Showing 60001 words to 63000 words out of 112633 words
Chapter 21 - DAURIN GORO COMPLET book 1 by Hafsat Rano.txt
aiki soji inda ya tafi makarantar horar wa dake garin na Kaduna, inda Marwan ya zabi tafiya jami'ar ta Ahmadu Bello dake garin na Zaria. Haka rayuwa ta cigaba da tafiya cikin nasara.
Kasancewar shi Marwan d'a daya tilo wajen iyayen sa yasa shi kara shakuwa sosai da aminin nasa, saboda babu wani wa ko k'ani da zasuyi shawara sosai. Masu arziki ne na gaske, abun kwatance a kaf fadin yankin su .
Kabir su uku ne wajen iyayen su duk maza, shi ne na farko sai kannen sa Adamu da Ahmadu. Mahaifiyar su da suke kira da Dadah mace ce mai kirki da sanin ya kamata. Tana da abokiyar zama guda daya sai dai Allah bai sa ta haihu a gidan ba har zuwa lokacin da maigidan ya rasu ta tattara ta kama gaban ta, duk da hakan har yanzu suna gaisawa da juna.
Bayan rasuwar mahaifin su komai ya dawo hannun Kabir, shine ya tsaya tsayin daka wajen ganin ya kula da abinda mahaifin su ya bar musu, ya kuma cigaba da kula da yan uwan sa.
Cikin hukuncin Allah komai ya dinga tafiya musu cikin nasara da daukaka.
***
A gaggauce ya shirya yana yi yana duba agogon dake daure a tsintsiyar hannun sa, karo na shida kenan da yake faman kiran sa akan an fara baya wajen, cikin sa'a ya gama shirya wa ya dauki hanyar jami'ar.
Yana isa yayi saurin dukawa kansa a k'asa yace
"Tuba nake ranka ya dade."
Harara ya sakar masa, ya bigi saman kafadar sa cikin jin haushi yace
"Allah ka iya jirga mutane, da ban azalzala ka ba da shikenan sai ayi babu kai."
"I'm deeply sorry oga."
Ya sara masa yana kokarin cire hular kansa, da wani irin shock ya tsaya yana kallon su, yan mata ne su biyu cikin shiga iri d'aya sai dai d'aya ta girmi daya duba da yanayin shekarun su
"Kb!"
Ya kira shi da d'an ƙarfi ganin yadda ya bada attention d'insa gaba daya wajen su.
"Man nayi farin zuwa, wallahi naganta, no wonder naji sai na tsaya na tsara kwalliya ta ashe yau zan hadu da future d'ina."
Dariya Marwan yasa ya kama hannun sa.
"In dai Abidah ce kamar yadda naji ana fada ba sauraran ka zatayi ba, amma wacce kake so cikin su? Karamar ko babbar?"
"Babbar, itace Abidah?"
"Wai, toh ka gwada sa'ar ka, nidai babu ruwana idan ta wulakanta ka."
Gyara wa ya shiga yi sosai
"Aiko zan gwada, nasan nafi karfin wulakanci wallahi."
"Owk best of luck, bari na matsa ciki kafin a fara, kuma wallahi ka zama kusa dan zan neme ka."
"An gama my guy."
A chan nesa ya hange su, suna tsaye gefe suna kallon yadda ake gabatar da taron convacation ɗin, magana suke kasa kasa da juna, kai tsaye ya isa wajen cikin gwarewa ya shiga introducing kansa, duk suka zuba masa ido suna kallon sa, dan murmushi tayi kawai bata ce komai ba, karamar ce ta amsa masa suka shiga hira kamar sun saba, da haka ya hilace su har ta saki jiki dashi, cikin dan kankanin lokaci suka saba, ta ware sosai tana amsa masa,tun daga lokacin shikenan suka saba, soyayya ta shiga tsakanin su.
***
Bayan Aure!
Part uku ne sai na Dadah dake gefe, baya zama saboda yanayin aikin sa, hakan yasa ka shakuwa mai karfi shakanin ta da Adam da Aliyu, bata da matsalar komai duk sanda yazo yakan yi two weeks sai kuma wani dogon lokacin. Kasancewar Dadah mace wadda tasan ya kamata yasa suke zaune lafiya kowa yana mutunta kowa.
