Showing 15001 words to 18000 words out of 112633 words
Chapter 6 - DAURIN GORO COMPLET book 1 by Hafsat Rano.txt
magana da driver, muna fitowa ya bude mana baya muka shiga shi kuma ya zauna a gefen me zaman banza driver ya data motar muka fita daga gidan. Tunda nazo yau ce rana ta farko dana fita, murna sosai nake ina jin kamar muyi ta dawwama a irin yanayin da muke ciki a yanzu, kadan kadan nake tunawa da yan gidan mu shima ba ko yaushe ba, yawanci nafi tunawa dasu idan Amal tayi bacci ta barni. Bani da sauran matsala komai muke so mukeyi, sai nake jin kamar nafi kowa sa'a a duniya.
Fita daga kauyen namu mukayi baki daya muka shiga cikin gari, a bakin wani babban shago muka tsaya,ya Farouk ne kaɗai ya fita ya bar mu a motar, chan ya dawo da kaya ya zuba a booth sannan muka nufi wani shagon, haka mukayi ta yawo daga nan zuwa nan wani wajen ya shiga damu wani ya bar mu a mota. Bamu muka dawo ba sai yamma likis cike da gajiya dan Amal tun a hanya tayi bacci ta barni.
****Tun daga ranar muka fara karatu da Ya Farouk, kullum da abinda zamuyi, chan baya muke tafiya mu saka babar darduma mu baje sai mun gaji sosai yake kyale mu musamman ma ni, dan mafi ya yawan lokuta ni yake wa karatun dan ita Amal ta wuce wajen.
Muna cikin wannan yanayin Daddy ya turo aka tafi da Amal, ranar nayi kuka sosai nace lallai sai an maida ni gidan mu, da kyar shi da Dada suka shawo kaina na hakura na zauna, amma bani da wani kuzari tun bayan tafiyar ta ta wadda Dada tace min sun koma makaranta ne kuma ba nan kusa bane. Haka dai na hakura na cigaba da daukar karatu da yanzu yafi min komai a rayuwata.
Wata na hudu cif a gidan, sau biyu su Karime suka zo ita da yan gidan mu suka wuni, suka tafi, anan ne suke fada min ai aure akayi min shiyasa nake zaune anan, kuma Inno ce take hanasu zuwa shiyasa. Ban dauki zancen nasu da muhimmanci ba, haka na tattara na cigaba da sabgata saboda ba karamin sabo nayi da Ya Farouk ba, gashi kusan kullum sai ya kira min Amal da daddare munyi waya.
Ranar da bazan taba mantawa da ita ba, nayi bacci na tashi kenan, dakin ya Farouk na nufa da sauri na ina tunanin ko ya zo tashi na ya ga ina bacci ya gudu bayan yayi min alkawarin yau zai kaini gidan mu har na wuni, kwana yace zanyi na fafure nace sai dai yini, yayi ta min dariya yana tsokana ta, ban damu ba,dan zama na anan ɗin yafi min dadi musamman ma saboda karatun da nake yi.
Tura dakin nayi na shiga bayan na kwakwasa ya bani izini, Yana lullube a bargo ya rufa har kansa, kiran sunan sa na fara yi ina k'arasa ciki. Cikin muryar bacci ya amsa min, dariya nayi na haye kan gadon ina jan bargon dan nasan ba bacci yake ba, mafiya yawan lokuta ya saba yi min hakan. Rike bargon yayi yana ja ina ja har na samu na bude masa fuskar sa.
"Laaa bacci karya fa kake ya Farouk." Nace ina dariya, bude idon sa yayi cikin yanayin bacci ya zuba su a kaina
"Bacci nake fahhh..." Ya fada cikin wata irin murya kamar ba tasan ba, jan bargon yayi ya sake rufawa nayi saurin janye wa ina sake yin dariya
"Ni dai ka tashi, ba kaine kace zaka kaini gida yau ba."
"AMINATU pleaseeeeee..., bacci anjima zan kaiki."
