan ba haka ba bashi da niyyar tanka kowa a cikin su, musamman Daddy Da Dadah, wanda yake ganin sun fi kowa rashin son shi bayan yana da yakinin su suke fi kusanci dashi. Bai manta abinda Dadah tayi masa ba, ya kuma kasa tantance a wanne matsayi zai ajiye ta, ganin da yayi mata a yanzu kawai yaji yana bukatar tuntubar ta akan abinda ta aikata masa, yana so yaji dalilin ta na yin haka, a darare kamar wani bako yace
"Fatan na sami kowa lafiya."
Tsananin mamaki ya kama Daddy, ya gaza cewa komai sai Dadah ce da Alhaji Marwan suka amsa masa.
****Kiran sallar magriba yasa kowa ya mike domin gabatar da sallah, daki Dadah ta nuna min tace naje na yi alwala nayi sallah, ban mata musu ba sai dai ina so na tafi gida, nasan duk inda hankalin Baba Altine yake ya tashi yanzu, dan ma na sanar da ita in da na tafi ne.
Tana kwance na shiga dakin, ta ɗora kanta a saman pillow da alama bacci take kuma tana jin dadin baccin nata, kofar dana gani dake nuna alamun toilet na wuce ina tuna ranar dana hadu da ita da abubuwan data fada min.
Mik'ewa tayi jin wayar ta dake gefen ta nata vibration, ba tare da sanin ina ciki ba ta daga,
"Kina jina? Tashi maza ki duba min bakin da akayi a gidan, ki gani idan akwai Namiji Babba da matar sa da yara uku, yi maza ina jiran ki."
"Toh..." Tace tana mik'a, mikewa tayi ta tsaya tana duba fuskar ta a gaban mudubi kafin ta fita, babu kowa a falon sai Amir da Amrah babban yabi su Daddy masallaci, kallon su tayi kallon su waye ku kafin ta wuce dakin Dadah ta leka, Anty Safiyya na kan sallaya tana sallah dake gefe Dadah na gabatar da tata sallar ita ma, dan jim tayi kafin ta juya zuwa dakin nata, bata lura dani akan abin sallah ba, ta dauki wayar ta ta kira shi
"Na duba, naga yara biyu a falo sai wata mata a dakin Dadah tana sallah."
"What!" Yace cikin k'araji
"Da gaske kenan Aliyu ya dawo, Amma how comes?"
"Waye shi?" Tace tana zama
"Shine wanda ya raba ki da mahaifin ki tun kina tsumma, yanzu ma kuma zai sake wargaza min aikin dana jima ina yi, Amal so yake ya kashe miki uba ki zama marainiya gaba da baya, will you allow that?"
Da sauri ta girgiza kai
"Ba zan taba barin shi ba, nima ina bukatar uba kamar kowacce 'ya."
"Then zaki yi yadda nace?"
"Zanyi." Tace kai tsaye
"Good girl, zan kiraki anjima."
"Ok." Ta ajiye wayar, wayun bakin tane ya makale ta hau murza idon ta da sauri, kallo na tayi, nima na zuba mata ido babu ko daukewa bayan na gama sauraron wayar da tayi zan iya alakanta hakan da maganganun da naji anayi dazu.
"Me kike yi anan, yaushe kika zo gidan nan, waye ya kawo ki gidan nan?"
"Wanne kike so na amsa miki aciki?"
Nace mata ina murmushi
"Ni na kawo ta!" Ya shiga takowa cikin dakin yana kallon ta, sake shiga rudu tayi da sauri tace
"Ya Farouk!"
Daga mata hannu yayi
"Karki kuskura, kinji na fada miki."
Kasa nayi da kaina, ya iso gaban sallayar ya zauna yana tankwashe kafar sa, leka fuskata ya shiga yi, ganin naki yarda na kalle shi yasa shi sa hannu ya daga min fuskar.
"Gudu na kike Aminene? Nine Farouk dinki fa."
Gefe na kauda fuskata ina jin zafin abinda yayi min a baya, na farko saki na biyu ƙaryata abinda yake tsakani na dashi, wanda shine Ummul aba'isin jefa ni cikin gararin rayuwa.
"Please dan Allah kiyi min magana, shekara nawa? Kinsan yadda na azabtu da rashin ki? Kinsan wacce irin rayuwa nayi bayan na rasa ki? Dan Allah kiyi min magana."
Kamar tatsuniya haka nake jin maganar tasa, idan har abinda yake fada gaskiya ne me yasa ya rabu dani, yunkurawa nayi da nufin tashi ya sa hannu ya maida ni baya
"Wallahi baki isa ba, duk tsawon lokacin nan dana yi ba tare dake ba amma kiki cewa komai, haushi na kike ji? Me nayi miki?"
A zafafe nace
"Baka san abinda kayi min ba Ya Farouk? Baka sani ba? All this while ni kasan irin rayuwar da nayi? Why are you selfish? Shikenan nice me laifi saboda bani da gata balle galihu, daka tafi ka barni da ciki ka taba tunanin halin da zan shiga? Ka taba? Ka sake ni bayan ka koya min sonka, na shaku da kai na soka,amma nice abar tuhuma ko..."
Kuka ne ya taso min, na sake shi ina saka fuskata cikin cinyoyi na, be hanani ba, ina jin yadda numfashin sa yake kai kawo a saman kaina, tashi naji yayi, ya isa wajen da Amal ke zaune tana sharar kwalla yasa hannu ya fizgota ya dire ta a gabana
"Ki faɗa mata, ki faɗa mata komai da kula kulla ke da munafukan da suka tayaki, kin fi kowa sanin bani da laifi akan abinda take tuhuma ta, ki faɗa mata ko na kakkaryaki a wajen nan wallahi Allah."
"Ni...ni bansan komai ba." Tace cikin kuka, shaka ya kai mata ta shiga kakari, da sauri na shiga tsakani ina masa kallon mamaki
"Me kake yi haka? Dukan mace ya Farouk!"
Jin haka yasa shi sakin ta da sauri yana zama gefen gadon hannun sa rike gam da kansa, juyawa nayi na bar dakin da sauri, lokacin duk sun dawo suna zaune a falon, a gaban su Daddy na durkusa Ina share fuskata
"Zan tafi Daddy, dare yanayi."
"Eh kuma haka ne, na manta shaf Aminatu, ina farouk sai ya maidake, duk da zanso ki dawo nan ɗin amma for now tunda munsan inda kike shikenan."
"Aminatu." Dadah ta kira sunana, matsawa nayi gaban ta ta kamo hannu na
"Naji abinda ya faru, in Sha Allah za'a ganta, ki cigaba da addu'a kinji, sannan zaki dawo waje na zanzo da kaina har inda kike, kiyi hakuri kinga abinda kika tarar karki ga ban baki lokaci ba."
"Babu komai." Nace ina musu sallama, har waje ta rako ni kafin ta koma ciki.
"Wai kinsan