A lokacin ne Marwan yayi aure ya auri wata yar zaria, basu wani dade ba auren ya mutu tun da ya ji tana waya akan yadda take so dukiyar sa ta dawo hannun ta, ya tattara ya watsar da duk wata maganar aure ya cigaba da zaman sa haka nan.
Rayuwar ahalin Dadah rayuwa ce mai dadi da kaunar juna.
Shekaru biyar da auren Kabir da Abidah Allah ya azurta su da samun d'a namiji, wanda take Dadah ta zaba masa sunan mahaifin ta Umar Farouk, dukkan soyayyar da d'a yake nema wajen mahaifin sa Uncle Aliyu kamar yadda Abidah take ce masa ya karbe ta, shine yake masa komai na uba saboda rashin zaman mahaifin sa.
A lokacin Marwan ya sake auren har mata biyu suma duk abu daya ne ke kawo su data farkon, gashi duk cikin su babu wadda ta haihu sai dai suzo su tafi.
Kanwar Abidah mai suna Safiyya ta gama karatun ta, ashe dama soyayya suke da Aliyun babu wanda ya sani, hakan ya kara faranta ma Dadah dan ta gamsu da Abidah saboda haka zata so su kara hada zuri'a.
Rikon Farouk ya koma kachokam wajen Aliyu da Safiyya bayan auren, su ka cigaba da zaman lafiyar su cikin kauna da kwanciyar hankali.
***
Cikin kankanin lokaci dukiyar Marwan Muhammad Dikko ta bunkasa. Samun aikin sa a PTDF ya sa dole suka tattara suka koma garin na Abuja, kasuwanci ya cigaba yana juya dukiyar su, daga shi sai mahaifiyar sa har lokacin baya maganar aure, babu yadda aminin sa bai masa ba amma sam yaki maganar auren da uzurin har lokacin bai samu wadda tayi masa ba.
Gini ya fara a hade da juna guda biyu, komai iri daya sai dan banbancin girma, abun da akwai kudi ba'a wani dau lokaci ba ya kammala. Yanayin aikin Kabir yasa har aka gama ginin be san komai akai ba, mukullin gida kawai ya damka masa a matsayin kyauta ya zauna har karshen rayuwar sa. Ba karamin murna yayi ba, saboda bai taba zato ko tsammani ba, nan suka hau shirin tariya suka tattara komai suka koma garin na Abuja har Dadah, duk da Safiyya da Aliyu basu ji dadin tafiyar tasu ba, amma sun san hakan wani cigaba ne, dole suka bisu da fatan alkhairi suka rabu cike da kewar Farouk da ya zama tamkar d'an su.
****
Shekaru sun ja, abubuwa da yawa sun faru, ciki har da haihuwa da Allah ya azurta Aliyu da Safiyya ta d'a namiji, suka sa masa suna Ja'afar, lokacin Farouk na da shekara biyar a duniya. Har lokacin Alhaji Marwan Dikko bai yi aure ba, kuma bashi da niyyar yi, takanas Hajiya Turai ta aika aka kira mata Kabir (Daddy) ta sasu a gaba da fadan lallai ya matsa masa ya fitar da mata, dan zaman shi haka ya ishe ta babu da balle jika, hakuri suka hada baki suka bata, suna fitowa Kabir ya sake dora masa da nasa fadan, haka dai yayi masa alƙawarin zai yi kwanan nan babu jimawa.
***
*Bakaken Ranaku*
Yanayin aikin soja da rashin lokacin su ya kara saka shakuwa mai karfi tsakanin Adam da Abidah, a bangaren ta yake zama har dare ayi kallo ayi hira da wasa da dariya, wani lokacin ma har sai ta tafi ta kwanta ta barshi idan ya gama ya rufe mata kofa.
Watarana da daddare bayan ta tafi daki ta kwanta sai taji tana buƙatar dauko ruwa, kanta tsaye ta nufo falon, tun daga nesa take jin alamun magana a cikin fushi, d'an dakatawa tayi tana sauraron shi,
"Kinsan Allah, kije chan ki nemi uban da yayi miki ciki, dan kin rainan wayo shine zaki kwaso cikin ki kizo ki na na min."