'Dage kafada nayi na sake janye bargon ina bubbuga masa damtsen hannun sa. Da wani irin karfi nayi ya riko ni, gaba daya na shige cikin jikin sa, ya jawo bargon ya rufa akanmu. A tsorace nake kallon sa, idon sa a kulle ya sake maidashi ya rufe, zura wa fuskar sa ido nayi kamar wadda ta fara ganin sa, na kasa kwakkwaran motsi, balle na yi yunkurin tashi. Takun tafiya naji yana tunkaro dakin, hade da karar abu kamar ana jan wani abu, janye bargon nayi daga saman fuskar mu na zuba wa kofar shigowa dakin ido tun da dama dana shigo ban rufe ta ba ina sauri. Cikin wata irin shiga ta alfarma, me cike da haiba tayi wa kofar dakin tsinke, tsaye take janye da yar karamar jakar matafiya, sai handbag din ta dake sakale a sangalalin hannun ta. Cikin mintuna da basu gaza biyar ba nayi mata kallon tsaf, yadda naga ta buda idon ta sosai akanmu ya ɗan tsorata ni, cikin tsananin mamaki naji ta kira sunan sa da d'an karfi.
"Son!"
A firgice ya dago idon sa ya sauka a kanta, yayi wani irin tashi da dukkan karfin sa har yana ture ni daga jikin sa, cikin sakin bakin ya furta
"Mom!"
DAURIN GORO😢😢😥😥😓
ZAFAFA BIYAR
KAUNAR MU: MAMUH GEE
ALKAWARIN ALLAH; HUGUMA
GUDU DA WAIWAYE: BILLYN ABDUL
DAURIN GORO:HAFSAT RANO.
IGIYAR ZATO: MISS XOXO
LITTAFI DAYA 200
BIYU 300
UKU 400
HUDU 450
BIYAR 500
*_ZAKU BIYA KUDI TA BANKI TA WANNAN ACCOUNT DIN👇👇_*
2260792279
_MARYAM SANI_
_ZENITHBANK_
saiku tura shaidar biyanku ta maana screenshot ta wannan layin👇👇
*07067124863*
*_GA MASU TURA KATIN MTN SAISU TURA KATINSU ZUWA GA WANNAN NUMBER TAREDA TURA MATA SHAIDA_*👇👇
*09032345899*
_Sayen nagari, maida kuɗi gida masoyan asali😉😻🥰🥰😍😍😘😘👌🏻💃🏻💃🏻_
©️®️HafsatRano
*ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER*
07067124863
*Ko kuma*
09032345899
*ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sababbi,karku manta ku dannan SUBSCRIBE kuyi LIKE sannan kuyi SHARING*🙏🏽
https://youtu.be/Zyl7_eSgXuo
(8)
***
Kallon mu take babu ko dauke ido cikin wani yanayi, ranta a matukar bace, da sauri ya isa gaban ta yana mika hannu zuwa wajen jakar kayan ta
"Welcome Ma. Ashe kina hanya."
Kallon banza tayi masa, ta wuce shi ta shigo dakin, har in da nake, bina ta cigaba da yi da kallo tana tabe baki kafin tace
"Yanzu akan wannan ka zabi ka katse rayuwar ka, ka hakura da komai ka anan, yaushe ka zama haka Farouk?"
Ta fada tana buɗe idon ta sosai akan sa
"Mummy Please, ki huta sai muyi magana."
"Naki na huta ɗin, kana son ka kashe rayuwar ka abanza kana cemin ma huta, saboda kai kafi kowa tausayi a duniya ko? Abin da kuma nazo na tarar fa, ko shima tausayin ne? Kuna kwance tare amma a waya kana nuna min kai kawai kana son taimaka mata ne."
"Ya Salam... Mummy bafa abinda kike tunani bane."
"Toh mene?" Ya fada a harzuke
Kallo na yayi ganin yadda nake ta binsu da ido kamar na samu tv yace
"Jeki dakin ki Aminatu, anjima sai na kaiki gidan ko?"
Zumburo baki nayi cikin jin haushi na tashi na bar dakin, sakin baki tayi tana dubanshi.
"Farouk!"
"Mummy dan Allah, here me out, idan kika ji komai sai ki yanke min hukuncin da kika ga ya dace dani."
"Farouk wanne abu kuma zanje bayan wanda ka fada min, Ja'afar ya fada min, akwai wani sauran point ne da ban ji ba?"
"Ja'afar...?" Ya ambata cike da mamaki
"Ban isa ya fada min ba ne ko me? Ina chan ni sam hankali na ya kasa kwanciya kai kana nan kana baccin ka da yar yarinya karama, toh wallahi an gama, munafukar kakar taku sai tazo ta warware wannan kullin da tayi, ko da bana gidan naku amma ido na na kan duk wani motsin ku, kuma wannan karon bazan yarda ba wallahi."
Dafe kansa yayi ya juya mata baya da sauri, matsalar mahaifiyar su kenan, ya rasa dalilin da yasa a komai take blaming Dadah, bayan babu wani abu da tayi mata, shi yasa yayi ta iya kokarin sa na ganin ya kwantar mata da hankali amma sai da Ja'afar ya kai mata gulmar, yana jin ta tana sababi kafin ta nemi waje daya ta ajiye kayan ta tana zaman gefen gadon.
Dakin ya bari ya nufi wajen Dadah dan sanar mata kar sai ta fito su hadu, tana zaune akan babbar darduma da alama ta gama sallar walaha kenan, tana dan bitar karatun Alkur'ani, gefen ta ya zauna har ta kai aya ta rufe ta juyo tana murmushi
"Babana an tashi kenan."
"Uhum." Yace yana tankwashe kafarsa
"Dama Mummy ce tazo."
Ya fadi maganar kamar wanda baya so, shiru Dadan tayi cikin nazari, tabbas tasan zuwan nata ba zai zame musu Alkhairi su dukka ba, sai dai abu daya ta take tsoro shine yadda zata dauki maganar Aminatu, tasan ta sarai mace ce wadda take da son kanta, ba lallai ta fuskanci maganar ba, shiyasa take ta kokarin ganin Daddy yasauko ya bar su sun tafi baki daya, idan yaso Farouk sai ya koma makarantar sa ita kuma a sata a ko tasu Amal ce, sai dai hujjar daya bata na cewa wa'adin daya deba wa Farouk din be cika ba yasa ta hakura, sai dai zuwan mahaifiyar shi a yanzu yasa ta ɗan ji tsoron abinda zai je ya dawo. Duk da haka ba zata shiga hurumin da bana ta ba, d'anta ne tafi kowa sanin ciwon sa.
"Ah sannun ta da zuwa, yaushe ta zo?"
"Yanzu." Ya amsa yana kallon yanayin ta
"Madallah, sannun ta da zuwa."
"Uhum." Kawai yace ya tashi
"Dan Allah Dadah... Kinsan halin Mummy, karki bari tayi abinda ba dai-dai ba dan Allah."
Kallon sa tayi ba tare da tace komai ba har ya juya ya bar dakin, tashi tayi ta koma saman gadon ta tana tunanin yadda abubuwan zasu zama.
***
Kwanciya na koma nayi ina jin haushin katse min zuwa gida da matar tayi, ido na a lumshe kamar ina bacci aka turo kofar dakin, da sauri na bude ina kallon kofar, yana tsaye ya rike hannun kofar yana kallon ciki, tashi nayi zaune ina saukowa da kafata kasa
"Ya Farouk wacece datazo?"
"Mamana ce." Ya amsa min yana sakin kofar, ciki ya shigo ya zauna gefen gadon yana matso dani kusa dashi ssosai.
"Kina son ta ko?" Ya tambaye ni yana kallon fuska ta, da sauri na girgiza masa kai alamun a'ah, ware idon sa yayi gaba daya akaina.
"Are you serious! Mamana ce fa."
"Eh ni bana son ta." Na faɗa cike da yarinta
Da sauri ya rufe baki yana harara ta
"Kar na sake ji kin fada, kice kina son ta."
"Ni toh ba masifa take maka ba, ni bana son ta, ni kai kadai nake so sai Amal,sai yan gidan mu."
Murmushi naga yayi, ya rike hannu na cikin nasa ya murza a hankali
"Ni kina so na ko?" Ya tambaye ni
"Eh mana, kana da kirki ai."
"Toh idan kina son na, kiso mummy ma kinji."
A cunkushe na amsa da toh
"That's my girl." Yace yana mik'ewa. A nutse ya juya ya bar dakin ina kallon sa har ya gama ficewa.