"Eh nasan wannan amma sau daya shikenan sai kice ni, tab ai wallahi uban da yayi miki kije can ki neme shi, dan tsabar iskanci sai da kike gab da haihuwa sannan zaki kirani kina min wani banzan zance, karki kara kirana wallahi kinsan ni kinsan me zan iya."
Tsaki yaja da karfi ya kashe wayar yana bugata saman kujera, rai a bace Abidah ta ƙaraso falon
"Anty!" Ya fada cikin alamun tsoro tsoron ko taji, bata amsa ba sai ma zama da tayi kujerar dake kallon sa tana tallafe cikin ta dake wata takwas.
"Adam, me naji kana cewa?"
Ta watso masa tambayar tana kallon yanayin sa. Zai yi magana tayi saurin daga masa hannu
"Ciki kayi ma wata Adam?"
Juyar da kansa yayi gefe a ciki ciki yace
"Tun da kin riga kinji, bani da damar boye miki, mistake ne ba wai hali na bane."
A cikin tsananin mamaki take kallon sa, bata taɓa tunanin Adam da aikata abu makamancin hakan ba, fada ta hau yi masa ta inda take shiga bata nan take fita ba, tayi masa tas kuma tace tabbbas dole yan uwan sa da mahaifiyar sa su sani, da sauri ya zamo kasa ya haɗa hannun sa ya hau yi mata magiya, bata saurare shi ba tayi wucewar ta daki ta rufe da key.
Tsawon kwanaki uku yana mata ziryar ta rufa masa asiri, kin bashi fuska tayi, ta daina sakar masa fuska ko kadan, tunanin yadda zata sanar wa Dadah take, bata son abinda zai daga wa matar hankali, haka tayi ta fama da abin a ranta ta rasa wanda zata faɗa wa.
Kwatsam sai ga Safiyya da Aliyu sun zo, hakan ba karamin dad'i yayi mata ba, bayan sun huta ne ta samu damar sanar musu abinda yake faruwa, sosai Aliyu ya dau zafi ya kirashi ya ci masa mutunci sannan ya ce dole ne Dadah ta sani sannan dole Kabir ma ya sani, shawarar yadda zasu fara fad'a wa ita Dadah sukayi musamman suka je har dakin ta, tare da Adam ɗin yana sunkuyar da kansa kamar munafiki, tun da taga yadda suke nuku-nuku ta gane akwai matsala, kafin su samu damar fada mata ta jefe su da tambayar,ala dole Aliyu ya daure ya sanar da ita, iya kar rudewa ta rude, bata san sanda ta rufe shi da duka ba, tana yi tana kukan ya cuce ta, da kyar suka lallaba ta, ta yi shiru suka shiga tunanin yadda za'a bullo wa al'amarin tun da dai ya tabbatar musu ba halin yarinyar bane shine ya yaudara ta da dadin bakin zai aure ta ita kuma ta amince masa.
Tunanin zuwan Daddy kowa ya shiga yi dan yasan ba karamin artabu za'a sha dashi ba, ranar da ya kira kuwa yace yana hanya duk jikin su a sanyaye, haka ya zo ya tarar dasu sukuku kamar wanda akayi ma mutuwa.
Wanka yayi ya fara hutawa kafin ya nufi bangaren Dadah, bayan sun gaisa ne suna d'an taba hira Alhaji Marwan ya shigo, yana zama aka shiga yin sallama a ɓangaren, Dadah ce ta yunkura ta leko, mata ne guda biyu cikin yanayin tashin hankali da rashin nutsuwa, hannun su tabi da kallo a take tasha jinin jikin ta jiri-jiri ne ya soma daukar ta, tayi saurin dafe bangon tana yi musu iso ciki, a d'arare suka bita, falon suka koma suka samu waje suka zauna. Hakan yasa suka katse hirar da suke suna kokarin mik'ewa Dadah ta dakatar dasu
"Ku tsaya ayi komai a gaban ku, dan kuma ta shafe ku."
Komawa sukayi suka zauna da tunanin abinda yasa tace hakan,
"Sannun ku da zuwa."
Tace tana mika hannu dan karbar jaririyar hannun su.