***Waya ce a rike a hannun ta sanda ya shiga, yanayin da take magana ya gane akan sa take wayar, kai tsaye wajen kayan sa ya nufa ya tattara abubuwan da zai bukata ya kai chan dakin su Ja'afar ya zuba sannan ya shiga Kitchen yasa masu aikin gidan suka bashi breakfast ya kai mata dan yasan bata karya ba. Ko da ya koma ta gama wayar tana dan dube dube a cikin iPad.
"Mummy gashi nasan baki yi breakfast ba, in Kika gama sai kije ku gaisa da Dadah pls tasan kinzo."
Tabe baki tayi ta ja tray din gaban ta ta bude, juyawa zaiyi ta dakatar dashi
"Ka daina gudu dole muyi magana kaji da abinda nazo, ba zama nazo yi ba ina da abubuwan yi da yawa."
"Watsa ruwa zanyi sai nazo muyi maganar, kiyi hakuri."
"Yayi, ina jiran ka."
"Ok."
Yace ya nufi dakin Aminatu, budewa yayi ya ganta tana kokarin zuge zib ɗin doguwar rigar dake jikin ta, karasawa yayi ya taymaka mata ta cire sannan yace tayi wanka ya kaita, da gudu tayi toilet shi kuma ya nufi dakin su Ja'afar da ya zama nasa a yanzu.
A gurguje ya shirya ya fito dan baya so taje neman sa dakin sa, baya so sam su hadu ita da Mummy su biyu ba tare da shi din a tsakani ba. Aikuwa a hanya sukayi kicibis ta tafi dakin nasa, riko hannun ta suka juya zuwa hanyar fita murnar ta take tsayawa.
Babu driver da alama Dada ta aike shi, sai driver mummy shi kuma baya so ya nuna masa gidan dan be san abinda mummyn zata iya aikatawa ba. Kawai sai ya yanke shawarar su tafi a kafa tun da babu nisa. Fita sukayi a kafa hannun sa sakale cikin nata, tana tayi masa hira duk yawanci akan wayar su da Amal ne, sama sama yake sauren ta, hankalin sa ya tafi akan yadda zai ɓullo wa Mummy. Sun kusa isa gidan suka yi kicibis da Garbati da Ilu, da mamaki suke duban su, sam Garbati be yi tunanin abin a iya nan zai tsaya ba, wani haushi ne ya taso masa, yayi saurin shan gabansu, da sauri ta koma bayan Farouk din tana buya.
"Me hakan?" Farouk ya fada bayan ya haɗa girar sama data kasa.
"Babu komai, kawai dai ajiya ta ta wajen ka nake dubawa, naga alama kuma dai babu wata matsala."
Haushi ne ya kama Farouk, sai dai ba zai biye masa ba, dan yaga alama sam Garbatin baya cikin jerin mutane masu ƙwaƙwalwa, hannun ta ya damke sosai suka raba ta gefen su suka wuce kawai ba tare da yace komai ba. Haushi sosai ya kama Garbati, yaji kamar ya jawo shi ya ta bugun sa ko zai huce, haka yayi ta zage zage Ilu na bashi baki suka wuce in da zasu.
A kofar gida ya tsaya ta shiga ciki ya tabbatar ta shiga sannan ya juya ya bar wajen.
***
A tsaye na tarar da Inno wajen in da take kiwon ta, tana gani na ta saka min ido cike da mamaki, da sauri nayi wajen ta ina murnar ganin ta, murmushi ta k'ak'alo wanda ya zauna iya saman fuskar ta, ta ajiye abinda take
"Ke kuma daga ina?" Ta tambaya tana yin gaba, bin bayan ya nayi lokacin su Karime suka ganni, ihu muka hau yi muka dane juna. Nan da nan aka fara shigowa daga cikin gidan namu zuwa gani na, hakan ya bata ran Inno ta kwala mana kira ni da Karime muka shiga dakin ta, waje ta nuna mana da hannun ta sannan ta fice ta bar mu a dakin bayan ta ja mana kunne akan karmu sake fitowa sai ta kiramu. Hakan da tayi ya rage masu shigowar dan sun sane abinda take nufi, hirar mu muka baje irin ta yarinta nida Karime ina ta bata labarin gidan Bature, murna take tana jin dama ita ce. Chan da azahar Inno ta kira Karime ta kawo mana dambu da wake, rabon dana ci irin abincin gidanmu an jima, ai kowa na saki ciki naci sosai harda k'ari, nasha ruwa nabi lafiyar katifar Inno na baje abina cikin jin dadi.