"Gata nan, tabbas bamuyi tunanin ganin ku haka nan ba, ranmu a bace muka tawo sai dai a yadda kika yi mana yasa muka ji nauyi da kunya, gata nan, yar ku ce dan dukkan bincike ya nuna yaron gidan nan ne yayi mata cikin, sai dai ita Allah yayi mata rasuwa wajen haihuwar shiyasa ma muka jinkirta kawo ta har zuwa sanda akayi sadakar bakwai."
"Allahu Akbar, Allah ya jikan ta, Allah ya raya mana, kuyi hakuri dan Allah, d'a ne ka haife shi, amma baka haifi halin shi ba, kuyi hakuri kuyi hakuri."
"Me ya faru Dadah.?"
"Kira min Adamu a waya, yazo nan bangaren sai kuji komai."
Daga waya yayi ya kirashi, ya ajiye yana jin zuciyar sa kamar zata faso kirjin sa. Kan sa tsaye ya shigo falon, da kallo duk suka raka shi har ya samu waje ya zauna yana kallon matan. Tashi Dadah tayi ta mika masa jaririyar tana buɗe rufin da akayi mata da abin daukar yara
"Ko da ace zaka ƙaryata, ka dube ta, babu abu daya data bari naka sanda kana karami, babu abu ɗaya, kaga ikon Allah ko? Toh haka rayuwa take, duk wanda yayi da kyau zai gani."
Sai ta juya wajen su Daddy
"Gashi nan ya ce aka kawo muku, sai yayi muku bayanin yadda akayi aka haihu a ragaya, sai dai wannan tsantsar kamar ta isa ta tabbatar da komai."
"Ku kuma dan Allah kuyi hakuri akan abinda ya faru, bani da bakin da zan iya baku hakurin rashin kyautawar da akayi wa yarku, sanadiyar da har ta rasa ranta, Allah ya baku hakurin rashin ta."
Mik'ewa sukayi a tare, sukayi sallama suka tafi. Suna fita Dadah ta karbi jaririyar tayi dakin ta tana jin kamar ta yi kuka, yau itace zata goya yar da ba ta hanyar sunna aka same ta ba, sai dai dole laifin iyayen ba zai shafe ta ba, zatayi kokarin ganin hakan bai shafi rayuwar ta nan gaba ba.
***Wata irin shaka Daddy ya kai masa, ya shiga bugun sa da dukkan karfin sa, da kyar Alhaji Marwan ya kwace shi dan tuni ya sauya masa halitta, da rarrafe ya fita daga falon saboda tsabar yadda ya daku.
Saman kujera ya fada yana dafe kansa, idan akwai abinda ya tsana take kyama a rayuwar sa ya kasance zina, abu ne da duk wanda zai iya aikatata to tabbas bashi da sauran mutunci a idon sa.
Idan ya tuno yar jaririyar sai yaji kansa ya sake sarawa, komai daren dadewa dole ne gaskia ta fito. Ya zatayi da abinda bata da masaniyar komai akai? Shigowar matar dake dan taimakawa Abidah da aiki a guje ya maida hankalin su gareta
"Alhaji ina tunanin haihuwar tazo."
A kid'ime suka bi bayan ta, aka nufi asibiti da ita, lokacin ta riga ta gama galabaita sosai, har bata gane wanda ke kanta sosai. Sai data dau tsawon lokaci dan har an soma shirye-shirye shiga da ita theatre ta haihu sai dai abinda ta haifa bai zo da rai ba. Kwanan ta biyu a asibitin aka sallame ta.
***
Bangaren Abidah Dadah ta nufa dauke da jaririyar a hannun ta, Abidah na zaune tana shan tea a kofi duk jikin ta babu dadi aka shigo, ajiye kofin tayi tana kokarin mik'ewa ta dakatar da ita
"Zauna dan Allah. Ke da ba lafiya ba."
"Ai da sauki Dadah, ashe sun zo ranar." Tace tana mai kallon hannun nata
"Hmmm sun kawo ta gata nan, gashi sam taki karbar madara wallahi, kwana biyun nan kuka kawai take sai dai idan taji uwar bari ta karba tasha kadan, na rasa yadda zan."
"Allah sarki."
Tace tana kallon yarinyar, da sauri Farouk ya taso yana leka fuskar ta, daidai lokacin ta saka kuka sosai, da sauri ya kalli Abidah
"Mummy kuka take, sabuwar bbyn da kika haifa mana ce?"
Daga masa kai tayi, ta mika hannu ta karɓe ta daga hannun Dadah ta soma jijjigen ta.
"Bari na dauko madarar a sake gwada mata, kukan ya soma yawa wallahi."
"Mummy ya sunan ta? Itama kanwata ce kamar Ja'afar?"
"Kanwar ka ce Farouk."
"Yess!" Yace yana murna, yana kama dan karamin hannun ta, Dadah ce ta dawo dauke da madarar ta bata ta koma wajen bakin da tayi, karbar ta tayi suka shiga daki, ta sake hada mata madarar ta bata, kadan tasha ta yi bacci, shiru tayi tana tunanin taimakon yar jaririyar da bata san abinda duniyar ke ciki ba. Ba tare da shawara da kowa ba ta yanke abinda take ganin zai taimaka mata ya kuma farantawa Dadah.
***: *DG*
27
Adam duk ya fita hayyacin sa, babu wanda ke bashi fuska a gidan, zaman daki ne ya zama abin yin sa tunda idan ma ya fito babu wanda ke kulashi, gefe daya yarinyar da yake mutuwar so da kauna, kwana wajen nawa kenan yana sintirin kiran ta a waya amma bata daga wa, daga karshe ma sai tayi blocking kiran sa baki daya, abin yayi masa zafi ssoai, dole ya shirya ya tafi gidan su, tun da ya hango motar yaji jikin sa ya soma rawa, ganin an bude gate din gidan yasa shi labewa a baya, itace tayi kyau ainun, cikin shigar ta kamar ko yaushe, ta nufi motar. Motar Alhaji Marwan ce, ji yayi numfashin sa ya soma ja da kyar, be kara shiga tashin hankali ba sai daya ga ya zuro kafafun sa ya fito, shi din ne kowa, fuskarsa dauke da madaukakin farin ciki, yadda tayi masa jagora zuwa cikin gidan yasa gama tabbatar da komai ya kare masa. Wayar sa ya sake kira yana son sake tabbatar wa, sai dai kamar ko yaushe ne, ba zai taba iya kiran nata.
Da kyar ya kai kansa gida, zuciyar sa na zafi, zafi irin na rabuwa da masoyin daka kwallafa rai akan sa, ka dora dukkan buri akan sa, shin me hakan ke nufi? Ta san abinda ya faru dashi ne yasa ta juya masa baya? Ko kuwa dai Alhaji Marwn...
Tuni zuciyar sa ta hau tururi, yaji kamar ana zare masa sauran tausayin da ya rage masa a zuciyar sa, sai da ya zama babu digo ko sauran tausayin kowa a ransa, a take ya yanke wa kansa shawarar abinda yake ganin shine daidai.
***
Zagayen dakin yake yana dan shafa saman kansa, tunanin sa ya tsaya tsak daga lokacin da ya tuna tabbas Abidah ta shayar da Amal nono, eh duk da ba wai ta shayar da ita bane har zuwa sanda ta isa yaye, amma tabbbas ta zama mahaifiyar ta ta shayarwa kamar yadda musulunci yace,ya akayi dukka suka manta da wannan? Duk da a lokacin ya hane ta ya gargade ta akan kadda ta shayar da ita bayan ya gano take taken ta, sai dai a yanzu yana hasaso hakan a matsayin wani ɓangare da yake bukatar dubawa. Da sauri ya jawo wayar sa, number ta da har lokacin ke ajiye a wayar sa, har ya danna kiran sai kuma yayi saurin katsewa, akwai sauran abubuwan da yake son ganowa, dan haka dole ya gama bitar komai daki-daki kafin ya kira ta.
***Babu bata lokaci aka shiga hidimar bikin Alhaji Marwan Dikko, zuwa lokacin Adam ya zama kamar wani tsohon mahaukaci, komai ya tsaya masa, babu kuma wanda ke bin takansa, kowa sabgar gaban sa yake akan abinda yake ganin wani kuskure ne da ya aikata da