****
Tun da ya koma gidan yaki yarda sam su hadu da Mummy, rufe kansa yayi a daki ya cigaba da aikin da yake na neman admission din sa tun wajen sati biyu da ya wuce, be samu gama wa shi yasa yau ya dage ya gama. Baya so ya kara bata wani zangon karatun a banza kamar yadda yayi wannan karon, shiyasa ya yanke shawarar chanja akalar karatun nasa zuwa abinda yake da tabbacin zai taimaka masa matuka wajen hukunta mutane irin Garbati.
Knocking din dayaji a kofa yasa gaban sa ya fadi, kin magana yayi aka cigaba da knocking din, ya zata zata hakura ta tafi, ganin da gaske take yasa ya kashe komai ya mayar waje daya, ya nufi kofar cikin tafiya irin ta masu bacci. Budewa yayi tana tsaye ta harde hannun ta. Kallon da tayi masa ne yasa cikin sa murdawa, takardar hannun ta ta ware ta wurga masa.
"Tun da kaki yarda muyi magana, sai ka duba wannan, kuma dole cikin biyu kayi daya, idan kuma ba haka ba, abinda da biyo baya ba zai maka dadi ba, dan na lura sam baka da hankali baka san ciwon kanka ba."
"Mummy..." Juyawa tayi ta bar wajen bata ko sake kallon sa ba. Kasa ya tsugunna ya dau takardar hannun sa na rawa, layi cikin layi ya fara bin rubutun, gaban sa yayi wani mummunan faduwa, a take ya juya da mugun gudu ya nufi dakin da take, yana zuwa tana rufe kofar, bugawa ya hau yi yana kiran sunan ta da sauri
"Mummy dan Allah karki fara, dan Allah Mummy, nasan me nake da hankali na wallahi, zanyi ko menene kika ce amma dan Allah karki min haka."
Babu alamun zata saurare shi, zamewa yayi a wajen ya zauna kansa na juya masa.
Manage 🙏😥©️®️HafsatRano
*ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER*
07067124863
*Ko kuma*
09032345899
*ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sababbi,karku manta ku dannan SUBSCRIBE kuyi LIKE sannan kuyi SHARING*🙏🏽
https://youtu.be/Zyl7_eSgXuo
(9)
***Fitowar ta kenan zata dan taka kafarta ta hange shi a durkushe a kofar dakin sa, da dan saurin ta ta k'arasa
"Babana?"
Dagowa yayi idon sa sun kada sunyi ja ya kalle ta
"Tashi muje daki na."
Ta fada tana mika masa hannu, mik'ewa yayi cikin sanyi jiki yabi bayan ta, Mummy na jinsu ta tabe baki, babu wanda ya isa ya sata ta sauya ra'ayin ta akan abinda ta haifa, ba zata bari tana kallo a lalata masa rayuwa ba dan shi yafi kowa sauƙin kai.
Suna isa dakin ya zame ya zauna kasan carpet din dakin yana jin zuciyar sa na tafasa.
"Menene matsalar?" Ta saka masa ido, tana kallon yadda kirjin sa ke kaiwa da komowa. Shiru yayi ba tare da yayi magana ba ya mika mata takardar Mummy. Murmushi kawai tayi bayan ta gama karantawa ta mika masa, tasan zata aikata fiye da abinda tace ɗin, dan bata shakka ko kokonton hakan, sai dai babu yadda ta iya, musamman da babu wata alaƙa yanzu dake tsakaninsu da ita sai ta ya'ya, amma tana jan girman ta, bata so kuma wani abu ya shiga tsakanin shi da mahaifiyar sa.
"Kayi mata abin da take so kawai Babana, shine zaman lafiyar kowa."
"Dadah....?"
"Shine maslaha, abu ne me sauki, kuma tabbas kayi kokari ma ladan ka yana wajen wanda kayi domin sa."
Matsawa yayi jikin kafarta ya dora kansa a saman, zuciyar sa tayi rauni sosai, ba ya jin